Labarai




Mene neMisalin siffofin aiyuka daga Alkur’ani?


Misalin faxin Allah Maxaukakin Sarki:


sannan ya daidaita zuwa sama


Sannan fadinsa


shin suna jira face dai Allah ya je musu


Allah Madaukakin Sarki yana cewa:


kuma ba su kaddara Allah a bisa hakikanin ikon yinsa ba, kasa kuma duka damkarsa ce, ranar kiyama kuma sammai abubuwan nadewa ne ga damansa.


Allah Madaukakin Sarki yana cewa:


me ya haneka ka yi sujjada ga abin da na halicce shi da hannaye na?


Allah Madaukakin Sarki yana cewa:


kuma muka rubuta masa a cikin alluna daga kowa ne abu


Allah Madaukakin Sarki yana cewa:


yayin da Ubangijinsa ya kuranye zuwa ga dutsen, ya sanya shi nikakke


Allah Madaukakin Sarki yana cewa:


lalle Allah yana aikata abin da ya so


Da wasun su daga Ayoyi.


? Misalin siffofin Ayyuka daga Alkur’ani


Menene misalin siffofin Ayyukai daga sunna?


Fadar Manzon Allah tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi misali ce


Ubangijinmu yana sauka a kowane dare izuwa saman duniya lokacin da daya bisa ukun karshe ya yi


Kuma faxin Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi a cikin Hadisin Ceto


sai Allah ya zo musu cikin surarsa wacce suka sani sai ya ce nine Ubangijinku sai su ce kai ne Ubangijinmu


kuma muna nufi da siffar aiki a nan zuwa ba sura ba kawai ka fahimta. Da fadinsa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi


Lallai Allah yana danke Kasa a Ranar Alkiyama kuma Sama ta kasance a Hannun Damansa, sannan ya ce: Ni ne Sarki


Kuma Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:


yayin da Allah ya halicci halitta sai ya rubuta da hannunsa a bisa kansa cewa rahmata ta rinjayi fushi na


A cikin Hadisin jayayyar Annabi Adam da Musa: "Sai Adam ya ya kai Musa Allah ya zabeka da Zancensa kuma ya rubuta maka Attaura da Hannunsa to zancensa Madaukaki da kuma Hannunsa siffifi ne na Zati kuma Maganarsa Sifa ce ta Zati kuma da aiki hade kuma Rubuta Attaurarsa Sifa ce ta aiki Fadin Annabi Amincin Allah a gare shi:


Lalle ne Allah Madaukaki yana shimfida hannunsa da dare domin masu lefi da rana su tuba kuma yana shimfida hannunsa da rana domin masu lefi da dare su tuba


da wadansunsu da yawa.


Sunayen Allah dukkansu tsayayyu ne


Shin ana cirar wani suna daga dukkan siffofin aiki ko kuma sunayen Allah dukkansu tsayayyu ne?


A’a bari dai sunayen Allah Madaukaki dukkansu tsayayyu ne ba’a ambatonsa sai da abin da ya ambaci kansa da shi a cikin littafinsa ko kuma Manzan Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya sakar masa shi kuma dukkan wani aiki wanda Allah Madaukaki ya sakar ma kansa da shi to shi acikinsa yabo ne da kuma cika amma kuma ba dukkan su ne Allah ya siffanta kansa da shi ba kai tsaye kuma ba dukkanninsu ne ake cirar wani suna daga gare su ba, kadai dai akwai daga cikin su wadanda yake siffanta kansa da shi kai tsaye.kamar fadinsa Madaukaki:


Allah ne wanda ya halicceku sannan kuma ya azurta ku sannan kuma ya matar da ku sannan kuma ya raya ku


kuma ya ambaci kansa da Mahalicci Mai arzurtawa Mai rayawa Mai matarwa Mai tsarawa, kuma daga cikinsu akwai wasu aiyukan wadan da Allah madaukaki ya sakar ma kansa ta hanyar sakamako, da kabaltawa kuma ita a cikin abin da aka koro dan shi yabo ne da kamala, kamar fadinsa Madaukakin sarki:


suna yaudarewa da Allah, alhali kuwa shi ne mai yaudararsu


Kuma sun yi makirci, Allah kuma ya yi musu makircin,kuma Allah ne mafi alherin masu saka wa makirci


sun mance Allah sai ya manta da su


sai dai kuma bai halatta a saketa a bisa Allah ba cikin wanin abin da aka koro a ayoyin, ba za’a ce Allah Madaukaki yana makirci ba ko yana yaudara ko yana isgili ba da makamantan wadannan,,kuma hakanan ba za’a ce Makiri Mayaudari Mai isgili ba kuma Musulmi da mai hankali ba zasu fadi haka ba,to hakika Allah Mai girma da daukaka bai siffanta kansa da Makiri ba ko Mayaudari face ta fuskar sakayya ga wanda ya aikata hakan ba tare da gaskiya ba, kuma bayan tabbas ya sani cewa sakayya a bisa haka da adalci aiki ne mai kyau daga ababan halitta to kaka ga Mahalicci Masani Adali Mai hikima.


me sunansa Al-Aliyyul A’alaa ya kunsa


me sunansa Al-Aliyyul A’alaa ya kunsa da abin da yake a ma’anarsa kamar Al-Zahiru da Al-Kahiru da Al- Muta’aali?


sunansa Al-Aliyyul A’alaa yana kunshe da siffarsa abin cirowa daga gare ta shi ne tabbatar da daukaka a gare shi Mai girma da daukaka da dukkan ma’anoninsa, daukakar bisansa Madaukaki a bisa Al’arshinsa,ya daukaka bisa dukkan halittarsa Manisanci daga gare su Mai lura da su yana sanin abin da suke ciki hakika saninsa ya kewaye dukkan komai, babu wani abu daga gare su boyayye da zai buya a gare shi


da kuma daukakar rinjayensa babu wani mai rinjayarsa babu kuma wani mai jayayya ko mai kishiyanta ko mai hanawa a gare shi, bari dai dukkan komai mai kaskantar da kai ne ga girmansa, kuma wulakantacce ne ga buwayarsa, kuma kowa yana katkashin tasarrufinsa da rinjayensa ba’a kufcewa daga kamunsa.


kuma daukakar sha’aninsa, dukkan siffofi na kamala sun tabbata a gare shi kuma dukkan wata tawaya korarriya ce ga buransa ya girmama kuma ya daukaka kuma ya tsarkaka, kuma dukkan wadannan ma’anoni na daukaka mai lazimtuwa ce babu wata ma’ana daga gare ta da za ta rabu da wata.


dalilin daukakar bisa daga Alkur’ani


menene dalilin daukakar bisa daga Alkur’ani?


dalilan a sarari suke a kansa ba za su kirgu ba kuma ba za su kididdugu ba yana daga cikin su wannan sunayen da wadanda suke da ma’anarsu, kuma yana daga ciki fadinsa Madaukakin sarki:


Mai rahama ya daidaita a kan Al’arshi


cikin gurare bakwai daga Alkur’ani kuma yana daga cikinsu fadinsa Madaukakin sarki:


shin ko kun amince cewa wanda ke cikin sama


Misalin faxin Allah Maxaukakin Sarki:


suna tsoran Ubangijinsu daga bisansu


Misalin faxin Allah Maxaukakin Sarki:


Zuwa gare shi Magana mai dadi ke hawa, kuma aiki na kwarai yana daukarta


Allah Madaukakin Sarki yana cewa:


Mala’iku da Ruhi suna takawa zuwa gare shi


Sannan faxinsa


yana tsara lamari daga sama izuwa kasa


Allah Madaukakin Sarki yana cewa:


ya Isa lalle ni mai karbar ranka ne, kuma mai daukeka ne zuwa gare ni


Da wasun haka masu yawa:


dalilin daukakar bisa daga sunna


menene dalilin wancananka daga sunna?


dalilansa daga sunna suna da yawa ba za su kididdugu ba, yana daga ciki fadinsa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi cikin hadisin Al-au’aal


kuma Al’arshi yana bisan wancananka kuma Allah yana bisan Al’arshi kuma shi ya san abin da kuke a kansa


Da fadinsa ga Sa’adu cikin kissar bani kuraiza, "Hakika kayi musu Hukunci da Hukuncin Sarkin da yake Saman Bakwai“ da fadinsa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shiga kuyanga: ina Allah? Sai ta ce: cikin sama Sai ya ce: ka ‘yanta ta don cewa ita Mumina ce


da hadisan Mi’irajin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi cikin hadisin zuwan Mala’iku


sannan wadanda suka kwana a cikinku sai su hau, sai ya tambaye su alhali shi ne mafi sani da su


