Labarai




Kuma abinda ya same kun a wata masifa,to,game da abinda hannayenku suka sana’anta ne,kuma( Allah )Yan a yafewar (wadansu laifuffuka )masu yawa.


kuma Allah Madaukaki ya ce


Kuma ba Mu zalunce su ba,sai dai sun kasance sune Azzalimai


kuma Allah Madaukaki ya ce


Lallai ne Allah ba Ya zaluntar mutane da kome,amma mutanen ne ke zaluntar kansu


Shin bayi suna da mashi’a da qudura akan aiyukansu da aka jingina su a gare su


Shin bayi suna da mashi’a da qadura akan aiyukansu da aks jingina su gare su?


Na’am bayi suna da iko kan aiyukansu,sanan suna mashi’a da dama,a haqiqa aiyukansu an jingina su ne gare su, an yi zaton su zamo masu daukar nauyin, da su za su samu sakamako ko kuma ayi musu uquba,Allah bai dora musu ba sai don Ya san za su iya xauka, wannan duka ya zo musu a Littafi da kuma Sunnah an siffanta su da shi sai duk da haka ba za su iya qaddara komai ba face abinda Allah


Ya qaddara mu su, ba za su so wani abu ba face abinda Allah Ya so, ba za su aikata ba face Ya sanya su masu yin aikin kamar yadda ya gabata cikin nassoshin Mashi’a da nufi da halitta,


Kamar yadda ba za su sami kawukansu ba,ba za su sami aiyukansu ba,qudurarsu da mashi’arsu da nufinsu da aiyukansu dukkaninsu masu bin nufinsa ne Allah Maxaukakin Sarki da mashi’arsa da aiyukansa,ba mashi’arsu da nufinsu da qudurarsu da aiyukansu sune ido ga mashi’ar Allah da nufinSa ds qudurarSa da aiyukanSa.Kamar yadda basu kasance shi ba, tsarki ya tabbata ga Allah Maxaukakin Sarki ya tsarkaka daga haka ,aiyukansu an halitta su dominsu, sun dace da su, an jingina su gare su haqiqa, Allah shine Mai aiki na haqiqa, bawa kuma shine mai aikatawa na haqiqa, bawa shine abin shiryarwa, da wannan ne ake jingina dukkanin aiyukan ga wanda ya tsayar da su ,Allah Maxaukakin Sarki Ya ce:


Wanda Allah Ya shiryar,to,shi ne Mai shiryuwa


Jingina shiriya zuwa ga Allah ,an jingina shiryuwar zuwa ga bawa a haqiqa, kamar yadda Mai shiryarwa shi ne idon shiryayye, hakanan kuma shiriya ba itace idon shiryuwa, haka Allah Ya ke batar da da wanda Ya so a haqiqa da wannan bawa sai ya zama batacce haqiqatan,haka Allah Ya ke juya al’amuran bayinSa, wanda Ya jingina aiki da aikatawa zuwa ga bawa ya kafurta,wanda ya jingina zuwa ga Allah ya kafurta, wanda Ya jingina aiki zuwa mahalicci da zuwa ga abin halitta gabaxayansu a haqiqa wannan shine mumini.


Me ne ne amsar wanda ya ce shin ba ya yuwuwa cikin qudurar Allah Ya sanya dukkanin bayinsa su zamo muminai masu biyayyya kuma shiryayyu


Me ne ne amsar wanda ya ce shin ba ya yuwuwa cikin qudurar Allah Ya sanya dukkanin bayinsa su zamo muminai masu biyayyya kuma shiryayyu


Eh haqiqa Allah mai iko ne akan haka kamar yadda Ya ce:


Da Ubangijinka Ya so da dukkannin waxanda ke doron qasa sun yi Imani


kuma Allah Madaukaki ya ce


Sai dai hakan da ya aikata musu shine ya qunshi hikimarSa ya kuma wajabta Rububiyyarsa da


Uluhiyyarsa da SunayenSa da SiffofinSa ,to faxar mai Magana :saboda me zai zamo a cikin bayinSa akwai mai biyayya da mai savo ?kamar faxin mai cewa ne me ya sa bai zamo cikin sunayenSa ba mai Cutarwa ,Mai amfanarwa,Mai kyauta,Mai hanawa,Mai qasqantarwa,Mai xaukakawa,Mai ni’imtarwa,Mai kamawa da wasun haka ?da wannan sai mu ce aiyukanSa Maxaukakin Sarki sun qunshi sunayenSa ,kuma ragowar ne na sunayenSa ,har ma kan UluhiyyarSa da RububiyyarSa:


Tsarki ya tabbata ga Allah Ubangijin Al’arshi daga abinda suke siffantawa.Ba’a tambayarSaga abinda Yake aikatawa ,alhalinalhalin kuwa suna tambayar su.


Matsayin Imani da qaddara a cikin addini


Yankin Imani


Me ne ne matsayin Imani da qaddara a Addini?


Imani da qaddara tsari ne na Tauhidi,kamar yadda da sababan da suke sadarwa zuwa ga alherinsa ta kuma nesatar daga sharrinsa sune tsari na shari’a,babu wanda zai bi tsarin addini kuma sai wanda ya yi Imani da qaddara ya kuma bi shari’a,kamar yadda Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi Ya ce kan Imani da qaddara sa’annan Ya ce da waxanda suka ce da shi shin ba zamu dogara


ba akan Littafinmu ba mu bar aiki,Sai ya ce :’’ku yi aiki kowa an sauqaqe masa abinda aka halittashi dominsa ‘’


Wanda ya kore qaddara yana riya korewar ga shari’a, haqiqa Allah Maxaukakin Sarki Ya aiyukansa da qudurarsa,Ya sanya bawaya zamo mai tsayawa ne kan aiyukansa shine mahaliccinsu, ya tabbata cewa Allah Maxaukakin Sarki shi ne mahalicci ya kuma tabbatar cewa dukkanin halittu Allah ne ya halicce suWanda ya tabbata mai buqatuwa ne dashi kan shari’a,mai yaqarsa ne da shi,ya korewa bawa qudurarsa da zavinsa wanda Allah ya bashi ya kuma dora masa gwargwado sai ya riya Allah Ya dora bayinsa abinda ba zasu iya xauka ba kamar dora makanta wannan ya nasabta Allah da zalunci,shugaban shi shine shaidan Allah Ya la’ance ni a loqacin da Ya ke cewa:


Ya ce ‘’To ina rantsuwa da halakarwar da ka yi mini ,lallai ne,ina zaune musu tafarkinKa madaidaici


Amma mumini na gaskiya ,zai yi Imani da qaddara alkhairinta da kuma sharrinta,kuma Allah shine mahaliccin dukkanin waxannan,suna miqa wuya ga shari’a umarninta da haninta suna hukunta kawunnansu gare shi a fili da boye ,kuma cewa shiriya da vata a hannun Allah suke Yana shiryar da wanda Ya so da falalarSa,Yana kuma vatar da wanda Ya so da adalcinsa ,Shine mafi sanin wararen falalarSa da adalcinSa


Lallai ne Ubangijinka Shi ne Mafi saniga wanda ya ke vacewa daga hanyar Sa kuma Shine Mafi sani ga masu shiryuwa


A cikin haka akwai hikima matuqa da hujja kwakkwara,kuma cewa sakamako da uquba matakai ne na shari’a a aikatawa da kuma bari ba kan qaddara ba,suna xaukaka kawunan da qaddara a yayin masifu ;idan kuma suka tsinci kawunansu cikin mai kyau sai su gane gaskiya ,Allah Yana cewa akansu suna cewa


Godiya ta tabbata ga Allah da ya shiryar da mu ga wannan ,ba mu kasance muna iya shiryuwa ba ,ba domin Allah Ya shiryar da mu ba


Kan abinda suka ce,fajiri kuma ya ce:


An ba ni shi ne a kan wani ilimi wanda yake gare ni ne kawai


Idan suka aikata mummuna sai su ce kamar yadda iyaye guda biyu suka ce:


Ubangijinmu mun zalunci kawunanmu ,idan har baka yafe man aba ka yi mana rahama za mu zamo daga cikin tavavvu


Ba su fada ba kamar fadin shaidan jefaffe:


Ubangiji ina rantsuwa da hallakawar da kayi min


Idan wata musiba ta same su:


Lallai Mu daga Allah Muke kuma zuwa gare shi zamu koma


Ba za su ce kamar yadda waxanda suka kafirce suka ce ba:


Suka wa yan uwansu idan,sun yi tafiya a cikin qasa ko kuwa suka kasance a wurin yaqi :Da sun kasance a wurinmu da bas u mutu ba ‘’(Wannan kuwa )domin Allah Ya sanya waccan maganar ta zama nadama a cikin zukatansu. Allah shine Yake rayarwa kuma shine Yake mataewa.Kuma Allah ga abinda kuke aikatawa,Mai gani ne.


Nawa ne rabe – raben Imani?


