
SIFFAR SALLAR ANNABI – TSIRA DA AMINCIJ ALLAH
SU TABBATA AGARE SHI -
Na shehin Malami
AbdulAziz ɗan Abdullah ɗan Baaz
Da sunan Allah Mai Rahama Mai jin ƙai
Dukkanin godiya ta tabbata ga Allah Shi kaɗai, tsira
da aminci su tabbata ga bawanSa kuma manzonSa
Annabimmu Muhammad da alayansa da sahabbansa.
Bayan haka:
Waɗannan wasu taƙaitattun bayanai ne a cikin siffar
sallar Annabi, ina son in gabatar da su ga dukkanin
musulmi da musulma, domin duk wanda ya gani yayi
ƙoƙarin koyi da shi a cikin hakan, saboda faɗinsa: (Ku yi
sallah kamar yadda kuka ga ina yin sallah) 1 Bukhari ne
ya rawaito shi. Ga bayanin hakan ga mai karatu:
1 Bukhari, babin kiran sallah (605), Darimi, al-Sallah: (1253).
3
Kyautata alwala
1. Zai kyautata alwala, shi ne yayi alwala kamar
yadda Allah Ya umarce shi, don yin aiki da faɗinSa -
tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -:
{Ya ku waɗanda suka yi imani, idan kun tashi za ku
yi sallah, to, ku wanke fuskokinku da hannayenku zuwa
gwiwoyi, kuma ku shafi kawunanku, kuma (ku wanke)
ƙafafunku zuwa idon sawu}2 Zuwa ƙarshen ayar.
Da faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi _ (Ba’a karɓar sallah ba tare da tsarki ba)3 .
Fuskantar Alƙibla
2- Wanda zaiyi sallah zai fuskanci alƙibla, ita ce
kuma Ka’abah, duk ta inda yake da dukkanin jikinsa
yana nufin yin sallar da zaiyita da zuciyarsa ta farilla ko
nafila, ba zai furta niyya da harshensa ba, domin ba a
shar’anta furta niyya ba, yin hakan bidi’a ne, saboda
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -
bai furta niyya ba haka nan sahabbansa - Allah Ya
2 Suratul Ma'idah, aya ta: 6.
3 Muslim, Tsarki (224), Tirmizi, Tsarki (1), Ibnu Majah, Tsarki da sunnoninsa (272),
Ahmad (2/73).
yarda da su -, sai ya sanya suturar da zai yi sallah ga
reta idan ya kasance liman ne ko shi kaɗai yake sallah.
Fuskantar alƙibla sharaɗi ne a sallah, saidai a wasu
mas’alolin da aka togance kuma sanannu da a ka yi
bayaninsu a littattafan malamai.
Kabbarar harama, da ɗaga hannaye biyu a lokacin
kabbarar, da kuma ɗora hannayen biyu akan ƙirji.
3. Yana yin kabbarar harama yana cewa: Allahu
Akbar, yana mai kallon inda zai yi sujjada da
idanuwansa zuwa bigiren sujjadarsa.
4. Yana daga hannuwansa daura da kafaɗunsa ko
daidai da kunnuwansa.
5. Ya sanya hannuwansa a ƙirjinsa, na dama akan
tafin na hagu, da wuyan hannu da damtse, saboda
tabbatuwar hakan daga Annabi - tsira da amincin Allah
su tabbata a gare shi -.
Addu'ar buɗe Salla
6. An sunnanta, (mai sallah) ya karanta Addu’ar
buɗe sallah, ita ce: Ya Allah Ka nisantar da tsakanina da
kurakuraina kamar yadda Ka nisantar da gabas da
yamma, Ya Ubangiji Ka tsaftace ni daga kurakuraina
kamar yadda ake tsaftace farin tufa daga datti, ya Allah
5
Ka wankeni daga kurakuraina da ruwa da ƙanƙara da
sanyi.