Kuma Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:


wanda ya yi sadaka da kwatankwacin dabiniya na daga tsuwurwuri tsarkakakke domin Allah babu abin da yake hawa zuwa gare shi sai tsarkakakke


Kuma faxin Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi a cikin Hadisin Wahayi


idan Allah ya nufi zartar da lamari a cikin sama sai Mala’iku su yi bugu da fikafikansu suna masu kaskan da kai saboda fadinsa kai ka ce shi sarka ce a bisa fan dutse


kuma hakika dukkan ababan halitta sun tabbatar da wannan sai dai yan jahamiyya


Mas’alar istiwa’i


me shugabannin Addini daga magabata na kwarai suka fada a cikin mas’alar istiwa’i?


fadinsu baki dayansu Allah Madaukaki ya jikansu: istiwa’i ba abin jahilta ba ne kuma kaifiyyarsa ba abin hankalta ba ne kuma imani da shi wajibi ne kuma tambaya game da shi bidi’a ne kuma daga Allah sako yake, kuma a bisa Manzo isarwa take mu kuma a kanmu gasgatawa da mika wuya yake, haka kuma da fadinsu cikin dukkan ayoyi


mun yi imani da shi dukansa daga wajan Ubangijinmu yake


mun yi imani da Allah kuma ka shaida da cewa mu masu mika wuya ne


Dalilin daukakar Rinjaye daga Alkur’ani


menene dalilin daukakar tilastawa daga Alkur’ani?


Akwai dalilai ma su yawa daga ciki akwai faxin Allah Maxaukakin Sarki:


kuma shi ne tankwasa a kan bayinsa


kuma shi ne wanda ya kunshi daukakar tilastawa da kuma bisantaka.


Allah Madaukakin Sarki yana cewa:


Mai tsarki shi ne Allah shi kadai kuma Mai Rinjaye akan kowa


Allah Madaukakin Sarki yana cewa:


Mulki ga wa yake a yau? yana ga Allah Makadaici, Mai Rinjaye


Allah Madaukakin Sarki yana cewa:


Yace Ni ba kowa bane sai mai gargaxi haqiqa babu wani Allah face Allah Madaukakin Sarki


Allah Madaukakin Sarki yana cewa:


Babu wata dabba face shi ne mai riko ga makwarkwadarta


Allah Maxaukakin Sarki yana cewa:


ya jama’ar aljanu da mutane idan kuna iya zarcewa daga sasannin sammai da kasa, to ku zarce. Ba za ku iya zarcewa ba face da wani dalili


Da wasun waxannan daga ayoyi.


Dalilin daukakar bisa daga sunna


menene dalilin wancananka daga sunna?


dalilansa daga sunna suna da yawa yana daga ciki fadinsa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi:


ina neman tsarinka daga sharrin dukkan dabbar da kake rike da makwarkwadarta


Kuma Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:


ya Allah lalle ni bawanka ne kuma dan bawanka kuma dan baiwarka makwarkwadata tana hannunka Hukuncinka zartacce ne a kaina,kuma kaddararka gare ni mai Adalci ce


Kuma Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:


lalle kai ne kake hukunci babu wanda yake Hukunci a kanka, tabbas wanda ka jibince shi ba zai wulakanta ba wanda kuma ka ki shi ba zai daukaka ba


Da wasun haka masu yawa:


dalilin daukakar sha’ani


menene dalilin daukakar sha’ani kuma me ya wajaba a kore shi ga barin Allah Mai girma da daukaka?


Ka sani cewa daukakar sha’ani shi ne abin da sunansa AlkuddusAssalaam Alkabiir Almuta’aal ya kunsa da kuma abin da yake cikin ma’anarta da kuma dukkan siffofin cikarsa ya lazimta shi da siffofin daukakarsa ya daukaka a ce a cikin kadaitakarsa ya kasance waninsa yana da wani mulki ko wani yanki daga gare shi ko wani mataimaki ya kasance a gare shi ko wani mai ceto a gurinsa ba tare da izininsa ba ko yayi zalunci a gare shi


kuma ya daukaka cikin girmansa da mallakewarsa da rinjayensa a ce wani mai jayayya ko wani mai rinjaye ko wani masoyi saboda wulakanci ko kuma wani mataimaki ya kasance a gare shi


kuma ya daukaka cikin wadatuwarsa ga mata ko kuma da ko kuma uba ko tanka ko kuma mataimaki


kuma ya daukaka cikin cikarsa da rayuwarsa da tsayuwarsa da ikonsa ga mutuwa da gengedi da gajiya da wahala


Kuma ya daukaka cikin cikar iliminsa ga gafala da mantuwa da kuma fakuwar daidai da kwayar zarra ga iliminsa a cikin kasa ko a cikin sama


kuma ya daukaka cikin cikar hikimarsa da godiyarsa gay a halicci wani abu da wasa da kuma ya bar halitta sasakai ba tare da umarni da kuma hani da tashi da sakamako ba


kuma ya daukaka cikin cikar adalcinsa ga ya zalinci wani daya ko da kwatankwacin kwayar zarra ne ko ya cinye wani abu daga kyawawansa


kuma ya daukaka cikin cikar wadatarsa ga ciyarwar ko arzurtarwar ko bukata cikin wani abu izuwa ga waninsa ba


kuma ya daukaka cikin dukkan abin da ya siffanta kansa da shi kuma Manzansa ya siffanta shi da shi ga wofuntarwa da kamantawa kuma tsarki ya tabbatar masa da godiyarsa kuma ya buwaya ya daukaka


kuma ya daukaka ya tsarkaka ga dukkan abin da zai kore Allantakarsa da rububiyyarsa da kuma sunayensa kyawawa da siffofinsa madaukaka


kuma yana da misali wanda yafi daukaka a cikin sammai da kasa, kuma shi ne Mabuwayi Mai jin kai


nassoshin wahayi daga Alkur’ani da sunna cikin wannan babin sanannu ne kuma fahimtattu tare da yawanta da shahararta


Kuma faxin Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi game da Sunayen Allah


mafiya kyau wanda ya kiyayesu zai shiga Aljanna


menene ma’anar fadinsa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi cikin sunayensa mafiya kyau wanda ya kiyaye su zai shiga Aljanna?


hakika an fassara wannan da wasu ma’anoni yana daga cikinsu kiyaye ta da kuma rokon Allah da ita da godiya a gare shi da dukkansu. Kuma yana daga cikinsu cewa abin da ya halatta a yi koyi da shi kamar Mai jin kai da kuma Mai karamci to sai bawa ya bibiyi kansa a bisa ya inganta insafi da ita a kansa cikin abin da ya rataya da shiKuma wanda a cikinsa akwai ma’anar alkawarin narko kamar Mabuwayi Ma’abocin fansa Mai tsananin ukuba Mai gaggawar hisabi, to sai ya tsaya daga gare shi wajan tsoro da firgicikuma wanda a cikinsa akwai ma’anar alkawarin narko kamar Mabuwayi Ma’abocin fansa Mai tsananin ukuba Mai gaggawar hisabi, to sai ya tsaya daga gare shi wajan tsoro da firgici


kuma yana daga cikinta shaidar bawa a kanta da kuma bata hakkinta a ma’arifa da kuma ubudiyya misalinsa wanda ya shaida daukakar Allah Madaukakin sarki a bisa halittarsa da kuma bisansa a kan su da kuma daidaitonsa a kan al’arshinsa manisanci daga halittarsa tare kuma da kewayewarsa da su da ilimi da iko da wadansu wadannan kuma ya bauta masa da abin da wannan siffa ta hukuntar ta yadda zai zama da zuciyarsa mabukaciya yana hawa izuwa gare shi yana mai munajati da shi yana mai kwankwasawa kuma yana mai tsayuwa nan gaba gare shi tsayuwar bawa kaskantacce nan gaba ga Sarki Mabuwayi kuma ya dinga jin cewa zancansa da aikinsa mai hawa ne izuwa gare shi mai bijirowa ne a gare shi sai ya dinga jin kunyar cewa kada wani daga zancansa ko aikinsa da zai kunyata shi ya dinga hawa izuwa gare shi a can, kuma ya shaida saukar lamarin Ubangiji izuwa sassan duniyoyi a kowane lokaci da nau’o’in tsari da tasarrufi na daga kashewa da rayawa da daukakawa da kaskantarwa da bayarwa da hanawa da yayewar bala’u da kuma aikensa da kuma jujjuyawar kwanaki tsakanin mutane izuwa wadansun wadannan na daga tasarrufu a cikin daular da take ba mai tasarrufi a cikin ta in ba shi ba sai shugabancinsa ya zamo zartacce a cikinta kamar yadda yake so


Yanã shirya al'amari daga sama zuwa ga ƙasã, sa'an nan ya tãka zuwa gare Shi a cikin yini, wanda gwargwadonsa shekaru dubu ne ga abin da kuke lissafãwa.


to wanda ya cikawa wannan mash’hadi hakkinsa a halin sani da kuma bauta to hakika ya wadatu da Ubangijinsa kuma ya isar masa, kuma haka nan wanda iliminsa makewayi ya shaida da jinsa da ganinsa da rayuwarsa da tsayuwarsa da waninta kuma ba kowa ne yake arzurta da wannan mash’hadi ba face marigaya makusanta.