Allah Madaukakin Sarki ya ce:


Bai zama Addini ba domin kun juyar da fuskokinku wajen gabas da yamma,kuma amma addini shi ne ga wanda ya yi Imani da Allah da ranar lahira da mala’iku da Littattafan sama da Annabawa,kuma ya bayar da dukiya,akan yana sonta ga mai zumunta da marayu da matalauta da dan hanya da masu roqo,kuma a cikin fansar wuya,kuma ya tsayar da sallah,kuma ya bayar da zakka,da masu cika alqawari idan sun qulla alqawarin da masu haquri cikin tsanani da cuta da loqacin yaqi.Wadannan sune suka yi gaskiya ,kuma wadannan sune masu taqawa.


Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi Ya ce :’’imani sittin ne da kadan ‘’a wata ruwayar ‘’yanki saba’in ne da kadan na qololuwarta shine fadin La’ilaha illallah na qarshenta shine kawar da abinda zai cutar daga kan hanya,kunya wani yanki ce na imani’’


Fassarar malamai kan rabe—raben Imani


Da me malamai suka fassara rabe –raben Imani?


Qoqari sun kuma fa’idantu ,sai ba sharaxi ba ne saninta a cikin Imani,sai dai Imani yana isa da ita a dunqule,kuma ya zamo bata fita daga Alqur’ani da kuma Sunnah ,ya wajaba akan bawa ya yi aiki da umarninta ya kuma guji haninta,ya kuma gaasgata labaranta,rabe –raben Imani ya cika,waxanda suka qididdige su sun tabbatar da gaskiyarsu cewa duka suna daga cikin Imani,sai dai yankewa wanda shine manufar Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi kan wannan yana buqatar tsayawa


Rufewa kan abinda malamai suka qididdige daga rabe – raben Imani


Ka abaci rufewar abinda suka qididige?


Hafiz ya taqaita abinda Ibn Hibban ya rawaito a cikin’’Al Fath’’yane cewa :Waxannan rabe –raben sun haxa ne daga aiyukan zuciya da na harshe da na jiki,


Amma aiyukan zuciya :sune iitiqadi da niyyoyi su xabi’u ne guda ashirin da huxu ,Imani da Allah ya shiga ciki,Imani da ZatinSa da siffofinSa,da tauhidinSa ,cewa babu wani abu kwatankwacinSa shi Mai ji ne kuma Mai gani ne da I’itiqadin rashin samuwar wani bayanshi,da Imani da Mala’ikuda LittatafanSada ManzanninSa da qaddara alkhairinta da kuma sharrinta ,da Imani da ranar lahira ,mas’alal kabari ma zata shiga ciki da tashi bayan mutuwa ,da hisabi da mizani ,da siraxi da Aljannah da Wuta ,da soyayyar Allah ,da soyayya da qiyayya saboda Allah,da soyayyar Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi da qudurcewa wajen girmama shi ,sannan salatin Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya shiga ,da bin Sunnar shi ,da Ikhlasi ,barin riya ya shiga ciki ,da munafurci ,da tuba,da tsoro ,da fata ,da godiya,da cika alqawari,da haquri,da yarda da qaddara ,da tawakkali,da rahama,da qanqan da kai,ya shiga cikinsa girmama babba,da rahama ga qarami,da barin girman kai da mamaki ,da barin hassada ,da barin kyashi,da barin fushi


Aiyukan harshe :ya qunshi Dabi’u guda bakwai :yin lfazi da tauhidi,da tilawar Alqur’ani,da neman ilimi da koyar da shi ,da Addu’a ,da zikiri,Istigfari zai shiga


Ya gabata gare ka cewa Imani shi ne magana da kuma aiki ,faxin zuciya da kuma harshe ,da kuma aikin zuciya da kuma harshe da gavovi,shine gasgatawa ,fadin harshe kuma ,shine zane da Kalmar musulunci,aikin zuciya kuma shine niyya da ikhlasi ,aikin gabbai kuma shine ,miqa wuya da dukkanin biyayya ,idan gabakixayan wadan nan abubuwa hudun suka gushe fadin zuciya da aikinta fadin harshe da aikinshi da aikin gavvai Imani ya gushe baki daya,idan gasgatawar zuciya ya gushe sauran ba za su yi amfani ba ,domin cewa gasgatawar zuciya wani abu ne daga sallamawarta ta kuma kasance mai amfani wannan kamar wanda ya qaryata sunayen Allah ne da siffofinSa ko da kowanne abu da Allah ya aiko da shi ya saukar da LittattafanSa da shi ,idan aikin zuciya ya gushe tare da I’itiqadi na gaskiya.


Dalilin kyautatawa daga Littafi da Sunnah


Kyautatawa cikin ibada


Me ne ne dalilin kyautatawa daga Littafi da Sunnah?


Akwai dalilai ma su yawa daga ciki akwai fadin Allah Madaukakin Sarki:


Ku kyautata lallai Allah yana son masu kyautatawa


Lallai Allah Yana tare da wadanda suka yi taqawa da wadan da su ke su masu kyautatawa ne.


Kuma wanda ya mika fuskarsa zuwa ga Allah, alhali kuma yana mai kyautatawa to lalle ya yi riko ga igiya amintacciya


Wadanda suka kyautata suna da Kyautaye da kuma Kari


Shin kyautatawa na da wani sakamako ?(A’aha )face kyautatawa


Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce :’’haqiqa Allah Ya rubuta kyautatawa akan dukkan komai ‘’a wata kuma fadar yana cewa :Ni’ima ta tabbata ga bawa ace yam utu yana mai kyautata Ibadar Allah


Me ne ne kyautatawa a cikin ibada?


Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya fassara shi a cikin hadisin Jibril a loqacin da ya ke cewa ‘’ba ni labari akan kyautatawa ?sai ya ce :Ka bautawa Allah kamar kana ganinSa ,idan kai ka kasance baka ganinSa ,to ,shi Yana ganinka ‘’Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya bayyana cewa kyautatawa sau biyu ta hanyoyi daban –daban ,na qololuwar su:shi ne bautawa Allah kamar kana ganinSa,wannan shine abin dubawar ,shine bawa zai bautawa Allah gwargwadon yadda yake ganin Allah a zuciyarsa ,shi ne zuciya ta zamo tana haskaka da Imani


Na biyu: shi ne muraqaba ,shi ne bawa ya yi aiki yana mai halarto da ganin Allah tare da kusatuwa zuwa gare shi ,idan bawa ya halarto wannan a cikin aikinsa yayi aiki akan shi yana mai Ikhlasi ga Allah ;saboda halarto da Shi hakan cikin aiyukansa zai hana shi juyawa zuwa ga wanin Allah da nufarsada wani aiki


Ma’abota waxannan maqaman suna wucewa gwargwadon tasirin hangensu


Abubuwan da suke kishiyar Imani


Me ne ne kishiyar Imani?


Kishiyar Imani shine kafirci,asli yana da rabe – rabe kamar yadda Imani shima a asali ya da su .An sani a abinda ya gabata cewa aslin Imani shine gasgatawa tare da miqa wuya da Da’a ,shi kuma kafirci shine musawa da taurin kai abin lazimtawa ga girman kaida savawa, Da’a gabadayanta yanki ce na Imani ,an ambace ta a cikin nassoshi masu yawa tana daga cikin Imani kamar yadda ya gabata ,shi kuma savawa gakixayansa yanki ne na kafirci ambaci haka a nassoshi da dama da kafirci kamar yadda zai zo,idan ka san wannan zaka san cewa kafirci gida biyu ne ,kafirci babba yana fita daga Imani gaba daya ,shi ne kafirci da yin I’’itiqadi mai kore faxin zuciya da aiki da shi ko da daya daga cikinsu ,shi kuma qaramin kafirci shine yak e kore cikar Imani bay a korewa a sake ,shi ne kafirci na aiki shi baya warware fadin zuciya ko aikinsa baya lazimta haka


Yadda za’a kore qudurtaccen kafirci da Imani gaba daya


Bayyana min yadda za’a kore qudurtaccen kafirci da Imani gabaxaya ka kuma rarrabe abinda nah axe shi wajen gusar da shi?


Ya gabata gare ka cewa Imani shi ne magana da kuma aiki ,faxin zuciya da kuma harshe ,da kuma aikin zuciya da kuma harshe da gavbobi,shine gasgatawa ,fadin harshe kuma ,shine zane da Kalmar musulunci,aikin zuciya kuma shi ne niyya da ikhlasi ,aikin gvvai kuma shine ,miqa wuya da dukkanin biyayya ,idan gabakidayan waxannan abubuwa hudun suka gushe faxin zuciya da aikinta fadin harshe da aikinshi da aikin gavvai Imani ya gushe baki daya,idan gasgatawar zuciya ya gushe sauran ba za su yi amfani ba ,domin cewa gasgatawar zuciya wani abu ne daga sallamawarta ta kuma kasance mai amfani wannan kamar wanda ya qaryata sunayen Allah ne da siffofinSa ko da kowanne abu da Allah ya aiko da shi ya saukar da LittattafanSa da shi ,idan aikin zuciya ya gushe tare da I’itiqadi na gaskiya.


Ahlus Sunnah sun haxu kan cewa gushewar Imani gaba daya baya amfanar gasgatawa tare da tsarkakewar aikin zuciya shine sonsa da kuma miqa wuya ,kamar yadda suke qudurce gaskiyar Manzon


Allah suna masu girmama shi a fili da Boye suna cewa shi ba Maqaryaci ba ne sai mu ba zamu bi shi ba ,ba kuma zamu yi Imani da shi ba


Nawa ne kasha – kashen babban kafirciwanda ya ke fitarwa daga addini?