Idan (mai sallah) ya ga dama maimakon wannan sai
ya karanta:
Tsarki ya tabbata a gareKa ya Allah haɗi da gode
maKa,
(4). 4
kuma sunanKa ya girmama kuma ƙarfinKa ya
ɗaukaka, kuma babu abin bautawa da gaskiya sai Kai
Idan ya yi (wata addu’ar) da ba waɗannan ba cikin
addu’oin buɗe sallah tabbatattu daga Annabi to babu
wani laifi, abinda yafi yayi wannan wani lokacin kuma
yayi waccan wani lokacin daban, domin hakan yafi
kaiwa ƙoli wurin biyayya, sannan sai ya ce:
Ina neman tsari daga sheɗan jefaffe.
Da sunan Allah Mai rahama Mai jin ƙai, sai ya
karanta Fatiha, saboda faɗinSa: (Babu sallah ga wanda
bai karanta Fatihatul Kitab ba)5 . Sai ya ce: Amin, bayan
(ya karanta ta) a bayyane a cikin sallar da ake karatu a
bayya ne, kuma a sirrance idan sallar a ɓoye ake yinta,
sannan ya karanta abinda ya sawwaƙa na AlKur’ani.
4 Al-Bukhari, Kiran sallah (711), Muslim Masallatai da wuraran sallah (598), Nasa’i
buɗe sallah (895), Abu Dawud Sallah (781), Ibnu Majah, Iƙamatus Salah Wassunnantu
fiha (805), Ahmad (2/231), al-Darimi (Sallah1244).
5 Bukhari Kiran sallah (723), Muslim (394), Tirmizi Sallah (247), Nasa’i Buɗe sallah
(911), Abu Dawud Sallah (822), Ibnu Majah, Iƙamatus Salah Wassunnantu fiha (837),
Ahmad (5/316), al-Darimi (1242).
6
Abinda ya fi ya karanta bayan Fatiha a sallar Azahar
da La’asar da Issha cikin tsakatsakin Mufassal, a Asuba
cikin dogayan Mufassal, a Magariba kuma wani lokacin
cikin dogayan Mufassal, wani lokacin kuma cikin
gajerun Mufassal, don yin aiki da hadisan da suka zo da
hakan .
Ruku’i da tasowa daga ruku’in da kuma
abinda ya ƙunsa
7. Zai yi ruku’i yana mai yin kabbara kuma yana
ɗaga hannayansa zuwa daidai kafaɗunsa ko
kunnuwansa, yana mai sanya kansa daidai da gadon
bayansa, yana ɗora hannayansa akan gwiwowinsa,
yana mai wara yatsunsa, ya kuma nutsu a ruku’insa
yana mai cewa:
Tsarki ya tabbata ga Ubangijina Mai girma.
Abinda yafi shine ya maimaita faɗin sau uku ko
sama da haka, kuma an so ya ce tare da hakan: (Tsarki
ya tabbata a gareKa ya Allah Ubangiji tare da gode
maKa, ya Ubangiji Ka gafarta min6 .
8. Yana ɗago kansa daga ruku’i yana mai ɗaga
hannayansa zuwa kafaɗunsa ko daura da kunnuwansa,
6 Bukhari Tafsirul Kur’an (4683), Muslim Sallah (484), Nasa’i Taɗbik (1122), Abu
Dawud (877), Ibnu Majah Iƙamatus Salah Wassunnatu fiha (889).
7
yana mai cewa: (Allah Ya ji mai gode masa (7) -7 Idan ya
kasance liman ko shi kaɗi ne sai ya ce a lokacin da yake
tasowa: (Rabbana Walakal Hamdu, Hamdan Kasiran
Ɗayyiban Mubarakan Fihi, Mil’as Samawati, Wa Mil
al’ard, Wa Mil’a Ma Baina huma, Wa Mil’a Ma Shi’ata
Min Shai’in Ba’adu) 8 . Amma idan ya kasance mamu ne
to a lokacin ɗagowa daga ruku'u sai ya ce:
Rabbana walakal Hamd”. Zuwa ƙarshen abinda ya
gabata, idan kuma kowannan su ya ƙara, wato liman
da mamu da mai sallah shi kaɗai" (Ahlus Thana’i wal
majd, a haƙƙun ma ƙalal abdu, wakulluna laka abdu.