Kadaita Allah cikin sunayensa da siffofinsa


menene kishiyar tauhidin sunaye da siffofi?


kishiyarsa shi ne ilhadi cikin sunayen Allah da siffofinsa da ayoyinsa, kuma shi nau’i uku ne


na farko: ilhadin mushirikai wadanda suka karkatar da sunayen Allah Madaukaki daga yanda suke kuma suka kira da ita gumakansu sai suka kara kuma suka rage sai suka ciri laata daga Al-ilaah da kuma uzzaa daga Al-Aziiz da kuma manaata daga Al-Mannaan.


na biyu: ilhadin masu kamantawa sune wadanda suke kwaikwaita siffofin Allah Madaukaki kuma suke siffanta shi da irin siffofin halittarsa kuma shi ne mukabilin ilhadin mushirikai to wadannan sun daidaita ababan halitta da Ubangijin talikai, kuma wadannnan sun sanya shi matsayin jukkuna ababan halitta kuma suka siffanta shi da ita ya daukaka kuma ya tsarkaka abisa haka.


na uku: ilhadin masu korewa kuma su kaso biyu ne: kason da suka tabbatar da lafazan sunayensa Madaukaki kuma suka kore gare shi abin da suka kunsa na daga siffofin cika sai suka ce: Mai rahama Mai jin kai ba tare da rahama ba Masani ba tare da sani ba Mai ji ba tare da jib a Mai gani ba tare da gani ba Mai iko ba tare da kudura ba, kuma suka kore sauranta hakanan, da kuma kason da suka bayyana kore sunayen da abin da suka kunsa baki daya, sai suka siffanta shi da rashi tsantsa wanda ba shi da suna kuma ba shi da siffa tsarki ya tabbata ga Allah kuma ya daukaka ga abin da azzalumai masu musu masu ilhadi suke fada daukaka mai girma


Ubangijin sammai da kasa da abin da yake tsakaninsu to sai ka bauta masa, kuma ka yi hakuri ga bautarsa. Shin ka san wani takwara a gare shi


Babu abinda yayi kama da Allah kuma shi ne Mai ji kuma mai gani


yana sanin abin da yake tsakanin gabansu da kuma abin da yake bayansu kuma su ba su kewaye sani da shi ba


Dukkan nau’o’in tauhidi malizimta ne


shin dukkan nau’o’in tauhidi malizimta ne sai ya koreta dukkanta abin da yake kore wani nau’i daga gareta?


hakane ita malizimciya ce wanda yayi shirka cikin wani nau’i daga gare ta to shi yayi shirka a sauran, misalin wannan shi ne kiran wanin Allah da rokonsa cikin abin da ba mai iko akansa face Allah,to kiranta


ita kadai ibada ne kai tsantsar ma ibada wacce ya juyar da ita ga wanin Allah ba Allah ba to wannan shirka ce cikin Ilahiyya.kuma rokonsa shi kadai wannan bukata ta samin alheri ko ije wani sharri yana mai kudirta cewa shi mai iko ne a bisa bada wannan, wannan shirka ce cikin rububiyyarsa ta yanda ya kudirce cewa shi mai tasarifi ne tare da Allah cikin mamallakarsa,sannan cewa shi bai roke shi wannan Addu’a daga koma bayan Allah ba face tare da kudirinsa cewa shi yana jinsa a bisa nesa da kuma kusa a cikin kowane lokaci ya kasance da kuma kowane guri kuma suna bayyanawa da wancananka kuma shi shirka ne cikin sunayen da siffofin ta yadda ya tabbatar masa da ji mai kewayewa da dukkan majiyai kusanci ba ya yi masa hijabi hakana nisa sai wannan shirka ta lazimta a cikin uluhiyya shirka cikin rububiyya da sunaye da kuma siffofi.


Dalili bisa imani da Mala’iku daga Alkur’ani da sunna


menene dalili a bisa imani da Mala’iku daga Alkur’ani da sunna?


Dalilan suna da yawa daga Alqur’ani da kuma Sunnah daga cikinsu akwai faxin Allah Maxaukakin Sarki


dalilan wancananka daga Alkur’ani suna da yawa yana daga ciki fadinsa Madaukakin sarkai:


Allah Madaukakin Sarki yana cewa:


Lalle ne, waɗanda ke wurin Ubangijinka bã su yin girman kai ga bauta Masa, kuma sunã tsarkake shi da tasbĩhi, kuma a gare shi suke yin sujada.


Allah Madaukakin Sarki yana cewa:


Wanda ya kasance maƙiyi ga Allah da malã'ikunSa da manzanninSa da Jibirĩla da Mĩkã'ĩla to, lalle ne, Allah Maƙiyi ne ga kãfirai.


kuma imani da su ya gabata daga sunna cikin hadisin Jibrila da waninsa, da kuma cikin sahihi Muslim cewa Allah Madaukakin sarki ya halicce su daga haske, kuma hadisai cikin sha’aninsu suna da yawa.


ma’anar imani da Mala’iku


menene ma’anar imani da Mala’iku?


shi ne ikrari yankakke da samuwarsu kuma cewa su halitta ce daga halittun Allah horarru kuma bayi ne masu girma


Bã su gabãtarSa da magana, kuma su da umurninSa suke aiki.


ba sa sabawa Allah ga abin da ya umarce su kuma suna aikata abin da ake umartarsu


Kuma waɗanda suke wurinSa (watau malã'iku), bã su yin girman kai ga ibãdarSa. kuma bã su gajiya.


kuma ba sa kosawa kuma ba sa gajiya.


nau’o’in Mala’iku ta izina da yadda Allah ya tanade su gare shi kuma ya wakilta su da shi


ka ambaci sashin nau’o’insu ta izina da yadda Allah ya tanade su gare shi kuma ya wakilta su das hi?


su ta izina da wancananka kashe kashe ne masu yawa, yana daga cikinsu wanda aka wakilta da kaiwa Manzanni wahayi, shi ne Ruhi amintacce Jibril Aminci ya tabbata a gare shi


kuma akwai daga cikinsu wanda aka wakilta da ruwa, shi ne Mika’il amincin Allah ya tabbata a gare shi.


kuma akwai daga cikinsu wanda aka wakilta da ruwa, shi ne Mika’il amincin Allah ya tabbata a gare shi.


kuma akwai daga cikinsu wanda aka wakilta da karbar rayuka, shi ne Mala’ikan mutuwa da mataimakansa.


kuma akwai daga cikinsu wanda aka wakilta da aiyukan bayi, sune masu girma Marubuta


kuma akwai daga cikinsu wadanda aka wakilta da kiyaye bawa daga gaba gare shi da kuma bayansa, su ne masu lura.


kuma daga cikinsu akwai wadanda aka wakiltawa Aljanna da ni’imominta, su ne Ribwan da wadanda suke tare da shi.


kuma akwai daga cikinsu wadanda aka wakiltawa wuta da azabarta, su ne Maliku da wadanda suke tare da shi daga Zabaniyawa kuma shugabanninsu goma sha tara ne.


kuma akwai daga cikinsu wadanda aka wakilta da fitinar kabari, su ne Munkar da Nakiir.


kuma suna daga cikinsu masu dauke da Al’arshi


kuma daga cikinsu akwai karubiyawa.


kuma akwai daga cikinsu wadanda aka wakilta da digon maniyyi a cikin mahaifa da kuma halittata da kuma rubuta abin da ake nufi da ita.


kuma akwai daga cikinsu wasu Mala’iku wadanda suke shiga baitul ma’amuri a kowace rana Mala’ika dubu saba’in ne suke shigarsa kuma ba sa dawowa izuwa gare shi,da kuma wasu Mala’iku das uke yawo suna bibiyar guraren zikiri.


kuma akwai daga cikinsu masu sahu suna tsaye ba sa kosawa.


kuma akwai daga cikinsu masu ruku’u ba sa dagowa


kuma akwai daga cikinsu wadanda ba wancananka ba


Kuma bãbu wanda ya san mayãƙan Ubangijinka fãce Shi, kuma ita (wutar) ba ta kasance ba fãce wata tunãtarwa ce ga mutum.


kuma nassoshin wannan kashe kasha daga Alkur’ani da sunna ba ya buya.


dalilin imani da littattafai


menene dalilin imani da littattafai?