Me ne ne kafirci na jahilci da qaryatawa?


Nawa ne kasha – kashen babban kafirciwanda ya ke fitarwa daga addini?


Mun sani daga abinda da ya gabata cewa ya kasu gida huxu :kafirci na jahilci da qaryatawa ,kafirci na musantawa,kafirci na taurin kai da girman kai ,da kuma kafirci na munafurci.


Me ne ne kafirci na jahilci da qaryatawa?


Shine abinda ya kasance a zahiri da kuma badini kamar kafiran quraishawa da wadan da suka gabace su daga al’ummatan da suka gabata


Allah Maxaukakin Sarki Yan a cewa akan su:


Wadan da suka qaryata,game da Littafin,kuma da abinda Muka aika Manzanninmu da shi.To za su sani.


kuma Allah Madaukaki ya ce


Kuma ka kau da kai daga Jahilai


kuma Allah Madaukaki ya ce


Kuma a ranar da Muke Tarawa daga kowacce al’umma,wata qungiya daga waxanda suke qaryata ayoyinMu,sai gas u ana kange su (ga kora) Har idan sun zo (Allah)zai ce ,’’Ashe kun qaryata ayoyinNa,kuma ba ku kewaye su da sani ba? To me ne ne kuka kasance kuna aikatawa?’’


kuma Allah Madaukaki ya ce


A’a,sun qaryata game da abin da ba su kewaye da saninsa ba,kuma fassararsa ba ta riga ta je mu su ba


Kafirci na musantawa


Me ne ne kafircin Musantawa?


Shine wanda ake boye gaskiya da rashin miqa wuya gare shi a zahiri tare da sanin hakan ,saninsa yana boye ,kamar kafircin Fir’auna da mutanensa ga Musa,da kuma kafircin yahudawa ga Annabi Muhammad tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi


Kuma suka yi musunsu,alhali zukatansu sun nutsu da su domin zalunci da girman kai


Kuma suka yi musunsu,alhali zukatansu sun nutsu da su domin zalunci da girman kai


Allah Ta’ala Ya ce akan yahudawa:


To a loqacin da abin da suka sani ya je musu,sai suka kafirta shi


kuma Allah Madaukaki ya ce


Kuma lallai ne wani vangare daga gare su,haqiqa,suna boyewar gaskiya alhali kuwa suna sane.


Me ne ne kafircin taurin kai da kuma girman kai?


Kafircin munafurci


Me ne ne kafircin taurin kai da kuma girman kai?


Shine rashi miqa wuya ga gaskiya da guje masa,kamar kafircin Iblis loqacin da Allah Maxaukakin Sarki yak e cewa:


Face Iblis ya qi,kuma ya yi girman kai,kuma ya kasance daga cikin kafirai


Bai dace daga gare shi ba musa umarnin Allah ko yi masa inkari ,sai dai ma ya juya baya gare shi ya kuma soke shi cikn hikimar umarnin shi da adalcinSa, ya ce:


Shin zan yi sujuda ne ga wanda Ka halitta daga Tavo ?


Kuma ya ce:


Ya ce: ’’ban kasance ina yin sujuda bag a mutum wanda Ka halicce shi daga busasshen yunbuun laka wadda ta canja’’


Kuma ya ce:


Ya ce: Ni ne mafificidaga gare shi,Ka halittani daga Wuta alhalikuwa Ka halitta shi daga laka


Me ne ne kafircin munafirci?


Shine abinda ya kasance da rashin gasgatawar zuciya da sanin shi rtare da miqa wuya a zahiri dan riya ga mutane,kamar kafircin Ibn Salul da jama’arsa


Allah Madaukakin Sarki ya ce


Kuma akwai daga cikin mutane wanda yake cewa :’’Mun yi Imani da Allah kuma da yinin Lahira ‘’ alhali k sub a Muminai ba ne .Suna yaudarar Allah da waxanda suka yi Imani ,alhali bas u yaudarar kowa face,kansu kuma basu sakankancewa.Acikin zukatansu akwai wata cuta,sai Allah Ya qara musu wata cutar,kuma suna da azaba mai raxaxi saboda abinda suka kasance suna yin a qarya –har zuwa ‘’Lallai Allah akan dukan koai Mai iko ne"


kafirci wanda baya fitarwa dag Addini


Me nene kafirci wanda baya fitarwa dag Addini ?


Shi ne kowane irin Sabo da Shari'a ta kirashi da sunan Kafirci tare da wanzuwar Sunan Imani ga Mai yinsa, Kamar fadin Annabi tsira da Aminci su tabbata a gareshi "kada ku koma bayana Kafirai wasu daga cikinku suna kashe wasu" da kuma fadinsa "Zagin Musulmi Fasikanci ne kuma yakarsa Kafircin" sai ya kira yakar Musulmi tsakanin junansu da cewa shi Kafirci ne kuma ya kira wanda yake yin hakan da Kafiri, tare da fadin Allah Madaukakin Sarki


kuma idan jama’a biyu ta muminai suka yi yaki, to kuyi sulhu a tsakaninsu- zuwa fadinsa- kadai muminai ‘yan’uwa ne to kuyi sulhu a tsakanin ‘yan’uwanku guda biyu


Sai Allah madaukakin sarki ya tabbatar musu da Imani da kuma ‘yan’uwantakar Imani kuma bai kore musu wani abu daga hakan ba


Kuma Ubangiji madaukaki ya fada acikin Ayar kisasi:


To wanda aka yi rangwamen wani abu gare shi daga dan’uwansa to abi da Alheri, da biya zuwa gare shi da kyautatawa


Sai Allah madaukaki ya tabbatar masa da ‘yan’uwartakar Musulunci bai kore ta daga gare shi ba


Haka kuma Annabi tsira da amincin Allah su tabbata agareshi yace:“Mazinaci baya zina alokacin da yake zinar alhalin yana mumini, kuma baya sata alokacin da yake satar yana mumini, kuma baya shan giya yayin da yake shanta yana mumini, kuma tuba abin bujurowa ne daga baya” yayi kari a cikin wata riwayar” kuma bazai yi kisa ba a lokacin yana mumini- acikin wata riwayar kuma-kuma ba zai kwaci wani abu mai Daraja ba da zai sa Mutane su rika daga kansu sama sabida ganinsa, Hadisin yana nan cikin Buhari da Muslim


Hadi da Hadisin Abi zarrin kuma, Annabi tsira da amincin Allah su tabbata agareshi yace: babu wani bawa da zai ce Laa’ilaaha illallahu sannan ya mutu akan haka sai ya shiga Aljanna” sai nace kuma koda yayi zina kuma yayi sata? Sai yace: koda yayi zina kuma yayi sata” ya fada sau uku sannan yace ana hudun ”Ko da kuwa Abu Zarr baya so"


To wannan yana nuni da cewa ba’a kore gaba ki dayan imani ga Mazinaci da Barawo da Mashayin giya da wanda yayi kisa matukar yana mai dayanta Allah, domin cewa shi da yana nufin hakan ba zai bada labari ba da cewa duk wanda ya mutu abisa La’ilaha illallahu zai shiga Aljanna,kuma idan ya aikata wadancan laifuka to bazai shiga Aljannaba sai dai rai Mumina,


Yana nufi da hakan tawayar imani da kuma kore cikarsa, kuma kadai Bawa yana kafirta ne da wadan can laifuka tare da halartawarsa ita mai lazimta karyata Alkur’ani da Manzo acikin haramtata barima yana kafirta da kudirce halaccinta, kuma koda bai aikatata ba Allah shi ne mafi sani.


Yiwa Gumaka sujjada da wulakanta Alkur’ani da zagin Manzo da kuma wasa da Addini


Idan akace da mu shin yin sujjada ga Gumaka da kuma wulakanta Alkur’ani da zagin Manzo da wasa da Addini da makamantan wadannan wannan dukkaninsa yana daga kafirci na aiki cikin abinda yake bayyana, to saboda me ya kasance mai fitarwa daga addini kuma bayan kun san kafirci karami da aiki?


Kasani cewa wannan hudun da wanda yake shakalinta ba itace take daga cikin kafirci na aikiba sai dai ta fuskar kasantuwarta mai afkuwa da aikin gabobi cikin abinda yake bayyanuwa ga mutane, kuma sai dai cewa ita bata afkuwa sai tare da tafiyar Aikin zuciya na daga Niyyarsa da tsarkakewarsa da Soyaryarsa da kuma jawuwarsa ba wani abu da yake wanzuwa tare da ita daga wannan, to ita duk da ta kasance ta aiki a zahiri to cewa ita ba makawa mai lazimta kafircice na kuduri, kuma wannan baza ta afku ba sai daga Munafiki mai fita daga Addini ko mai kin gaskiya kuma shin abinda ya dauki munafukai a yakin tabuka abisa fadar Kalmar kafirci kuma sun kafirta bayan musuluntarsu kuma sun yi himma da abinda basu samu ba sai dai wancan tare da fadin su yayin da aka tambaye su “ kawai mun kasance muna hira kuma muna wasanni.