Allahumma La mani’a lima aaɗaita wala mu’uɗiya lima
mana’a ta, wala yanfa’u zal jadd mikal jadd (9)"9 Yin
hakan yana da kyau, saboda tabbatuwar hakan daga
gare shi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -,
kuma an so kowannen su ya ɗora hannuwansa a
ƙirjinsa kamar yadda yayi a tsaye kafin yayi ruku’i,
saboda tabbatuwar abinda yake nuni akan hakan daga
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -
cikin Hadisin Wa’il ɗan Hujri da Sahl ɗan Sa’ad - Allah
Ya yarda da su -.
7 Bukhari, Azan (657), Muslim al-Sallah (411), Tirmizi al-Sallah (361), Nasa’i Imamah
(832), Abu Dawud Sallah (601), Ibnu Majah Iƙamatus Salah Wassunnatu fiha (1238),
Malik Annida’u Lissalah (306), Darimi al-Sallah (1256).
8 Muslim, Salatul Musafirin wa ƙasriha (771), Tirmizi al-Da’awat (3423), Abu Dawud
al-Sallah (760), Ahmad (1/103).
9 Muslim Sallah (477), Nasa’i Taɗbiƙ (1068), Abu Dawud Sallah (847), Ahmad (3/87),
Darimi Sallah (1313).
8
Sujjada da ɗagowa daga gareta da abinda ya
ƙunshi hakan
9. Yana yin sujjada tare da kabbara, yana sanya
gwiwowinsa kafin hannayansa, idan haka ya sawwaƙa
a gare shi, idan kuma yayi masa wahala sai ya fara
gabatar da hannayansa kafin gwiwowinsa, yana mai
fuskantar da yatsun kafafuwansa da hannayansa zuwa
alƙibla, yana mai haɗe yatsun hannuwansa yana miƙar
da su, kuma sujjudar ta kasance akan gaɓɓai bakwai:
Fuska tare da hanci, da hannuwa da gwiwowi, da cikin
yatsun ƙafafuwa, kuma ya ce:
Subhana Rabbiyal Aalah. ) ( �ﻋﻷا �ر نﺎﺤ�ﺳ)
An sunnanta ya faɗi hakan sau uku ko sama da haka
, kuma an so ya faɗa tare da hakan: (Subhana
Kallahumma wabi hamdiKa, Allahumma ghfirli 10 . Ya
yawaita addu’a saboda faɗin Annabi - tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi -: (Amma a ruku’i to ku
girmama Ubangiji a cikinsa, Amma a Sujjada to ku yi
ƙoƙarin addu’a domin ya cancanci a amsa muku) 11 Ya
kuma roƙi Ubangijinsa na alhairan duniya da lahira,
hakan a sallar farilla ne ko sallar nafila, ya buɗa
damatsansa daga ɓarin jikinsa, cikinsa kuma daga
10 Bukhari, Azan (761), Muslim, Sallah (484), Nasa’i Taɗbiƙ (1122), Abu Dawud,
Sallah (877), Ibnu Majah Iƙamatus Salah Was Sunanu fiha (889), Ahmad (6/43).
11 Muslim (479), Nasa’i Taɗbiƙ (1120), Abu Dawud Sallah (876), Ahmad (1/219),
Darimi Assalah (1325).
9
cinyoyinsa, ya kuma raba cinyoyinsa da ƙwaurinsa, ya
ɗaga hannayansa daga barin ƙasa, saboda faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare - shi: (Ku
daidaita a sujjada, kada ɗayanku ya shinfiɗa hannuwa
irin shinfiɗawar kare) 12
Zama tsakanin sujjadu biyu da kaifiyyarsa
10. Yana ɗago kansa tare da kabbara, ya kuma
shinfiɗa diddigensa na hagu sai ya zauna a kansa, ya
kuma kafe ƙafarsa ta dama, ya ɗora hannayansa akan
cinyoyinsa da gwiwowinsa sai ya ce: (Ya Allah Ka
gafarta mini Ka ji ƙaina Ka shiryar da ni Ka azurtani Ka
tsare ni Ka agaza mini 13 Ya kuma natsu a wannan
zaman.