Akwai dalilai ma su yawa daga ciki akwai faxin Allah Madaukakin Sarki:


Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku yi ĩmãni da Allah da Manzonsa, da Littãfin da Ya saukar ga ManzonSa da Littãfin nan wanda Ya saukar daga gabãni.


Allah Madaukakin Sarki yana cewa:


Ku ce: "Mun yi ĩmãni da Allah, da abin da aka saukar zuwa gare mu, da abin da aka saukar zuwa ga Ibrãhĩm da Ismã'ĩla da Is'hãka da Ya'aƙũbu da jĩkõki, da abin da aka bai wa Mũsã da Ĩsã, da abin da aka bai wa annabãwa daga Ubangijinsu, bã mu rarrabewa a tsakãnin kõwa daga gare su


kuma ya isa cikin wancananka fadinsa Madaukakin sarki:


kuma ka ce, "Nã yi ĩmãni da abin da Allah Ya saukar na littãfi.


shin an ambaci gaba ki dayan littattafan nan a cikin Alkur’ani


shin an ambaci gaba ki dayan littattafan nan a cikin Alkur’ani


Allah ya ambata daga cikinsu a cikin Alkur’ani shi da Attaura da Linjila da Zabura da suhufiIbrahim da Musa kuma ya ambaci sauran a jumlace sai ya ce:


Allah, bãbu wani abin bautawa fãce Shi, Rãyayye Mai tsayuwa da kõme Yã sassaukar da Littãfi a gare ka da gaskiya, yana mai gasgatãwa ga abin da ke gaba gare shi, kuma Allah Yã saukar da Attaura da Linjĩlã a gabãni


kuma Allah Madaukaki ya ce


kuma mun bawa Dawuda littafin Zabura


kuma Allah Madaukaki ya ce


Ko kuwa ba a ba shi lãbãri ba ga abin da yake a cikin Littafan Mũsã da Ibrãhĩm wanda ya cika alkawari?


kuma Allah Madaukaki ya ce


Haƙĩƙa, lalle Mun aiko ManzanninMu da hujjõji bayyanannu, kuma Muka saukar da Littãfi da sikeli tãre da su dõmin mutãne su tsayu da ãdalci


to abin da Allah ya fada daga cikinsu a warware to ya wajaba a kanmu mu yi imani da shi a warwaren, kuma wanda ya ambata daga cikinsu a jimlace to ya wajaba a kanmu imani da shi a jimlacesai mu fada a cikinsa abin da Allah ya yi umarni da shi da Manzansa


kuma ka ce, "Nã yi ĩmãni da abin da Allah Ya saukar na littãfi.


Menene ma’anar imani da Litattafan Allah Mai girma da daukaka?


Menene ma’anar imani da Litattafan Allah Mai girma da daukaka?


ma’anarsa gasgatawa yankakkiya da cewa dukkansu ababan saukarwa ne daga Allah Mai girma da daukaka kuma cewa Allah yayi zance da ita a hakika akwai daga cikinta abin ji daga gare shi Madaukakin sarki daga bayan hijabi ba tare da wasidar Manzo Mala’ika ba, kuma akwai daga gare ta wanda Manzo Mala’ika zai isar da shi izuwa Manzo Mutum, kuma akwai daga gare ta abin da Allah Madaukakin sarki ya rubuta da hannunsa kamar yadda Allah Madaukaki ya fada:


Kuma bã ya kasancewa ga wani mutum Allah Ya yi masa magana fãce da wahayi, kõ daga bãYan wani shãmaki, kõ Ya aika wani Manzo, sa'an nan Ya yi wahayi, da izninsa ga abin da Yake so


Allah Maxaukakin Sarki yace akan Annabi Musa


ya ce: "Ya Mũsã! Lalle ne Nĩ, Nã zãɓe ka bisa ga mutãne da manzanciNa, kuma da maganãTa


Kuma Allah yayi magana da Musa Magana sosai


Kuma Ubangiji madaukaki ya fada acikin Maganar Attaura:


Kuma Muka rubũta masa a cikin alluna daga kõwane abu, wa'azi da rarrabewa ga dukan kõwane abu


Ya ce akan Annabi Isa


kuma mun bashi Linjila


kuma Allah Madaukaki ya ce


kuma mun bawa Dawuda Zabura


kuma ambatonta ya gabata da lafazin saukarwa


Allah Madaukakin Sarki yana cewa acikin Sha'anin Alkur'ani:


Amma Allah Yanã shaida da abin da Ya saukar zuwa gare ka. Yã saukar da shi da saninSa. Kuma malã'iku sunã shaida. Kuma Allah Yã isa Ya zama shaida.


Allah Madaukakin Sarki yace acikin ta


Kuma yanã abin karãtu Mun rarraba shi dõmin ka karanta shi ga mutane a kan jinkiri kuma Mun sassaukar da shi sassaukarwa


kuma Allah Madaukaki ya ce


Kuma lalle shi (Alƙur'ãni), haƙĩƙa, saukarwar Ubangijin halittu ne. Rũhi amintacce ne ya sauka da shi. A kan zũciyarka dõmin ka kasance daga mãsu gargaɗi Da harshe na Larabci mai bayãni.


Allah Madaukakin Sarki yace acikinta


Waɗannan da suka kãfirta game da Alkur'ãni a lõkacin da ya je musu, kuma lalle shi haƙĩƙa littãfi ne mabuwãyi. Ɓarna bã zã ta je masa ba daga gaba gare shi. kuma bã zã ta zo ba daga bãya gare shi. Saukarwa ce daga Mai hikima, Gõdadde.


da wadansunsu da yawa.


matsayin Alkur’ani daga sauran littattafan


menene matsayin Alkur’ani daga littattafan da suka gabata?


Allah Madaukakin Sarki ya ce:


Kuma Mun saukar da Littãfi zuwa gare ka da gaskiya, yanã mai gaskatãwa ga abin da yake a gaba gare shi daga Littãfi (Attaura da Injĩla), kuma mai halartãwa a kansa


kuma Allah Madaukaki ya ce


Kuma wannan Alƙur'ãni bai kasance ga a ƙirƙira shi ba daga wanin Allah, kuma amma shi gaskatawar wannan ne da yake a gabãninsa da bayãnin hukuncin littãffan Allah, Bãbu shakka a cikinsa, daga Ubangijin halittu yake.


kuma Allah Madaukaki ya ce


Bai kasance wani ƙirƙiran lãbãri ba kuma amma shi gaskatãwa ne ga abin da yake a gaba gare shi, da rarrabewar dukan abũbuwa, da shiriya da rahama ga mutãne waɗanda suka yi ĩmãni


ma’abota tafsiri sun ce: Muhaiminan Mai amintarwa kuma Mai shaida a bisa abin da ya zo kafinsa na daga littattafai kuma mai gasgatawa da ita, yana nufin yana gasgata abin da yake cikinta na daga inganci, kuma yana kore abin da ya ya afku a cikinta na daga canji kuma yana hukunci a kanta da shafewa ko tabbatarwa, saboda haka ne duk wani mai ruko da littattafan da suka gabata yake kaskantar da kai a gare shi daga cikin wadanda basu juya masa baya ba kamar yadda Allah Madaukaki ya ce:


wadanda muka ba su littafi kafin shi su suna yin imani da shi kuma idan aka karanta a gare su sai su ce: mun yi imani da shi lalle shi gaskiya ne daga ubangijinmu lalle mu mun kasance kafin shi masu mika wuya.


abin da ya wajaba a lazimce shi cikin hakkin Alkur’ani


menene ya wajaba a lazimce shi cikin hakkin Alkur’ani a bisa dukkan al’umma?


shi ne binsa a zahiri da badini da ruko da shi da kuma tsayawa da hakkinsaAllah Madaukaki ya ce


kuma wannan littafi ne da muka saukar da shi mai albarka to ku bi shi kuma ku ji tsoro


kuma Allah Madaukaki ya ce


ku bi abin da aka saukar izuwa gare ku daga Ubangijinku kuma kada ku bi wasu masoya koma bayansa


kuma Allah Madaukaki ya ce


kuma wadanda suke ruko da littafin kuma suka tsaida salla lalle mu ba ma tozarta ladan managarta


kuma ita ta hade komai cikin kowane littafi da ayoyi cikin wancananka masu yawa, kuma Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yi wasiyya ga littafin Allah sai ya ce:” ku kama littafin Allah kuma ku yi ruko da shi” kuma a cikin hadisin Aliyyu marfu’I “ cewa da sannu wasu fitinu za su kasance” na ce : menene mafita daga gare ta ya ma’aikin Allah? Ya ce:” littafin Allah” kuma ya ambaci hadisin


menene ma’anar rook da Alkur’ani da kuma tsayawa da hakkinsa?


menene ma’anar rook da Alkur’ani da kuma tsayawa da hakkinsa?


kiyaye shi da karanta shi da tsayuwa das hi dare da rana da yin tadabburi ga ayoyinsa da kuma halarta halalinsa, da kuma haramta haram dinsa da kuma jawuwa ga umarninsa, da tsawatuwa daga abin da ya tsawatar da kuma lura da misalansa, da wa’aztuwa da kissoshinsa da aiki da muhkaminsa, da mika wuya ga mutashabihinsa da tsayawa ga iyakokinsa, da korewa ga barinsa canzawar


Hukuncin wanda ya ce Alkur’ani halitta ne


menene Hukuncin wanda yace Alkur’ani halitta ne?