Ubangiji madaukakin sarki yace: kace shin da Allah da ayoyinsa da manzonsa kuka kasance kuna izgili? Kada ku kawo wani uzuri, hakika kun kafirta a bayan imaninku,kuma mu bamu san kafirci karami na aiki kawai ba sai dai na aiki tsantsa wanda bai lazimci I’itikadi ba kuma bai warware fadin zuci ko aikinsa.


Kashe kashen zalunci da fasikanci da kuma munafunci


Zuwa kaso nawa zalunci da fasikanci da munafunci suka kasu?


Kowannen su ya kasu gida biyu Babba shi ne Kafirci da kuma Karami shi ne kasa da haka


Misalin zalunci babba da karami


Mene ne Misalin zalunci babba da karami?


Misalign zalunci babba shine abinda Allah madaukaki ya ambata cikin fadinsa: hakika shirka wani zalunci ne maigirma. Da kuma fadinsa madaukakin sarki: lalle ne shi wanda ya yi shirka da Allah to lalle ne Allah ya haramta masa Aljanna. Kuma babu wasu mataimaka ga azzalumai.kuma misalin


zaluncin da yake koma bayan wancan sh ne wanda Allah ya ambata da fadinsa cikin suratu-aldalak: kuma ku ji tsoran Allah Ubangijinku kada ku fitar dasu daga gidajensu kuma kada su fita sai dai in suna zuwa da wata Alfasha mabayyaniya. Kuma wadan can iyakokin Allah ne.kuma duk wanda ya ketare iyakokin Allah to lallai ya zalunci kansa. Da fadin sa madaukakin sarki: kuma kada ku rike su a kan cutarwa domin ku yi zalunci, kuma wanda ya aikata wancan, to hakika ya zalunci kansa.


Misalin zalunci babba da karami


Mene ne Misalin zalunci babba da karami?


Misalin fasikanci babba shi ne wanda Allah madaukakin sarki ya ambata cikin fadinsa lalle Munafukai su ne Fasikai. Da fadinsa madaukakin sarki sai dai Iblis ya kasance daga Aljanu sai ya yi fasikanci ga barin umurnin Ubangiji. Da kuma fadinsa: kuma muka tserar dashi daga Alkaryar nan da take aikata munanan aiyuka. Lalle su sun kasance mutanen mugun aiki,fasikai. Kuma misalin fasikanci koma bayan wancan shi ne fadinsa madaukakin sarki ga masu kazafi: kuma kada ku karbi wata shaida a gurinsu har abada, wadancan su ne fasikai. Da kuma fadinsa madaukakin sarki: ya ku wadanda suka yi imani idan fasiki ya zo muku da wani labari to ku nemi bayani, domin kada ku cuci wasu mutane a cikin zalunci , saboda haka ku wayi gari a kana bin da kuka aikata kuna masu nadama. An rawaito cewa ita ta sauka a kan Walidu dan Ukbata


Misalin kowanne daga Babban Munafunci da kuma Karami


Mene ne Misalin zalunci babba da karami?


Misalin munafunci babba shi ne wanda ambatonsa ya gabata a cikin ayoyin farko na suratu-albakra da kuma fadinsa madaukaki: lalle ne Munafukai suna yaudarewa da Allah, alhali kuwa shi ne mai yaudarar su zuwa fadinsa lalle ne Munafukai suna cikin magangara mafi kaskanci daga wuta. Da fadinsa madaukaki: idan Munafukai suka je maka suka ce, muna shaidar lalle kai hakika Manzon Allah ne kuma Allah yana sane da lalle kai Manzonsa ne kuma Allah yana shaida lalle Munafukai hakika makaryata ne. da kuma wadan su wadan can daga ayoyi, kuma misalin munafunci wanda yake koma bayan wancan shi ne wanda Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya fada a cikin fadinsa: Alamar Munafiki uku ce, idan ya yi zance sai ya yi karya, idan kuma ya yi alkawari sai ya saba, idan kuma aka amince masa sai ya yi ha’inci. Da kuma hadisin “abu hudu wanda suka kasance a cikinsa ya kasance Munafiki


Hukuncin tsafi da Matsafi


Menene hukuncin tsafi da Matsafi?


Tsafi samuwarsa da tasirinsa tabbatacce ne amma tare da dacewa da kadaru na kasancewa, kamar yadda madaukaki ya fada: suna neman Ilmin abin da suke Rarrabewa tsakanin mutum da Matarsa das hi daga gare su. Kuma sub a su zama masu cutar da kowa da shi ba, face da Iznin Allah. Kuma tasirinsa tabbatacce ne cikin Hadisai ingantattu.


Amma kuma Matsafi duk da kasancewar tsafin nasa daga abinda yake samu ne daga Shaidanu kamar yadda ayar Bakara ta yi nassi a kansa to shi Kafiri ne saboda fadinsa madaukaki: kuma ba su sanar da kowa ba face sun ce: mu fitina kawai ne, saboda haka kada ka kafirta zuwa fadinsa- kuma suna neman ilmin abinda yake cutar dasu,kuma ba ya amfaninsu. Kuma lalle ne hakika sun sani tabbas wanda ya saye shi ba shi da wani rabo a cikin Lahira.


Haddin Matsafi


Menene haddin Matsafi?


Tirmizi ya rawaito daga Jundubi y ace: Manzan Allah tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: haddin Matsafi dukansa da takobi. Kuma ya inganta wakafinsa


Ya ce kuma aiki a kansa yake a wajan sashin ma’abota ilimi daga sahabban Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da kuma shi ne fadin Maliku dan Anas


Kuma Shafi’i Allah madaukaki ya jikansa ya ce: kadai ana kasha Matsafi idan ya kasance yana aiki da tsafin nasa abinda yakai matsayin kafirci, amma idan ya yi aiki koma bayan kafirci to baya ganin kisa a kansa, kuma ya hakika ya tabbata kasha kasha Matsafi daga Umar da dansa Abdullah da ‘yarsa Hafsah da Usman dan Affan da Jundubi dan Abdullah da Jundubi dan Ka’abu da kais bin Sa’ad da Umar dan Abdul’aziz da Ahmad da Abi Hanifa da wadansunsu Allah ya ji kansu.


Ta’arifin Al-nushrah da Hukuncinta Rukiyya da aka shara’anta


Menene Al-nushra kuma menene Hukuncinta?


Al-nushrah it ace warware tsafi ga wanda akaiwa tsafin to idan hakan ya kasance da tsafi ne kwatankwacinsa to ita daga aikin Shaidan ne, kuma idan ta kasance da rukiyya ce da kuma matsarai wanda aka shar’anta to babu laifi da hakan.


Mecece rukiyyar da aka shara’anta?


Ita ce wacce ta kasance daga Kur’ani da sunna tsarkakakkiya kuma ta kasance da harshen larabci, kuma kowanne daga mai rukiyyar da wanda akewa rukiyyar suka kudirta cewar tasirinta baya kasancewa said a izinin Allah mabuwayi kuma madaukaki domin cewa Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi hakika Jibrilu ya yi masa rukiyya, kuma shi da kansa ya yiwa da yawa daga cikin sahabbai kuma ya tabbatar musu da aikata ta barima kuma ya umarce su da ita kuma ya halatta musu karbar lada a kanta, dukkan wancan yana cikin Bukhari da Muslim da wadansunsu.


Rukiyyar da aka hana


Mecece rukiyyar da aka shara’anta?


Ita ce wacce bata kasance ta Alkur’ani da sunna ba kuma bata kasance da larabci ba bari dai ita daga aikin Shaidan da kuma neman yi masa hidima, da kuma kusanci zuwa gare shi da abinda yake so kamar yadda da yawa daga makaryata da ‘yan rufa ido


Hukuncin rataye rataye na daga layu da tsirkiya da Guru da Kashi da Maikama da su


Menen Hukuncin rataye rataye na daga layu da tsirkiya da Guru da Kashi da Maikama da su?


Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: wanda ya rataya wani abu to an jingina shi a gareshi


Manzan Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi a cikin sashin tafiye tafiyansa ya aiki wani jakada a bisa cewa kada ya bar wata laya ko rataye a wuyan wani rakumi face ya tsinke ta


Kuma tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: lalle rukiyya da layu da maganin soyayya shirka ne


Kuma tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: duk wanda ya rataya laya kada Allah ya kare shi kuma duk wanda ya rataya dodon kodi to kada Allah ya kare shi A cikin wata riwayar kuma “wanda ya ya rataya laya to hakika ya yi shirka


Kuma tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya fada ga wanda ya ga a hannunsa akwai kewaye na daga tagulla, sai y ace masa menene wannan? Sai y ace maganin raunin tsufa ne.sai y ace masa jefar da ita domin ita ba za ta kara maka komai ba face rauni,domin cewa da ka mutu tana jikinka dab a za ka rabauta ba har abada


Kuma Huzaifa Allah ya yarda da shi ya yanke zare daga hannun wani mutum sannan ya karanta fadinsa madaukaki:


Kuma da yawa mafi yawansu basa imani da Allah face suna masu shirka


Kuma Sa’idu dan Jubair Allah ya jikansa y ace wanda ya yanke wata laya daga wani mutum ya kasance kamar wanda ya ‘yanta wuyaye,


Kuma wannan yana da hukuncin Hadisi marfu’i.