11. Yana yin sujjada ta biyu tare da kabbara, ya
kuma yi hakan kamar yadda yayi a sujjada ta farko.
12- Yana ɗago kansa tare da kabbara, sai ya zauna
zama ƙanƙani kamar yadda ya zauna tsakanin sujjada
biyu, ana kiransa da zaman hutu, wannan zaman
mustahabbi ne, idan ya bari babu wani laifi akansa,
babu wani zikiri ko wata addu’a a cikinsa, sannan ya
yunƙura ya tashi tsaye zuwa raka’a ta biyu yana mai
dogara akan gwiwowinsa idan hakan ya yiwu a gare
12 Bukhari Azan (788), Muslim Salah (493), Ahmad (3/192).
13 Tirmizi sallah (284), Abu Dawud Sallah (850), Ibnu Majah Iƙamatus Salah
Wassunnatu fiha (898).
10
shi, idan kuma yayi masa wahala ya dogara akan ƙasa,
sannan ya karanta Fatiha da abinda ya sawwaƙa a gare
shi na AlKur’ani bayan Fatihar, sannan ya yi kamar
yadda ya yi a raka’a ta farko.
Zama domin yin Tahiya a zama na biyu da
kaifiyyarsa
13. Idan sallar ta kasance mai raka’a biyu ce kamar
sallar Asuba da Juma’a da Idi biyu, to sai ya zauna
bayan ya ɗago kansa daga sujjada ta biyu yana mai
kafa ƙafarsa ta dama yana kuma shinfiɗa ƙafarsa ta
hagu, yana ɗora hannun sa na dama akan cinyarsa ta
dama, yana naɗe yatsunsu baki ɗaya sai manuniya, sai
ya yi nuni da ita akan Tauhidi, idan ya naɗe ƙaramin
yatsansa da wanda yake biye da shi na dama ya kuma
lanƙwasa babban yatsa da na tsakiya ya yi nuni da
manuniya (kaɗai) hakan ma ya yi kyau, saboda
tabbatuwar duka siffofin biyu daga Manzon Allah -
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, abinda ya
fi shi ne ya yi wannan a wani lokaci kuma ya yi wancan,
sai ya dora hannun sa na hagu akan cinyarsa ta hagu
da gwiwarsa, sannan sai ya yi Tahiya a wannan zaman,
ita ce kuma: (Dukkanin gaisuwa kyawawa sun tabbata
ga Allah, da salloli da kyawawan (maganganu), aminci
ya tabbata a gareka ya kai wannan Annabi da rahamar
Allah da albarkarSa, aminci ya tabbata a garemu da
kuma bayin Allah salihai, ina shaidawa babu abin
11
bautawa da cancanta sai Allah kuma ina shaidawa
(Annabi) Muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa ne.
Sannan sai ya ce:
Ya Allah Ka yi salati ga (Annabi) Muhammad da
iyalan Muhammad kamar yadda Ka yi salati ga (annabi)
Ibrahim da iyalan Ibrahim, lalle Kai abin godewa ne
kuma mai girma. Ya Allah ka yi albarka ga (annabi)
Muhammad da iyalan Muhammad kamar yadda ka yi
albarka ga (annabi) Ibrahim da iyalan Ibrahim lalle Kai
abin godewa ne kuma Mai girma. 14 Kuma ya nemi
tsarin Allah akan abubuwa huɗu, sai ya ce: Ya Ubangiji
ina neman tsarinKa daga azabar Jahannama da azabar
ƙabari da fitinar rayuwa da ta mutuwa da fitinar
Masihul Dajjal (Jujal) 15 Sannan ya yi addu’a da abinda
ya ga dama na alhairan duniya da lahira, idan kuma ya
yi addu’a ga iyayansa ko wasu daga cikin musulmai
duka babu laifi, daidai ne hakan a sallar farilla ne ko
nafila, saboda gamewar faɗin Annabi - tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi - a cikin Hadisin ɗan Mas’ud
a lokacin daya koyar da shi Tahiya, sannan ya zaɓi
addu’ar da tafi ƙayatar da shi sai yayi addu'a da ita. A
wani lafazin kuma, sannan ya zaɓi abinda yake so ya
14 ( )Bukhari, Kiran sallah (797), Muslim Salah (402), Tirmizi Nikah (1105), Nasa’i
Sahwu (1298), Abu Dawud Sallah (968), Ibnu Majah, Iƙamatus Salah Wassunnantu fiha
(889), Ahmad (1/428), Darimi (1340).