Alkur’ani zancan Allah ne Mai girma da daukaka tabbas harafansa da ma’anoninsa ba wai zancansa harafai ne banda ma’anoni ba kuma ba ma’anoni ne ba banda harafai Allah yayi Magana da shi Magana kuma ya saukar da shi a bisa Annabinsa a wahayi kuma muminai sun yi imani da shi tabbas to shi duk da cewa an rubuta shi da yatsu kuma an karanta shi da harshe kuma an hadda ce shi da a zuciya kuma ana jinsa da kunnuwa kuma idanuwa biyu suka ganshi hakan ba zai fitar da shi daga kasancewarsa zancan Mai rahama ba,To ‘yan yatsu da tawwadu da takardu abin halitta ne abin da kuma aka rubuta da ita baa bin halitta ba ne kuma harsuna da sautuka abin halitta ne abin da ake karantawa da ita a bisa sabaninta baa bin halitta ba ne, kiraza abin halitta ne amma kuma abin da ake haddacewa a cikinta baa bin halitta ba ne, kuma majiyu abin halitta ne amma abin da ake jin baa bin halitta ba ne


Allah Madaukakin Sarki ya ce:


Lalle shi (wannan littãfi), haƙĩƙa, abin karantãwa ne mai daraja. A cikin wani littafi tsararre


kuma Allah Madaukaki ya ce


Ã'a, shĩ ãyõyi ne bayyanannu a cikin ƙirãzan waɗanda aka bai wa ilmi. Kuma bãbu mai musun ãyõyinMu fãce azzãlumai


kuma Allah Madaukaki ya ce


ka karanta abin da aka yi wahayi izuwa gare ka daga littafin Ubangijinka babu mai canzawa ga kalmominsa


kuma Allah Madaukaki ya ce


Idan wani daga mushirikai ya nemi maƙwabtakarka to, ka ba shi maƙwabtakar har ya ji, maganar Allah


Kuma dan Mas’ud Allah ya yarda da shi ya ce: “ku dauwamar da ganinku cikin mus’hafi, kuma nassoshi a cikin wannan ba za su kidanyu ba


Duk wanda yace Alqur’ani ko wani abu daga cikin Alqur’ani halitta ne to ya kafirta kafici mai girma wanda zai fitar da shi daga musulunci gaba daya ,saboda Alqur’ani zancen Allah Maxaukakin Sarki ne da shi ya fara gare shi kuma yake komawa zancen sa kuma siffara sa ne wanda duk yace wata siffa ta Allah halitta ce to shi kafiri ne yayi ridda za’a bijiro mai da komawa Musulunci ,idan ya koma shikenan idan kuma yaqi sai a kasha shi a kafiri bas hi da wata dangantaka da hukunce hukuncen da suka hau kan Musulmi


siffar zance zati ce ko aiki ce


Shin siffar zance zati ce ko aiki ce?


Wajen bayyana cewa siffar zancen Allah da jingina shi da Zatin Allah Maxaukakin Sarki da kuma siffanta Allah Maxaukakin Sarki da shi daga cikin siffar Zatin Allah akwai Iliminsa ya saukar da shi da iliminsa kuma shine mafi sanin abinda ya saukar ,amma wajen bayyana zancensa da ikonsa da qudirarsa siffarsa aiki ce kamar yadda Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi yake cewa


‘’Idan Allah Madaukakin Sarki ya yi niyyar wahayi kan wani abu sai yayi magana da wahayi‘’


Hadisi


Da wannan ne Magabata na qwarai Allah yayi musu rahama suke cewa akan siffar zancen Allah Madaukakin Sarki cewa shidin siffa ce ta zatin Allah tare da aikinsa a tare ,Allah Madaukakin Sarki bai gushe ba kuma ba zai gushe ba ana siffanta shi da zaance ba har abada ,kuma yin zance dashi da zancen shi da ikonsa ne da qudurarsa yana yin zance a lokacin da ya so da yadda ya so yin zancen wanda kadai ya so ne zai iya sauraronsa ,haka kuma zancen sa ba shi da maqura ba shi da qarshe.


Da kogi zai zamo Tawwada da zai rubuta kalmomin Ubangiji Na da Kogin ya qafe kafin Kalmomin Ubangijina su qare ko da kuwa za’a karo kwatankwacin sa


Da za’a mayar da duk wata Bishiya Alqalami kogi kuma a mayar da shi Tawwada bayan shi da akwai wasu Koguna guda bakwai a rinqa qarawa Kalmomin Allah ba za su qare ba ba


Kuma kalmomin Ubangijinka sun cika da gaskiya da kuma adalci babu wani da ya isa ya canja kalmomin sa haqiqi shine Mafi ji kuma mafi Sani


Al Wafiqa kuma mene hukuncinsu?


Su wane Al W afiqa me ne kuma hukuncinsu?


Al Wafiqa sune wadan da suke cewa akan Alqur’ani ba zamu ce Alqur’ani zancen Allah ne ba kuma ba zamu ce abin halitta ne ba ,Imam Ahmad Allah yayi masa rahama yana cewa


Duk wanda ya kasance yana kyautata zancen to shi Dan Jahamiyya ne wanda kuma ya kasance baya kyautatawa to ya zamo jahili hujja zata tsaya akansa da bayani tare da hujja, sai dai idan ya tuba ya kuma yi Imani da cewa Aqur’ani zancen Allah ne ba halitta ba ne ,in bahaka ba kuma to shi wani sharri ne daga Jahamiyya"


Hukuncin wanda ya furta cewa Alqur’ani halitta ne


Mene ne Hukuncin wanda ya furta cewa Alqur’ani halitta ne


Wannan maganar bai halatta abarta ba haka kawai a sakewajen hani ko tabbatarwa; saboda lafazin a ma’anarsa ya haxu ne tsakanin furta lafazin wanda shi aikin Bawa ne,da abinda aka urta lafazin akan shi wanda shine Alqur’ani idan aka saki maganar kan cewa halitta ne sai ya dauki ma’ana ta biyu, ya koma kaga fadin Jahamiyya, idan kuma aka ce shi Alqur’anin ba halitta ba ne shi kuma ya hada ma’anar farko wanda shine aikin Bawa ,shi kuma wannan yana daga cikin Bidi’ar Ittihadiyya da wannan ne Magabata na qwarai suke cewa: ’’Duk wanda a furta cewa Alqur’ani halittane to shi Dan Jahamiyya ne ,wanda kuma yace ba halitta bane ta shi kuma Dan Bidi’a ne


Dalilin Imani da Manzanni


Me ne ne dalilin Imani da Manzanni?


Dalilan suna da yawa daga Alqur’ani da kuma Sunnah daga cikinsu akwai faxin Allah Maxaukakin Sarki


Lallai Wadan da suka kafircewa Allah da Manzonsa kuma suke son su raba tsakanin Allah da Manzonsa suna faxin mun yi Imani da wani sashi na Littafi mun kuma kafircewa wani sashin suna son su samu a tsakanin haka wata hanya waxannan su kafirai na gaske kuma haqiqa mun tanadarwa kafirai azaba ta wulaqanci; Waxanda suka yi Imani da Allah da Manzonsa basu kuma yi qoqarin raba tsakaninsu ba wadannan haqiqa zamu basu sakamakonsu


Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:


Nayi Imani da Allah da Manzonsa


Maanar Imani da Manzanni


Mene ne Imani da Manzanni?


Shi ne gasgatawa da kuma tabbatarwa haqiqa Allah Madaukakin Sarki ya aikowa kowacce Al’ummah daga cikinsu akwai wadanda suka kira su zuwa ga bautawa Allah shi kadai ,da kuma kafircewa bautawa wani abu ba Allah ba kuma daukkaninsu sun yi Imani da sun gasgata sun kuma zamo masu biyayya shiryayyu,masu karamci tsarkaka masu tsoron Allah Shiryayyu masu shiryarwa ,da hujjoji mabayyana da Ayoyi baiyanannu daga Ubangijinsu tabbatattu, cewa Su haqiqa sun isar da gabaki dayan abinda Allah ya aiko su su Boye ba ba su kuma canja ba ba su qara komai a ciki ba dai dai da harafi kuma basu rage shi ba.