Menene hukuncin abin ratayawar idan ya kasance daga Alkur’ani ne?


An rawaito halaccinsa ga sashin magabata kuma mafi yawansu sun tafi abisa hana shi kamar Abdullah bun Akim da Abdullah bin Amru da Abdullah bin Mas’ud da sahabbansa tsira da amincin Allah su tabbata a gare su kuma shi ne ya fi saboda gamewar hanin ga ratayawar, kuma saboda rashin wani abu na daga hadisi marfu’I da zai kebance wancan kuma saboda kiyaye Kur’ani daga wulakanta shit a inda za’a iya daukarsa galibi ba tare da tsarki ba, kuma hakan yana iya bayuwa izuwa rataya waninsa,kuma saboda toshe kafa abisa I’itikadin abinda aka hana da kuma karkatawar zuciya zuwa ga wanin Allah musamman a cikin wannan zamani.


Hukuncin Bokaye


Menene hukuncin Bokaye?


Bokaye suna daga Dagutai kuma sune masoyan shaidanun da suke yi musu wahayi kamar yadda Allah madaukaki y ace:


Kuma lalle ne shaidanu hakika suna yin ishara zuwa ga masoyansu


Zuwa karshen ayar


Kuma suna sassauka a kansu suna jefa musu kalmomin da suka jiyo sannan sai su hada tare da ita karya dari kamar yadda madaukaki y ace:


Shin in gaya muku a kan wanda shaidanu kan sauka? Sukan sauka a kan dukan makaryaci, mai zunubi. Suna jefa ji alhali mafi yawansu makaryata ne.


Kuma tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi y ace: a cikin hadisin wahayi sai mai satar ji ya ji ta da kuma wani mai satar jin haka dai sashinsa yana birbishin sashi to sai ya jefawa wanda yake kasansa sannan shima ya jefawa wani da yake kasansa har sai ya jefata abisa harshen Matsafi ko Bokan to wani lokacin sai tauraro ya riske shi kafin ya jefata wani lokacin kuma zai sami jefatan amma zai hada ta da karya dari. Hadisin yana cikin Bukhari da cikarsa


Kuma yana daga wancan zane da kasa wanda suke kiransa da bugun kasa, kuma da ta hanyoyin yi da tsakuwa da makamantansu.


Hukuncin wanda ya gasgata Boka.


Hukuncin wanda ya gasgata Boka.


AllahMaukakin Sarki ya ce


Ka ce: wanda suke sammai da kassai basu san gaibu ba sai Allah


kuma Allah Madaukaki ya ce


Kuma mabudan gaibu suna gurinsa ba wanda ya sansu sai dai shi kakaranta har zuwa karshen Ayar


kuma Allah Madaukaki ya ce


Ko kuma suna da ilimin gaibu ne, da suke rubutawa


kuma Allah Madaukaki ya ce


Shin akwai ilimin gaibu a wurinsa, saboda haka yana ganin gaibin a cikin sa?


kuma Allah Madaukaki ya ce


Kuma Allah ne ya sani kuma ku ba ku sani ba


Kuma Annabi tsira da amincin Allah su tabbata agare shi y ace: dukkan wanda ya je wajan dan duba ko Boka ya kuma gasgata shi da abinda ya fada to hakika ya kafirta da abinda aka saukarwa Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi


Kuma tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi ya ce: wanda ya je wajan dan dubakuma ya tambaye shi ga wani abu sannan kuma ya gasgata shi ba za’a karbi sallar kwana arba’in daga gareshi ba


Hukuncin Ilimin taurari


Menene Hukuncin Ilimin Taurari?


Allah Madaukakin Sarki ya ce:


Kuma shi ne wanda ya sanya muku taurari don ku shiryu da su a cikin duffan tsandauri da ruwa.


kuma Allah Madaukaki ya ce


Kuma lalle mun kawata saman Duniya da fitilu , kuma muka sanya su abin jifa ga shaidanu


kuma Allah Madaukaki ya ce


Kuma taurari Horarru ne da umarninSa


Kuma Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi y ace: dukkan wanda ya dosani wani yanki na taurari to hakika ya dosani wani yanki na daga tsafi ya kara abinda ya kara


Kuma Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi y ace: kadai abinda na ke tsoro abisa al’umata si ne gasgatawa da taurari da kuma karyatawa da kaddara da zaluncin shugabanni


Kuma dan Abbas Allah ya yarda da su ya fada ga mutanen da suke rubuta Abajada kuma suke duba a cikin taurari” ba na ganin ga wanda yak e aikata wancan yana da wani rabo a wajan ubangiji”


Kuma Katada Allah ya jikansa y ace: Allah ya halicci wannan taurarin saboda abu uku: don ado ga sama da kuma jifa ga Shaidanu da kuma alamomi da ake samun shiriya dasu, to wanda ya yi fassara ba wannan ba to hakika ya kuskurewa rabonsa kuma ya tozartar da nasibinsa kuma ya kallafawa kansa abinda bas hi da ilimi das hi.


Hukuncin Rokon Ruwa da taurari


Hukuncin shu’umanci da abinda yake tafiyar da ita


Mene ne Hukuncin Rokon Ruwa da taurari?


Allah Madaukakin Sarki ya ce: Kuma kuna sanya Arzikinku lalle ku kuna karyatawa. Kuma Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:abubuwa Hudu a cikin al’umata yana daga al’amuran


jahiliyya kuma baza su barsu ba: alfahari da iyaye, da sukar dangi, da kuma neman shayarwar ruwa ga taurari, da kuma kukan kera


Kuma tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi y ace Allah madaukaki y ace: a cikin bayina an wayi gari akwai wanda ya yi imani da ni da kuma wanda ya kafirta, amma wanda y ace an yi mana ruwa da falalar Allah, to wannan shi ne ya yi imani da ni ya kafirta da taurari, amma wanda kuma wanda y ace ammana ruwa saboda tauraro kaza da kaza to wannanya kafirta da ni kuma ya yi imani da taurari


Hukuncin shu’umci da abinda yake tafiyar da ita


Allah ya yi masa Rahama


Ku saurara! Kadai shu’umcinsu yana ga Allah


Sai yace da shi haqiqa Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi


Babu adwa(harbin cututtuka ta kashin kansu) babu shu’umci babu camfi da mujiya, ba camfa watan safar


Sai yace da shi haqiqa Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi


Shu’umci shirk ace shu’umci shika ce


Ibn Mas'ud ya ce:


Kuma babu wani daga cikinmu face (wato wani abu da wannan ya darsu a cikin zuciyarsa) amma Allah yana tafir dashi da dogaro ga Allah


Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:


Shu’umci kawai shi ne abinda ya sa ka ka aikata wani abu ko ya hana ka, kuma an karbo daga Ahmad daga hadisin Abdullah bin Amru : wanda shu’umci ya komar das hi ga barin bukatarsa to hakika ya yi shirka. Sai suka ce to menene yake kankare hakan? sai Ya ce: ku ce ya Allah babu wani alheri sai dai alherinka, babu shu’umci sai abinda ka halitta, kuma babu abin bautawa da gaskiya sai kai


Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:


Mafi gasgatuwarta kyakkyawan fata kuma kada ta komar da musulmi, to idan daya ya ga abinda yake ki to y ace: ya Allah ba wanda yake zuwa da kyakkyawa sai kai kuma ba wanda zai ije mummuna sai kai, kuma babu wayo babu karfi sai sai daga kai


Hukuncin kambun baka


Menene hukuncin kambun baka?


Sai yace da shi haqiqa Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi


Kambun baka gaskiya ne kuma Annabi ya ga wata Baiwa a fusarta ta Dashe sai yace kuyi mata Magani Kambun Baka ya kamata


Aisha- Allah ya yarda da ita -


Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya umarce ni ko Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yi umarni a nemi magani daga kambun baka


Sai yace da shi haqiqa Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi


Babu rukiyya sai dai daga kambun baka ko zazzabi


Kuma dukkaninta tana cikin Bukhari kuma a cikinta akwai hadisai masu yawa banda wadanda muka ambata,


Kuma bata da tasiri face da izinin Allah kuma hakika an fassara da ita fadinsa mai girma da daukaka kuma lalle ne wadanda suka kafirta suna yin kamar su kayar da kai saboda kallonsu, a lokzcin da suke jin karatun Alkur’ani, daga masu yawa na daga magabata na kwarai Allah ya yarda da su.


Kashe kashen sabo


zuwa kaso nawa sabo ya kasu?


Ya kasu zuwa kananu it ace munana, da kuma manya suna masu halakarwa.


Abubuwan da ake kankare munana da su


Da menene ake kankare munanan ?


Allah ya yi masa Rahama


Idan kuka nisanci manya manyan abinda aka haneku da shi to zamu kankare muku munanan aiyukanku kuma mu shigar daku mashiga ta karamci


kuma Allah Madaukaki ya ce


Lalle kyawawan aiki suna tafi da munanan


Sai ubangiji madaukakin sarki ya bamu labari cewa munanan ana kankareta da nisantar manyan da kuma yin aiki mai kyau


Haka nan kuma ya zo a cikin hadisi


Ka bibbiyi mummuna da kyakkyawa ta shafe ta.