15Bukhari Jana’iza (1311), Muslim Masajid wa mawadi’us Salah (588), Tirmizi
Da’awar (3604), Nasa’i Isti’aza (5513), Abu Dawud Salah (983), Ibnu Majah Iƙamatus
Salah Wassunnatu fiha (909), Ahmad (2/454), Darimi Salah (1344).
12
roƙa, wannan ya game duk abinda bawa yake so na
duniya da lahira, sannan yayi sallama a damar sa da
kuma hagunsa, ya ce: Assalamu alaikum wa
rahmatullah.
Zama domin yin Tahiya a sallah mai raka’a biyu ko
huɗu da kaifiyyarsa
Idan sallar ta kasance mai raka’a uku ce, kamar
Magariba ko mai raka’a huɗu ce kamar Azahar da
La’asar da Issha, sai ya yi Tahiyar da aka ambata a
baya, tare da yin salati ga Annabi - tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi -, sannan sai ya yunƙura ya
tashi tsaye yana mai dogara a kan gwiwowinsa yana
ɗaga hannayansa daidai kafaɗunsa ko daidai
kunnuwansa yana cewa: Allahu Akbar, yana mai ɗora
hannayansa akan ƙirjinsa kamar yadda ya gabata, sai
ya karanta Fatiha kaɗai, idan ya karanta a raka’a ta uku
da ta huɗu a Azahar ƙari akan Fatihar a wasu lokutan
to babu laifi, saboda tabbatuwar abinda yake nuni
akan hakan daga annabi - tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi - cikin Hadisin Abu Sa’idu, sannan sai
ya yi Tahiya bayan raka’a ta uku a magariba, da kuma
bayan raka’a ta huɗu a Azahar da La’asar da isha
kamar yadda ya gabata a hakan a sallah mai raka’a
biyu, sannan ya yi sallama a damansa da kuma
hagunsa, ya kuma nemi gafarar Allah sau uku, sannan
ya ce: (Ya Allah Kai ne aminci, daga gareKa aminci yake
13
alherinKa ya yawaita ya Ma’abocin girma da karamci) 16
Kafin ya juya ya fuskanci mutane idan ya kasance liman
ne, sannan ya ce: (Babu abin bautawa da gaskiya sai
Allah Shi kaɗai Yake, ba Shi da abokin tarayya, kuma
Shi Mai iko ne akan dukkan komai. Ya Allah babu mai
hana abinda Ka bayar kuma babu mai bayar da abinda
Ka hana, wadatar mai wadata bata anfani a wurinKa,
babu ƙarfi kuma babu wata dabara sai da taimakon
Allah. Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, ba ma
bautawa kowa sai Shi, ni’ima ta sa ce da falala, da yabo
mai kyau, babu abin bautawa da gaskiya sai Shi, muna
masu tsarkake addini gare Shi, ko da kafirai sun ƙi 17 , Sai
ya yi tasbihi: Subhanallah, talatin da uku, ya gode maSa
kwatankwacin
hakan,
yayi
maSa
kabbara
kwatankwacin hakan a cikon na ɗarin sai yace: Babu
abin bautawa da gaskiya sai Allah ba Shi da bokin
tarayya, mulki naSa ne, kuma godiya taSa ce, kuma Shi
Mai iko ne akan dukkan komai.