Haqiqa babu komai akan Manzanni sai isar da saqo


Dukkaninsu sun kasance akan gaskiya bayyananniya ,Allah Madaukakin Sarki ya zabi Annabi Ibrahim Badadinsa ,Ya kuma zavi Annabi Muhammad tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi Badaxi ya kuma yi zance da Annabi Musa zance , Ya daga Annabi Idris zuwa wuri madaukaki , sannan Annabi Isa Bawan Allah ne kuma Kalmarsa ne Ya jefa ta izuwa ga Maryama kuma Ruhi ne daga gare shi kuma Allah ya fifita sashensu bisa wani Sashen Ya daukaka darajar wasunsu akan wasu.


Da’awar Manzanni gaba daya ta hadu ne kan abinda suke umarni da kuma hani


Shin Da’awar Manzanni gabadaya ta hadu ne kan abinda suke umarni da kuma hani?


Gabaki dayan Da’awarsu ta hadu ne tun daga kan na farkon su har zuwa na qarshensu kan asalin ibada da tushenta shi ne Tauhidikan kadaita Allah a dukkanin nau’o’in bauta daga kan qudurcewa da Magana da kuma aiki tare da kuma kafircewa bautawa duk wani abu ba Allah ba.


Wajiban da aka wajabta yin bauta dasu sune Sallah da Azumi da wasunsu ba’a wajabta kan sauran ba ,an haramta akan su abinda aka halatta akan sauran jarrabawa ce daga Allah Madaukakin Sarki:


Dan ya jarrabe ku ya ga Waye mafi kyautata aiki daga cikin ku.


Dalili kan haxuwar Manzanni kan asalin Ibada


Me ne ne dalilin haduwar Manzanni kan Aslin bauta wacce aka ambata ?


Dalili akan haka daga Littafi nau’I biyu ne Mujjamal da Mufassal


A dunkule shi ne misalign fadin Allah Madaukakin Sarki:


Haqiqa mun aiko ga kowacce Al’ummah Manzo ku bautawa Allah ku kuma guji bautawa Dagutu


Allah Madaukakin Sarki yana cewa:


Bamu tura gabaninka ba wani Manzo face mun yi masa wahayi cewa babu wani Allah face Ni ku bauta mi ni


Allah Madaukakin Sarki yana cewa:


Ka tambaa kan waxanda muka turo gabaninka daga Manzannin mu shin mun sanya musu komabayan Allah wani abin bauta


A bayyane kuma shi ne misalin fadin Allah Madaukakin Sarki:


Haqiqa mun aika da Annnabi Nuhu zuwa ga mutanen sa yana mai cewa dasu yak u mutane na ku bautawa Allah ba ku da Allah bayan shi


Mun aika zuwa ga Samudawa Dan uwansu Salih yace yaku mutane na ku bautawa Allah ba ku da wani Allah bayan shi


Mun aika zuwa ga Adawa Dan uwansu Hud yace yak u mutane na ku bautawa Allah ba ku da wani Allah bayan shi


Mun aika zuwa ga Mutanen birnin Madyana Dan uwansu SHu'aib yace yak u mutane na ku bautawa Allah ba ku da wani Allah bayan shi


Kuma ku tuna lokacin da Annabi Ibrahim yana cewa babansa da mutanensa haqiqa Ni na barranta daga abinda kuke bautawa sai ga wanda ya halicce ni


Musa yace hakika Allah shi ne Ubanginku babu wani Allah bayan shi saninsa ya mamaye dukkan komai


Al'masihu kuma ya ce: :


Ya ku Banu Isra’ila ku bautawa Allah Ubangiji na kuma Ubangijinku hakika duk wanda ya hada shi da abokin tarayya haqiqa Allah ya haramta masa Aljannah sannan mokomarsa wuta


Ya ce Ni ba kowa bane sai mai gargadi hakika babu wani Allah face Allah Madaukakin Sarki


Da wasun su Ayoyin


Dalilin sabanin shari’o’insu kuwa yana daga rassan ta na daga Halal da kuma Haram


Me nene Dalilin sabanin shari’o’insu ta vangaren rassan ta daga Halal da kuma Haram?


Fadin Allah maigirma da Daukaka:


Ga kowanne mun sanya muku shari’ah da kuma hanya da Allah ya so da ya sanya ku Al’ummah guda xaya amma sai dai dan ya jarabceku cikin abinda aka baku kuyi rigegeniya wajen aikata Alheri


Ibn Abbas Allah ya yi masa rahama ya na cewa ‘’Shari’ah da Hanya’’hanya ce da Sunnah misalign hakan Mujahid da Ikramata da Hasanul Basri da qatada dDihak da Sudai da Abu Ishaq Assubay’,a cikin Sahihul Bukhari Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi yana cewa: ’’Mu Annabawa yan uwa ne saboda munufar addinmu daya ne ‘’yana nufin Tauhidi wanda Allah ya aiko dukkannin Manzanni da shi kuma kowanne Littafi da aka saukar ya qunshe shi ,amma shari’o’I sun banbanta a umarni da kuma hani da kuma cikin Halal da kuma Haram


Dan ya jarrabe ku ya ga Waye mafi kyautata aiki daga cikinku.


Shin Allah ya bada labarin dukkanin Annabawa a cikin Alqur’ani


?Shin Allah ya bada labarin dukkanin Annabawa a cikin Alqur’ani


Hakika Allah Madaukakin Sarki ya bamu labarin kissoshin su abinda zai ishe mu ya kuma zamo wa’azi da kuma darasi a gare mu sai Allah Madaukakin Sarki y ace:


Wasu Manzannin mun baka labarin su tun a farko wasu kuma bamu baka labarinsu ba


Zamu yi Imani da dukkanninsu a rabe a wajen da aka raba ,a kuma hade a wajen da aka hade.


Annabawan da aka ambaci sunan su a Qur’ani


Nawa ne Annabawan da aka ambaci sunan su a cikin Alqur’ani?


Daga cikin wadan da aka ambaci sunan su akwai :Adam,da Nuh da Idris da Hud da Salih da Ibrahim da Isma’il da Ishaq da Ya’aqub da Yusuf da Lud da Shu’aib da Yunus da Musa da Haruna da Ilyas da Zakariya da Yahya da Yasa’ da Zal kifil da Dawud da Sulaiman da Ayyub an ambaci Al’Asbad a jumlace da Isa da Muhammad tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi tare da su baki daya


Ulu-Azm na Manzanni


Su waye Ulu-Azm daga Manzanni


Su biyar ne Allah ya ambace su daya bayan daya a wurare guda biyu a cikin Alqur’ani ,wuri na farko cikin Suratul Ahzab shi ne fadin Allah Madaukakin Sarki


A lokacin da muka kulla alkawari da Annabawa tare da kai da Nuh da Ibrahim da Musa da Isa Dan Maryam


Wuri na biyu kuma a Suratus Shura shine fadin Allah Madaukakin Sarki:


An shar’anta muku a cikin addini abinda aka y Nuhu wasiyya da shi da abinda muka yi maka wahayi da abinda muka yi wa Ibrahim da Musa da Isa wasiyya da shi Su tsaya akan addini kada Su rarraba a cikinsa


farkon Manzanni


Wa ne ne na farkon Manzanni:


Na farkon su bayan sabanin da aka samu shi ne Nuh amincin Allah ya tabbata a gare shi kamar yadda Allah madaukakin Sarki yace:


Hakika mun yi wahayi gare ka kamar yadda muka yi wahayi zuwa Nuh da Annabawan da suka zo bayan shi


kuma Allah Madaukaki ya ce


Kafin su mutanen Nuh sun karyata shi tare da jama’ar da suka zo bayansu


Yaushe ne sabanin ya faru?


Ibn Abbas yardarm Allah ta tabbata a gare shi yana cewa :tsakanin Annabi Nuh da Annabi Adam Karni goma ne dukkaninsu sun kasance akan shari’a ta gaskiya sai suka yi sabani


Sai Allah ya aiko Manzanni masu bushara da gargadi


Cika makin Annabawa


Wa ne ne cikamakin Annabawa?


Cika makin Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi


Me ne ne dalili akan haka?