Haka kuma ya zo a cikin hadisi ingantacce cewa kyautata alwala a bisa lokutan ki,da cirar taku izuwa masallaci da kuma sallolin biyar biyar da juma’a zuwa juma’a, da ramadana zuwa ramadana da tsaya shi da tsayuwar daren lailatul kadri da azimin ranar ashura da wadansunsu na daga da’o’I lalle ita mai kankare munana ne kurakurai


Da yawan wadancan hadisan akwai kayyadewa a cikinsu da nisantar manyan kuma akansa ne ake daukar sakakken daga gareta sai ya zama nisantar manyan sharadi ne na kankarewar kananun da kyawawa da kuma koma bayan ta.


Ta’arifin manyan


Menene manyan


A cikin tabbatar da hakikaninta akwai maganganun sahabbai da tabi’ai da wadansunsu, aka ce it ace dukkan zunubi da aka bishi da tsinuwa ko wuta ko kowace irin ukuba,kuma aka ce: it ace kowane laifi wanda ake jin aikata shi da rashin kin mai aikata shi da addini da kuma rashin damuwa da shi da kuma karancin tsoransa da Allah, kuma aka ce wani ba wannan ba, kuma hakika ya tabbata a cikin hadisai ingantattu ambaton da yawa daga cikin zunubai da kaba’ira bisa banbancin darajojinsu yana daga cikinsu kafirci mafi girma kamar shirka da Allah da tsafi, kuma yana daga cikinsu babba daga cikin manyan sabo da alfasha, kuma shi ne koma bayan wadancan, kamar kasha rai wanda Allah ya hana a kasha sai da gaskiya, da kuma juyawa a fagen fama, da cin riba da cin dukiyar maraya da fadin karya, yana daga cikinsu yiwa katangaggu rafkanannu muminai mata kazafi da shan giya da sabawa iyaye da wadansun wadannan


Ibnu Abbas ya ce Allah ya yarda da shi: "Su ne zuwa Saba'in kuma mafi kusanci da Bakwai"


Da wadannne Abubuwan da ake kankare Manyan Zunubai da da kanana da su


Abubuwan da ake kankare Manyan Zunubai da da kanana da su


Da wadannne Abubuwan da ake kankare Manyan Zunubai da da kanana da su


Ana kankare su baki daya da tuba na gaskiya


Allah ya yi masa Rahama


Ya ku wadanda suka yi imani ku k0ma zuwa ga Allah komawa ta gaskiya. Mai yiwa ubangijinku ya kankare muku miyagun aiyukanku kuma ya shigar da ku a gidan Aljanna, koramu na gudana daga karkashinta


Kuma mai yiwuwa daga Allah tabbas ce


kuma Allah Madaukaki ya ce


Sai dai wanda ya tuba kuma yayi imani kuma ya yi aiki aiki na gari to wadannan sune wadanda Allah yake canza munanansu da kyakkyawa….


kuma Allah Madaukaki ya ce


Kuma wadanda suke idan suka aikata aifasha ko suka zalunci kansu sai su tuna allah, saboda su nemi gafarar zunubansu ga Allah,kuma wanene yake gafarar zunubai face Allah?kuma ba su doge a kan abinda suka aikata ba,alhali kuwa suna sane. Wadannan sakamakonsu gafara ce daga Ubangijinsu da kuma gidajen Aljanna wanda koramu ke gudana a karkashinsu


Sai yace da shi haqiqa Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi


Tuba tana kankare abinda yake kafinta


Sai yace da shi haqiqa Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi


Allah yafi farin ciki da tuban bawansa daga mutumin da ya sauka a wani masauki yana da matsera,kuma a tare dashi akwai abin hawansa akanta akwai abincinsa da abin shansa sai ya sanya kansa ya yi bacci sosai, sai ya farka abin hawansa ya gudu har saida zafi da kishirwa suka yi tsanani a gare shi, ko sanda Allah ya so sai ya ce: bari na koma gurina sai ya koma ya kara yin bacci sosai sannan ya daga kansa kawai sai yaga abar hawansa a wajansa


Tuba na gaskiya


Menene tuba na gaskiya?


Shi ne tuba na gaskiya wanda ya hadar da abubuwa guda uku: ciruwa daga sabo, da kuma nadama abisa yinsa da yin niyya abisa ba za’a kuma komawa sabon ba har abada, kuma idan ya kasance a cikinsa akwai wani abin zalunta na wani musulmi sai ya warwareta daga gare shi in hakan ya yiwu domin cewa shi da sannu za’a neme shi da ita ranar alkiyama idan bai warwareta daga gare shi ba a yau, kuma za’a yi masa kisasi daga gare shi babu makawa, domin shi yana daga zaluncin da Allah baya barin komai daga gare shi, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:


Wanda ya kasance a gurinsa akwai wani abin zalunci na dan uwansa to ya yi kokari ya warware shi daga gare shi a yau tun kafin lokacin da babu dinare babu dirhami,in ya kasance yana da kyawawan aiki sai a dauka daga kyawawansa in kuwa babu sai a dauko daga munanan aikin dan uwan nasa sai jefa masa a kansa


Abinda ake yanke tuba dashi a cikin hakkin kowane Mutum


Yaushe ne ake yanke tuba a cikin hakkin kowane daya daga daidaikun mutane?


Allah Madaukakin Sarki ya ce:


Abin da yake tuba kawai ga Allah, it ace ga wadanda suke aikata mugun aikida jahilci sa’annan su tuba nan kusa.to wadannan Allah yana karbar tubansu, kuma Allah ya kasance masani ne, Mai hikima.


Sahabban manzan Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi sun hadu a kan cewa dukkan abinda aka sabawa Allah da shi to wannan jahilci ne dai dai ne ya kasance da ganganci ne ko waninsa, kuma dukkan abinda ya kasance kafin mutuwa to wannan kusa ne


Kuma Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi y ace: lalle Allah yana karbar tuban Bawa matukar bai kai gargara ba wannan ya tabbata a cikin hadisai masu yawa,


Amma idan ya ga Mala’ika kuma rai ya zo kirji kuma ya isa makogaro kuma numfashi ya zo gangara to babu karbar tuba a wannan lokacin kuma babu kubuta


Kuma wancan shi ne fadinsa mai girma da daukaka a karshen wannan Ayar


Kuma tuba bata kasance ba ga wadanda suka aikata munanan aiki har said a mutuwa ta zowa dayansu sai ya ce: lalle ni na tuba a yanzu


Zuwa karshen ayar


Lokacin yankewar tuba daga rayuwar Duniya


Yaushe ne lokacin yankewar tuba daga rayuwar Duniya


AllahMadaukakin Sarki ya ce:


A ranar da sashin Ayoyin Ubangijinka suke zuwa, Imanin rai wanda bai kasance ya yi imanin ba a gabani, ko kuwa ya yi tsiwirwirin wani Alheri, ba ya Amfaninsa


Kuma acikin sahihul Bukhari Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: lahaira ba zata tashi ba har sai rana ta fito daga mafadartato idan ta fito mutane suka ganta sai suyi imani baki dayansu kuma a wannan lokaci rai imaninta ba zai amfanar da ita ba


Sannan ya karanta Ayar,kuma hakika ya zo a cikin ma’anarta hadisai masu yawa daga jama’a na daga sahabbai daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi cikin iyaye mata da makamantansu


Safwan dan Assal y ace: na ji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa: lalle Allah ya bude wata kofa a yamma fadinta tafiyar shekara arba’in ne saboda tuba ba za’a rufeta ba har sai rana ta fito daga gareta.


Tirmizi ne ya rawaito shi da nasaa’I da dan majah a cikin wani hadisi mai tsayi.


Hukuncin wanda ya mutu daga cikin masu dayanta Allah yana mai zarcewa a bisa manyan sabo


Maye Hukuncin wanda ya mutu daga cikin masu dayanta Allah yana mai zarcewa abisa manyan sabo


Fadin Allah maigirma da Daukaka:


Kuma muna sanya ma’aunan adalci ga ranar kiyama, saboda haka ba a zaluntar raid a kome. Kuma koda ya kasance nauyin kwaya daga komayya ne mun zo da ita.kuma mun isa zama masu Hisabi


kuma Allah Madaukaki ya ce


a wadannne Abubuwan da ake kankare Manyan Zunubai da da kanana da su


kuma Allah Madaukaki ya ce


A ranar da kowane rai yake samun abin day a aikata daga alheri, a halarce,da kuma abin da ya aikata daga alheri


kuma Allah Madaukaki ya ce


A ranar da kowane rai yake samun abin day a aikata daga alheri, a halarce,da kuma abin da ya aikata daga alheri


Kuma ya ce:


Kuma kuji tsoron wata Rana wacce kuke komawa zuwa ga Allah sannan a sakawa kowace Rai da abinda ta aikata kuma ba za'a Zalunce su ba


kuma Allah Madaukaki ya ce


A ranar nan mutane za su fito daban-daban domin a nuna musu aiyukansu. to Wanda ya aikata gwargwadon kwayar zarra na alheri zai gan shi. Kuma wanda ya aikata gwargwadon kwayar zarra na sharri zai gan shi


Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:


Wanda aka binciki hisabinsa za’a yi masa Azaba


Sai A’isha Allah ya yarda da ita ta ce da shi shin ba Allah ne yake cewa: to da sannu za’a yi musu hisabi hisabi mai sauki? Sai ya ce haka ne,kadai wannan bujirowa ne kuma sai dai cewa duk wanda aka bincike hisabinsa za’a yi masa azaba


Kuma hakika mun gabatar da nassoshi game da tashi da halayen matsaya da ma’auni da bude littattafai da bujirowa da hisabi da siradi da ceto da kuma makamantansu abin da ake sani das hi fifikon darajojin mutane, da kuma bayyanar halayensu a cikin lahira ta gwargwadon fifikonsu a gidan duniya cikin biyayyarsu ga Ubangijinsu, da kuma kishiyarta na daga mai tserewa da mai tsakaitawa da kuma mai zaluntar kansa;


Idan kasan wannan to kasani lalle abin da ayoyin kur’ani da sunnonin annabta suka tabbatar kuma magabata na kwarai da na farko daga sahabbai da wadanda suka bisu da kyautatawa daga shugabannin tafsiri da hadisi da sunna suka tafi a kai cewa: masu sabo daga ma’abota tauhidi dabaka uku ne:


Ta farko: jama’ar da kyawawansu suka rinjayi munanansu to wadannan za su shiga Aljanna kuma wuta ba za ta shafe su ba har abada.