Kuma ya karanta Ayatul Kursiyy, da Kulhuwa da
Falaƙi da Nas a bayan kowacce sallah, kuma an so a
maimaita waɗannan surorin uku, sau uku bayan sallar
Asuba da Magariba, saboda Hadisan da suka zo akan
16Muslim Masallatai da wuraran sallah(591), Tirmizi Sallah(300), Abu Dawud (1512),
Ibnu Majah Iƙamatus Salah Wassunnatu fiha (928), Ahmad (5/280), Darimi Sallah
(1348).
17 Bukhari, Kiran Sallah (808), Muslim, Msallatai da wuraran sallah(593), Nasa’i
Rafkannuwa (1341), Abu Dawud Sallah (1505), Ahmad (4/250), Darimi Sallah (1349).
14
haka daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi -.
Dukkanin waɗannan zikiran sunna ne ba wajibi ba
ne.
Kuma an shar’anta ga kowanne musulmi da
musulma yin sallah (nafila) kafin sallar Azahar raka’a
huɗu bayanta kuma raka’a biyu, da raka'a biyu bayan
Magariba, da raka'a biyu bayan sallar Issha, da raka'a
biyu kafin sallar Asuba, idan aka haɗa ya kama raka’a
goma sha biyu. Waɗannan raka’o'in ana kiransu da
Rawatib, domin Annabi - tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi - ya kasance yana kiyaye su a halin
zaman gida. Amma a halin tafiya ya kasance ba ya
yinsu saidai na kafin Asuba da Wuturi, domin tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance yana
kiyaye su a halin zaman gida da kuma tafiya.
farilla18
Abinda yafi a sallaci waɗannan nafilfilin da Wuturi a
gida, idan yayi su a masallaci babu wani laifi, saboda
faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi -: “Mafificin sallar mutum a gidansa saidai (sallar)
Kiyaye waɗannan raka’oin yana cikin sabubban
shiga aljanna, saboda faɗin Annabi - tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi -: (Wanda ya yi sallah raka’a
18Bukhari, Ladubba (5762), Muslim, Salatul musafirin wa ƙasruha (781), Tirmizi
Sallah (450), Nasa’i tsayuwar dare da nafilar rana (1599), Abu Dawud Sallah (1447),
Ahmad (5/186), Malik, Kiran Sallah (293), Darimi Sallah (1366).
15
goma sha biyu a yini da dare domin neman lada, Allah
Zai gina masa gida a aljanna)19 . Muslim ne ya ruwaito
shi a Sahihinsa, idan ya yi raka’a huɗu kafin La’asar, da
raka’a biyu kafin Magariba, da raka’a biyu kafin Issha
to ya yi kyau, domin abinda yake nuni akan hakan ya
inganta daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi -.
Allah Shi ne Majiɓincin datarwa. Tsira da amincin
Allah su tabbata ga Annabimmu Muhammad ɗan
Abdullah da alayansa da sahabbansa da mabiyansa da
kyautatawa har zuwa ranar sakamako.
19Muslim Salatul musafirin wa ƙasruha (728), Tirmizi Sallah (415), Nasa’i Kiyamul
Lail wa Taɗawwu’un Nahar (1801), Abu Dawud Sallah (1250), Ibnu Majah, Iƙamatus
Salah Wassunnatu fiha (1141), Ahmad (6/327).
16
Teburin bayani
Kyautata alwala ............................................................... 4
Fuskantar Alƙibla ............................................................. 4
Kabbarar harama, da ɗaga hannaye biyu a lokacin
kabbarar, da kuma ɗora hannayen biyu akan ƙirji. ........ 5
Addu'ar buɗe Salla .......................................................... 5
Ruku’i da tasowa daga ruku’in da kuma abinda ya
ƙunsa ............................................................................... 7
Sujjada da ɗagowa daga gareta da abinda ya ƙunshi
hakan .............................................................................. 9
Zama tsakanin sujjadu biyu da kaifiyyarsa.................... 10
Zama domin yin Tahiya a zama na biyu da kaifiyyarsa . 11
Zama domin yin Tahiya a sallah mai raka’a biyu ko
huɗu da kaifiyyarsa ....................................................... 13