Allah Madaukakin Sarki ya ce


Annabi Muhammadu bai zamo Uban daya daga cikin mazajenku ba sai dai shi Manzon Allah ne kuma cikamakin Annabawa


Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:


Hakika a bayana zai kasance a sami wasu mutane Makaryata su talatin dukkaninsu zasu zo suna da’awar Annabta kuma ni ne cikamakin Annabawa babu wani Annabi baya na


Yazo a cikin Sahihul Bukhari maganarsa ga Aliyu Allah ya yarda dashi


Shin ba zaka yarda ka zamo min kamar yadda Annabi Haruna yak e ga Musa ba sai dai babu wani Annabi bayan ni


Kuma fadin Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi a cikin Hadisin Dujal


Ni ne cikamakin Annabawa babu wani Annabi baya na


Abinda Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya kebanta da shi daga sauran Annabawa


Abin da Annabi tsira da Amincin Allah su kara tabbata a gare shi ya kebanta da shi daga sauran Annabawa?


Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi yana da abubuwa masu yawa da ya kebanta da su daga cikinsu akwai: kasancewarsa cikamakin Annabawa kamar yadda muka ambata ,sannan kuma akwai kasancewar sa Dan Annabi Adam kamar yadda fadin Allah Madaukakin Sarki ya fassara:


Wadan can Annabawan mun fifita sashensu akan sashe daga cikin su akwai wanda Allah ya yiwa Magana ya Daukaka darajar wadansunsu


Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi yana cewa ‘’ Ba ina alfahari ba ne Nine shugaban yayan Adam’’daga cik kuma an aiko Annabi trira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi zuwa ga mutane baki daya Aljanunsu da kuma mutanensu kamar yadda Allah Madaukakin Sarki y ace:


Ya ku mutane ni manzon Allah ne zuwa gare ku baki Daya


kuma Allah Madaukaki ya ce


Bamu aiko ka ba sai zuwa ga mutane baki daya Mai gargadi kuma Mai bushara


Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi yace


An bani cin nasara ta hanyar tsoro (da ake jefawa abokan gaba)wata daya gabanin haduwar mu, kuma aka sanya mini kasa ta zama wajen yin sallah na kuma abar yin tsarki,don haka duk wanda salla ta


riske shi cikin al'umma ta to sai ya yi ta, kuma an halarta min ganima, ba'a taba halartawa wani kafin ni ba, kuma an bani ceto, ya kasance ana aiko Annabi zuwa ga mutanensa kadai, Ni kuwa an aiko ni zuwa ga mutane gaba daya


Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce


Na rantse da wanda raina ya ke hannunsa babu wani a cikin wannan Al’ummah Bayahude ko Nasara da zai ji wani abu game dani,sannan ya mutu bai yi Imani da abinda aka aiko ni da shi face sai ya zamo daga cikin yan wuta


Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi yana da abubuwan da ya kevanta dasu da yawa waxanda bamu ambata ba ka bibiye su cikin nassoshi


Mu’ujizar Annabawa


Me ce ce Mu’ujizar Annabawa?


Mu’ujiza wani abu ne da ya sabawa Al’ada ba’a saba ganin shi ba wanda yake hade da qalubale ,imam dai ta kasance abinda ido zai iya gani ce ko abinda za’a iya ji kamar fitar Taguwa daga dutse da kuma juyewar Sanda ta zamo Micijiya da maganar abubuwan da su da rai da wasun haka ko kuma wanda shi ba jiki bane da za’a iya gani da ido kamar Mu’ujizar Alqur’ani


Duk wadan nan an bawa Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi babu wata Mu’ujiza da wani Annabi yake da ita face an bashi ita shima mafi girmanta daga cikinsu tsagewar Wata da begen kututturen Dabino da bulbular ruwa daga tsakankanin yanyatsun sa masu daraja da maganar karfata da tasbihin Abinci da wasun hakan wadan da suka zo cikin Labarai masu inganci sai sub a kamar sauran Mu’ujizozin Annabawa bane wadan da aka hada su da wadan su abubuwan ba.


Babu abinda yayi saura daga gare sai ambatonta ,Mu’ujizar da ta wanzu itace Mu’ujizar Alkur’ani wacce abubuwan mamakinta basa Karewa sannan vata bata shigarsa ta dukkanin geffansa ta gabansa ko ta bayansa saukakke ne daga Mai Hikima abin Godewa


Dalilin Mu’ujizar Alqur’ani


Mene ne Dalilin Mu’ujizar Alqur’ani?


Dalili kan haka shine saukar da Alkur’ani fiye datsahon shekara ashirin yana kalubalantar mafi fasahar halittu kuma mafi iya zancenta mafi balagarta mafi daukaka wajen iya bayani yana mai cewa:


Su zo da wani zancen kwatankwacinsa in sun kasance masu gaskiya


kace musu su zo da Surori goma in kun kasance Masu gaskiya ne


kace musu su zo da Surori goma kwatankwacinsa wadanda sukekirkirarru


Basu aikata hakan ba duk da tsananin kwadayinsu wajen yin raddi ga Alqur’ani da duk abinda za su iya saboda kasantuwar Harufansa daga jinsin harshen da suke Magana da shi suke rigegeniya kuma suke alfahari da shi sai akayi kira da bayanin mu’ujizarsa gazawarsu da bayyana


Da mutane da Aljanu za su haxu kan su zo da kwatankwacin wannan Alqur’’anin ba zasu zo da shi ba koda kuwa sashinsu yana taimakar sashi


Annabi tsira da Amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:


Babu wani Annabi daga cikin Annabawa face an bashi daga cikin Ayoyi wadan da mutane za su yi Imani da shi Ni kuma abinda aka bani shi ne wahayi Allah yana yi min wahayi ina fatan na fisu mabiya ranar tashin Alqiyama


Mutane sun wallafa Littattafai kan mu’ujizar Alqur’ani ta fuskar Laffuzan sa da ma’anoninsa da labaran wadan da suka gabata da wadan da zasu zo wadan da gaibu ne duk da haka basu kai maqurar sa ba face kamar yadda Tsuntsu yake tsoma bakin sa cikin kogi


Dalilin Imani da Ranar Lahira


Mene ne Dalilin Imani da Ranar lahira?


Allah Madaukakin Sarki ya ce


Lalle ne wadanda bas u qaunar gamuwa da mu ,kuma suka yarda da rayuwar duniya kuma suka nutsu da ita ,da wadan da suke gafalallu ne daga ayoyinmu.Wadan nan matattararsu Jahannama ce saboda abinda suka kasance suna tsuwurwurta


kuma Allah Madaukaki ya ce


Lallai abinda ake yi muku alqawari(da zuwansa),haqiqa gaskiya ne kuma lallai sakamako (ga aiyukanku) haqiqa mai afkuwa ne


kuma Allah Madaukaki ya ce


Kuma lallai ne Sa’ar Tashin Alqiyama mai zuwa ce babu shakka a cikinta


Da wasunsu na daga ayoyi.


Mene ne Ma'anar Imani da Ranar lahira?


Me ne ne ma’anar Imani da ranar lahira me ne ne kuma zai shiga cikinta ?


Ma’anarta shi ne Imani tabbatacce kan cewa lallai zata zoba makawada kuma aiki kan wajabcin haka Imani da Alamomin tashin Alqiyamav wadan da zasu faru ba makawa.


Da kuma mutuwa da fitinar da zata faru cikin kabari bayan mutuwar da azabarsa da ni’im ominsa da busar qaho da fitar halittu daga kabari da kuma abinda zai faru a filin tashin Alqiyama na daga firgici da rabe raben taron da raba takardu da awo da siradi da kogi da ceto da wasunsu da Aljannah da ni’imominta wanda mafi kololuwar ta shi ne ganin Allah Madaukakin Sarki da kuma Wuta da azabarta mafi tsananinta shi ne hijabi tsakaninsu da Ubangijinsu Madaukakin Sarki.


Zuwan Tashin Alkiyama yana daga cikin limin gaibu


Shin wani ya san yaushe Alqiyama zata tashi ?


Zuwan tashin Alqiyama yana daga ilimin gaibu wanda Allah Madaukakin Sarki ya boye saninta kamar yadda ya fada :


Lallai Allah a wurinsa kawai sanin Sa’a yake ,kuma yana saukar da girgije ,kuma yana sanin abinda yake cikin mahaifa kuma wani rai bai san abinda yake aikatawa gobe ba ,kuma wani rai bata san a wacce qasazata mutu ba.


kuma Allah Madaukaki ya ce


Suna tambayarka game da Sa’a,wai yaushe ne zata tabbata ?me ya hadaka da ambatonta? zuwa ga Ubangijinka qarshen al’amarinta yak e.


kuma Allah Madaukaki ya ce


Suna tambayarka game da Sa’a,wai yaushe ne zata tabbata ?me ya haxaka da ambatonta?zuwa ga Ubangijinka qarshen al’amarinta yak e.