Ta biyu: jama’ar da kyawawansu da munanansu suka yi dai-dai munanansu ta takaita da su ga shiga Aljanna kuma kyawawansu ta tsallakar da su ga shiga wuta, wadannan su ne ma’abota bango wadanda Allah ya ambata cewa su ne wadanda ake tsayar da su tsakanin Aljanna da wuta iya lokacin da Allah ya nufi a tsayar da su sannan a yi musu izinin shiga Aljanna kamar yadda Allah ya fada bayan ya bada labara da shigar yan Aljanna Aljanna da kuma shigar yan Wuta Wutarkuma za’a kira su daga cikinta


Ya ce:


Kuma a tsakaninsu akwai wani shamaki, kuma a kan A’araf akwai wasu maza suna sanin kowa da alamarsu: kuma suka kirayi abokan Aljanna cewa: “Aminci ya tabbata a kanku: “bas u shigeta ba, alhali kuwa su, suna tsammani. Kuma idan aka juyar da gannansu wajen abokan wuta, su ce: “ ya Ubangijinmu! Kada ka sanya mu tare da mutane azzalumai


Zuwa fadin sa:


Ku shiga Aljanna, babu tsoro a kanku, kuma ba ku zama kuna bakin ciki ba.


Jama’a ta Uku : jama’a ne da suka hadu da Alllah suna masu dogewa abisa kaba’irar sabo da Alfasha amma a tare da su akwai asalin tauhidi da imani to sai munanansu suka rinjayi kyawawansu To wadannan su ne wadanda za su shiga Wuta na gwargwadon zunubansu to daga cikinsu akwai wanda zata kamashi zuwa guiwoyinsa,


Kuma akwai wanda zata kamashi zuwa rabin kaurinsa da wanda zata kamashi zuwa guiwoyinsa har cewa daga cikinsu akwai wanda Allah bai haramta wuta daga gare shi ba sai dai kawai bigiran sujjada, wannan jama’ar su ne wadanda Allah madaukaki yake bada ceto a cikinsu ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da kuma waninsa a bayansa daga Annabawa da waliyai da mala’iku da wadanda Allah ya so day a girmamashi, sai Allah ya yi musu wata iyaka sai su fitar dasu sannan ya kara yi musu wata iyakar sai su fitar dasu


sannan hakanan sai su fitar da wanda ya kasance a zuciyarsa akwai gwargwadon nauyin zinare na daga alheri, sannan wanda ya kasance a zuciyarsa akwai gwargwadon rabin nauyin dinare na daga alheri sannan wanda ya kasance a zuciyarsa akwai nauyin kwayar komaiya na daga alheri, zuwa su fitar daga cikinta wanda ya kasance a zuciyarsa akwai misalin nauyin kwayar zarra na daga alheri izuwa mafi koma baya daga misalin kwayar zarra izuwa masu ceton su ce Ubangijinmu bamu bar wani alheri a cikinta ba kuma ba daya wanda zai dawwama a wuta cikin wadanda suka mutu abisa tauhidi, kuma koda yayi kowane aiki, sai dai cewa duk wanda ya kasance mafi girman imani daga cikinsu kuma mafi saukin zunubi zai kasance mafi saukin azaba a cikin wuta kuma mafi karancin zama a cikinta kuma mafi saurin fita daga gareta, kuma duk wanda ya kasance mafi girman zunubi kuma mafi raunin imani zai kasance da kishiyar hakan.


Kuma hadisai a cikin wannan babi ba zasu kididdigu ba saboda yawansu kuma izuwa haka ne Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi ya yi nuni da fadinsa


Wanda y ace : la’ilaha illallahu zata amfane shi wata rana daga zamani abinda zai same shi zai same shi kafin haka


Wannan wani mukami ne wanda fahimtu suka bace a cikinsa kuma diga digai suka zame a cikinsa, kuma suka yi sabani a cikinsa sabani mai yawa to sai Allah ya shiryi wadanda suka yi imani ga abin da suka yi sabani a cikinsa na daga gaskiya da izininsa kuma Allah yanaa shiryar da wanda ya so zuwa ga hanya madaidaiciya


Shin haddi kaffara ne ga wanda akayi wa?


?Shin haddi kaffara ne ga wanda akayi wa


Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce a gefensa akwai wasu jama’a daga sahabbansa:ku yi min mubaya’a abisa baza ku tara Allah da wani abu ba kuma ba za ku yi sata ba kuma ba za ku yi zina ba kuma ba za ku kashe ‘ya’yanku ba kuma ba za ku zo da wata karya da kuke kirkirawa a tsakanin hannuwanku da kafafunku kuma ba za ku saba da wani abu da aka sani na shari’a ba to wanda ya cika daga gareku to ladansa yana wajan Allah, kuma wanda ya yi wani abu daga wancan sannan Allah ya suturta shi to shi yana ga Allah in ya so ya yi masa afuwa,in kuma ya sosai ya yi masa ukuba yana nufin ban da shirka Ubadat ya ce: sai muka yi masa mubaya’a abisa haka.


Hadawa tsakanin hadisan azabar Allah ga masu yin zunubi da kuma afuwarsa a gare su


Yaya za’a hadatsakanin fadinsa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi cikin wannan hadisin to shi izuwa Allah yake in ya so ya yi afuwa a gare shi, in kuma ya soya yi masa ukuba da kuma tsakanin abinda ya gabata daga cewa wanda munanansa suka rinjayi kyawawansa zai shiga wuta?


Ba mai korewa a tsakaninsu domin cewa wanda Allah ya so da ya yi masa afuwa sai ya yi masa hisabi sassauka wanda Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya fassara da bijurowa kuma ya fada a cikin siffanta shi dayan ku zai dinga kusantar Ubangijinsa mai girma da daukaka har sai ya saukar masa da kariyarsa, to sai ya ce: ka aikata kaza da kaza sai ya ce: haka ne sai ya kara cewa ka aikata kaza da kaza sai y ace : haka ne sai ya tabbatar masa sannan y ace: lalle na suturta ka a cikin


duniya, kuma ni na gafarta maka ita a yau amma kuma wadanda za su shiga wuta da zunubinsu to su ne wadanda ake bincika hisabinsu kuma hakika tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi y ace: wanda aka yiwa binciken hisabi to za’a yi masa azaba


Hanya madaidaiciya wanda Allah madaukaki ya umarce mu da binta kuma ya hane mu ga bin watanta


Wacce ce hanya madaidaiciya wanda Allah madaukaki ya umarce mu da binta kuma ya hane mu ga bin watanta


Shi ne Addinin musulunci wanda ya aiko manzanninsa da shi, kuma ya saukar da littattafansa da shi kuma ba zai karbi waninsa ga daya ba kuma ba wanda zai tsira sai wanda ya bishi, kuma duk wanda ya bi waninsa hanyoyi za su karkasu a kansa, kuma hanyoyi za su rarrabu da shi


Allah Madaukakin Sarki ya ce


Kuma lalle wannan ne tafarkina, madaidaici sai ku bi shi kuma kada ku bi wasu hanyoyi, su rarrabu da ku daga barin hanyata


Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya zana wani zane sannan y a ce: wannan itace hanyar Allah madaidaiciya kuma ya kara zana wani zanen a damansa da hagunsa, sannan ya ce: wannan hanyoyin babu wata hanya daga gareta face akwai Shaidan yana kira zuwa zuwa gare shi sannan ya karanta “kuma lalle wannan ne tafarki na, madaidaici sai ku bi shi kuma kada ku bi wasu hanyoyi,su rarrabu daku daga barin hanyata


Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce


Allah ya buga misalin hanya madaidaiciya kuma abisa geffan hanyar akwai bangwaye guda biyu acikinsu akwai wasu kofofi budaddu, kuma abisa kofofin akwai labulaye sakakku kuma abisa kofar hanya akwai wani mai kira yana cewa: yak u mutane ku shiga wannan hanyar madaidaiciya baki dayanku, kuma kada ku rarrabu da kuma wani mai kiran yana kira ta birbishin hanyar, to idan mutum ya nufi zai bude wani abu daga wadannan kofofin sai y ace kaitonka kada ka bud eta domin cewa kai idan ka budeta zaka shigeta,


To hanyar ita ce musulunci bangwayen biyu su ne dokokin Allah kuma kofofin budaddu su ne abubuwan da Allah ya haramta, kuma wancan mai kiran a kan hanyar shi ne littafin Allah, wanda yake kira a birbishin hanyar shi ne wani mai wa’azin Allah a cikin zuciyar kowane Musulmi.