A yayin da Mala’ika Jibril yacewa Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi bani labari akan Sa’a sai Yace: ’’Wanda ake tambaya bai fi wanda yake tambayar sani ba ‘’sai ya ambaci alamominta an qara a ruwayar: ’’cikin abubuwa guda biyar da babu wanda ya sansu sai Allah Maxaukakin Sarki’’ sai ya karanta ayoyin da suka gabata.


Alamomin Sa’a daga Alqur’ani


Me ne ne misalign alamomin Sa’a daga Alqur’ani?


Misalin faxin Allah Maxaukakin Sarki:


Shin suna jiran (wani abu )face dai mala’iku su je musu ko kuwa Ubangijinka ya je Aranar da sashen ayoyin Ubangijinka yake zuwa imanin rai wanda bai kasance yayi Imanin ba a gabani ,ko kuwa ya yi tsiwirwirin wani Alheri


Faxin Allah Maxaukakin Sarki:


Kuma idan Magana ta auku a kansu,Muna fitar musu da wata dabba daga qasa ,tana yi musu Magana cewa lallai mutane sun kasance game da ayoyinMu, basu yin imanin yaqini.


Allah Maxaukakin Sarki yana cewa:


Har sa’ar da aka bude Yajuju da Majuju alhali kuwa suna gaggawadaga kowanne tudun qasa Kuma wa’adin gaskiya ya gabato


Allah Maxaukakin Sarki yana cewa:


Saboda haka, ka dakata ranar da sama za ta zo da hayaqi bayyananne


Allah Maxaukakin Sarki yana cewa:


Yak u mutane !Ku bi Ubangijinku da Taqawa Lalle ne girgizar qasa ta tsayuwar Sa’a wata aba ce mai girma


Alamomin Sa’a daga Hadisi


Me ne ne misalign alamomin Sa’a daga Hadisi?


Misalin hadisin fitowar rana daga yamma da hadisin Dabbada hadisin fitintinu kamar Dujal da Yakuna.


Da hadisin saukowar Annabi Isa ,da fitowar Yajuju da Majujuda hadisin Hayaqi ,da hadisin Iska da zata xauki ran dukkanin Muminai da hadisin Wutar wacce zata bayyana da hadisin Kusufi da sauransu.


Dalilin Imani da Mutuwa


Me ne ne dalilin Imani da Mutuwa?


Allah ya yi masa Rahama


Kace :Mala’ikan mutuwa ne wanda aka wakkala a gare ku ,shi ne ke karvar rayukanku ,sannan zuwa ga Ubangijinku ake mayar da ku


kuma Allah Madaukaki ya ce


Kowacce rai mai dandanar mutuwa ce ,sa’annan zuwa gare mu ake mayar da ku


Sai yace da shi haqiqa Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi


Lallai kai zaka Mutu kuma suma zasu Mutu din


kuma Allah Madaukaki ya ce


Kuma bamu sanya dauwama ga wani mutum ba agabaninka Shin to idan ka mutu su madawwama ne?


kuma Allah Madaukaki ya ce


Dukkan wanda ke kanta mai qarewa ne,kuma fuskar Ubangijinka mai girma da Jalala da karamci irtace take wanzuwa


kuma Allah Madaukaki ya ce


Kowanne abu mai halaka ne face fuskarsa


kuma Allah Madaukaki ya ce


Ka dogara ga Mai ran da baya mutuwa


Akan wannan da hadisai waxanda ba zasu qirgu ba ,abin lura anan babu wanda zai jahilce shi babu kuma shakka acikinsa ko wani kaikawo sai dai cewa girman kai ba zai yi aiki kan wajabcin imaninsa da shi babu komai bayansa sai bayin Allah masu Ikhlasi mun kuma yi Imani cewa duk wanda ya mutu ko aka kasha da kowanne irin sababi ya kasance babu abinda zai rage shi da komai saboda hakan


Allah Madaukakin Sarki ya ce


Kowanne yana gudana zuwa ga ajali ambatacce


kuma Allah Madaukaki ya ce


Idan ajalinsu yazo ba za’a jinkirta musu Sa’a xaya ba kuma ba zasugabace ta ba


Dalilin fitinar Qabari ko Ni’imominsa daga Alqur’ani


Mene ne dalilin fitinar Qabari ko Ni’imominsa daga Alqur’ani?


Allah ya yi masa Rahama


Kayya!Lallai ne ita kalma ce, shine Mafaxinta ,alhali kuwa bayagaresu akwai wani shamaki har zuwa ranar da za’a tayar da su


kuma Allah Madaukaki ya ce


Kuma Azaba Mummuna ta riski Mutanen Fir'auna Wuta ce wacce aka bujuro musu da ita Safe da Maraice kuma a ranar da za'a tashi Alikiyama (za'a ce) ku Mutanen Fir'auna ku shi ga cikin Mafi tsananin Azaba.


kuma Allah Madaukaki ya ce


Allah yana tabbatar da wadan da sukai Imani da da magana matabbaciya a rayuwar Duniya da kuma a Lahira.


kuma Allah Madaukaki ya ce


Kuma da zaka ga Azzalumai a cikin Magagin Mutuwa kuma Mala'iku suna mika musu Hannayensu suna ku futo da Kawunanku yau ne zaa saka Muku da Azabar Wulakanci


kuma Allah Madaukaki ya ce


Za Mu yi musu azaba sau biyu ,sa’annan mu mayar dasu zuwa ga azaba mai girma


Dalilin fitinar Qabari ko Ni’imominsa daga Alqur’ani


Me ne ne dalilin hakan daga Sunnah?


Me nene dalilin haka daga Sunnah


Daga cikinsu akwai hadisin Anas Allah ya qara masa yarda yace lallai Bawa idan aka sanya shi a cikin kabarinsa abokanansa suka juya baya daga gare shi haqiqa yana jin sautin takalmansu sai Mala’iku guda biyu su zo masa sais u zaunar da shi su ce da shi me ka kasance kana cewa kan wannan mutumin Muhammad tsira da amincin Allah su qara tabbbata a gare shi ?Mumini sai yace :na yi Imani ds cewa


shi Bawan Allah ne kuma Manzon Sa ne Sai su ce da shi kalli mazauninka a wuta Allah ya canja maka da wani mazaunin a Aljannah sai ya gansu gabakixaya –sai Qatada yace an faxa mana sai a buxa masa kabarinsa .Sai ya koma kan hadisin Anas –yace amma munafiki da kafiri saisu ce masu :Me kuka kasance kuna cewa kan wannan mutumin ?sai yace :ban sani ban a kasance ne kawai ina faxar abinda mutane suka kasance suna faxa sais u ce dashi baka sani ba sais u dake shi da abin duka na qarfe duka ! sai yayi ihu ihun da duk wanda yake zagaye da shi banda mutum da Aljan


Hadisin Abdullahi xan Umar Allah ya qara yarda a gare shi daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi yace :idan xayanku yam utu za’a gabato masa da mazauninsa safiya da marece wanda ya kasance daga cikin yan Aljannah za’a nuna masa nay an Aljannah wanda ya kasance nay an wuta za’a gnuna masa na yan wuta ace dashi wannan shine mazauninka har zuwa ranar da Allah zai tashe ka ranar tashin Alqiyama


Da Hadisin kabarurruka guda biyu an ce ana yi musu azaba


Da hadisin Abu Ayub Allah ya yarda da shi yace :Mun fita da Manzon Allah tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi a lokacin rana ta fito sai muka ji wani sauti ,sai Yace :Wata Bayahudiya ce ake azabtar da ita a kabarinta


Da hadisin Asma’ Manzan Allah tsira da amincin Allah su qara tabbata agare shi ya tashi yana haxuba akan fitinar kabari wacce za’a fitini Bawa da ita sai Musulmai suka fara hayaniya sosai sai Aisha Allah ya qara yarda a gare ta tace :tun daga Nan ban qara ganin Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi yayi Sallah ba face ya nemi tsari da azabar kabari ,a hadisin kusufi Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya na neman tsari daga azabar kabari duk waxannan hadisan hadisai ne masu inganci sun kai kusan hadisai sittin dagatabbatattun hanyoyi daga jama’a ta Sahabbai


Dalilin Tashi daga kabari



Posts na kwanan nan

FALALAR AZUMIN KWANA ...

FALALAR AZUMIN KWANA SHIDA SHAWAL

TAKAITACCEN BAYANI MA ...

TAKAITACCEN BAYANI MAI ANFANI GA SABON SHIGA MUSULUNC

ZIKIRAI WADANDA AKE Y ...

ZIKIRAI WADANDA AKE YIN SU DA SAFE DA KUMA YAMMA

BIDI’AR ‘YAN SHI’A A ...

BIDI’AR ‘YAN SHI’A A RANAR ASHURA