Abin da zai zo da shi wajan bin hanya madaidaiciya da kuma kubuta daga karkacewa ga barinta


Da menene zai bi hanya madaidaiciya da kuma kubuta daga karkacewa ga baranta


Wancan ba ya samuwa sai ta hanyar riko da Alkur’ani da sunna, tafiyarwa irin tafiyarwarsu da kuma tsayawa nanga iyakokinsu, da kuma haka ne ake samun tsiraituwar tauhidin Allah da kuma tsiraituwar bi ga manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi


Kuma wadanda suka bi Allah da manzo to wadannan suna tare da wadanda Allah ya yi ni’ima a gare su daga Annabawa da Siddikai da Shahidai da managartan bayi kuma wadannan sun kyautatu ga zama abokan tafiya.


Kuma wadan nan da aka yi ni’ima a gare su da aka ambata anan a rarrabe su ne wadanda aka raba hanyar izuwa gare su acikin surar fatiha da fadinsa madaukaki


Ka shiryar damu hanya madaidaiciya hanyar wadanda ka yi ni’ima a gare su,ba wadanda aka yi wa fushi ba, kuma ba batattu ba


Kuma babu wata ni’ima ga bawa mafi girma wacce takai ta a shiryar das hi izuwa hanya madaidaicya, da kuma nisanta shi daga hanyoyi masu batarwa, hakika Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya bar al’umarsa akan hakan kamar yanda ya fada tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi: na barku akan hanya mai haske darenta kamar ranarta ne babu mai karkata ga buranta a baya na sai halakakke.


Bidi’o’i fararru


Menene kishiyar sunna?


Kishiyarsu su ne bidi’o’i fararru kuma ita ce shari’ar da ba Allah ne ya yi izini da ita ba kuma ita ce wacce Annabi tsira da amincin Allah yake nufi da ita da fadinsa “wanda ya farar da wani abu a cikin addininmu wannan, wanda babu daga gare shi to shi abin juyarwa ne “da kuma fadinsa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi “ina horanku da sunnata da sunnar halifofina shiryayyu ababan shiyarwa a bayana, ku yi ruko da ita, kuma ku yi cizo akanta da fika, kuma ina muku hani da fararrun al’amura, domin cewa kowa ne fararran abu bata ne sai Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yi nuni izuwa afkuwarta da fadinsa “da sannu al’umata za ta karkasu izuwa kaso saba’in da uku dukkansu suna cikin wuta face guda daya kuma ya ayyana tada fadinsa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi su ne wadanda suka kasance akan misalign abin da nake kai da sahabbaina” kuma hakika Allah madaukaki ya barrantar da shi daga ma’abota bidi’a da fadinsa “lalle wadanda suka rarraba addininsu kuma suka kasance jama’a jama’a ba ka tare da su a cikin wani abu kadai al’amarinsu yana ga Allah…


Kashe kashen bidi’a ta izna da shigarta ga Addini


Izuwa kaso nawa bidi’a ta kasu ta izna da shigarta ga Addini?


Ta kasu zuwa kaso biyu: bidi’a mai kafirtarwa da kuma bidi’a komawacce bata kai waccan ba


Bidi’o’I masu kafirtarwa


Mecece bidi’a mai kafirtarwa?


Ita tana da yawa amma yadda take, wanda ya yi inkarin wani al’amari wanda aka hadu akansa kuma yake da tawaturi a shari’a kuma larura ne a san shi a addini; domin cewa hakan karyatawa ne ga Alkur’ani da kuma abin da Allah ya aiko manzanninsa da shi kamar bidi’ar jahamiyyai a cikin inkarin siffofin Allah mai girma da daukaka, da kuma fadi da halittar kur’ani ko halittar kowace siffa daga siffofin Allah madaukaki da kuma inkarin cewa Allah ya riki Ibrahim badadayi kuma ya yi Magana da Musa Magana sosai da wadansun wadannan.


Da kamar bidi’ar ‘yan kadariyya cikin inkarin ilimin Allah madaukaki da aiyukansa da hukuncinsa da ikonsa, da kamar bidi’ar ‘yan tajsimi wadanda suke kamanta Allah madaukaki da halittarsa da wadansu wadannan na daga son zuciya, sai dai kuma wadannan akwai daga cikinsu wanda aka san cewa ainihin manufarsa shi ne rushe Addini, da san ya wa ahalinsa shakku a cikinsa to wannan abin yankeawa ne ga kafircinsa bari ma dai shi manisaci ne ga Addini kuma yana daga manyan makiyansa, kuma wadansu ababan rudarwa ne to wadannan kadai ana hukunci da kafircinsu bayan an tsayar musu da dalili a kansu da lazimta musu ita.


Bidi’a wacce bata kafirtarwa


Wacce bidi’a ce bata kafirtarwa


Ita ce wacce bata kasance kamar waccan ba ta daga abinda bai lazimta daga gare shi ba karyatawa da Alkur’ani bada kuma karyata abin da Allah ya aiko manzanninsa da shi ba kamar ‘yan marwaniyya


wacce sahabbai masu falala suka yi inkarinta,kuma ba su tabbatar da su akanta ba kuma ba su kafirta su da wani abu daga gareta ba,kuma ba su cire hannu ba wajan yi mu su mubaya’a saboda ita ba, kamar jinkirtawarsu ga sashin wasu sallolin izuwa karshen lokutanta, da kuma gabatarwarsu huduba kafin sallar idi da zama a cikin ita dai wannan hudubar a cikin juma’a da watanta, da kuma zaginsu ga sashin sahabbai akan minbarai da makamancin wancan daga abin da babu gare su na i’atikadi na shari’a bari dai kawai sai dai wani nau’I na tawili, da sha’awa sha’awe na rai, da manufofi na Duniya.


Kasha kashen bidi’a ta fuskar abin da take fadawa a cikinsa


Nawane kashe kashen bidi’a ta fuskar abin da take fadawa a cikinsa


Ta kasu zuwa bidi’o’i na cikin ibadu da bidi’o’i na cikin mu’amaloli.


Kashe kashen bidi’o’i na ibadu


Izuwa kaso nawa bidi’o’i suka kasu a cikin ibadu?


Zuwa kaso biyu:


Na farko: yin bauta da abin da Allah bai izini a bauta masa da shi ba yanke kamar bautar da jahilan sufaye suke yi da alolin wasa na rawa da tafi da rera waka, da nau’ikan kayan kida da makamantansu na daga abubuwan da suke a cikinsu akwai koyi da aikin wadanda


Allah madaukaki ya fada a kansu “ kuma sallarsu a wurin ‘Dakin ba ta kasance ba face fito da tafi.


Na biyu: yin ibada da abin da asalinsa abin shara’antawa ne sai dai kuma an sanya shi ba’a muhallinsa ba kamar bude kai a misali, shi a lokacin da ake cikin ihrami ibada ce, to idan wanda ba muharrami ba ya aikata shi a cikin Azimi ko a cikin Salla ko a waninsu da niyyar yin ibada ya kasance bidi’a haramtacciya.


Haka nan da kuma aikata sauran ibadu ababan shara’antawa a inda ba’a shara’nta ayi su acikinsa ba, kamar sallolin nafila a cikin lokutan hani da kuma azimtar ranar shakku, da azimtar idi biyu da makamantan wadannan.


Halayen bidi’a tare da ibadar da ta afku a cikinta


Nawa ne halayen bidi’a tare da ibadar da ta afku a cikinta?


Tana da halaye biyu


Ta farko: ta bata ta baki dayanta Kamar wanda ya kara a cikin sallar asubahi raka’a ta uku ko a cikin magariba ya kara ta hudu cikin wacce take hudu ya kara ta biyar da gangan, haka nan cewa idan ya rage misalign hakan.


Hali na biyu: cewa bidi’ar ta baci ita kadai, kamar inda take batatta kuma aikin da ta afku a cikinsa ya kubuta kamar wanda ya kara a cikin alwala abisa wanki uku to lalle Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi bai c eta baci ba bari dai ya ce wanda ya kara a kan haka to hakika ya munana kuma ketara haddi kuma ya yi zalunci


Bidi’o’I a cikin mu’amaloli



Posts na kwanan nan

FALALAR AZUMIN KWANA ...

FALALAR AZUMIN KWANA SHIDA SHAWAL

TAKAITACCEN BAYANI MA ...

TAKAITACCEN BAYANI MAI ANFANI GA SABON SHIGA MUSULUNC

ZIKIRAI WADANDA AKE Y ...

ZIKIRAI WADANDA AKE YIN SU DA SAFE DA KUMA YAMMA

BIDI’AR ‘YAN SHI’A A ...

BIDI’AR ‘YAN SHI’A A RANAR ASHURA