Labarai

5. Manzon Allah s.a.w yana bayyana soyayyar sa ga


iyalan sa:


Ya kasance manzon Allah s.a.w baya samun nauyi a zuciya


wurin bayyana soyayyar sa ga iyalan sa hasalima ya dauki


hakan cikin kyawawan dabi'u da kuma kyautata zaman takewa


da tarayya, kuma musamman ma kasancewar an aiko shi cikin 


al'ummar jahilai wanda basa ganin mace da wani kima, Aisha


Allah ya kara mata yarda tana cewa:


“ banyi kishi ba akan matan manzon Allah s.a.w sai akan


Khadija kawai kuma ban risketa ta mutu gabanin manzon


Allah s.a.w ya aure ni. Sai tace: manzon Allah s.a.w ya


kasance idan ya yanka akuya sai yace: ko aika ta zuwa ga


kawayen Khadija. Sai tace: sai wata rana kishinta ya


kamani sai nace: Khadija kuma?!! Sai manzon Allah s.a.w


yace: “ lallai ni an azurtani da soyayyanta ” muslim ne ya


rawaito shi.


An kuma karbo daga Aisha Allah ya kara mata yarda tace:


“ manzon Allah s.a.w ya kasance idan aka abmaci kahdija sai


ya yabeta ya kuma kyautata yabon nata sai tace: sai wata rana


kishin hakan ya kama ni sai nace ya naga kana yawan


anbatonta ne bayan Allah ya canza maka ita da wacce tafita


alheri! Sai yace: “ Allah be canzamun da wacce tafita alheri


ba: hakika tayi imani dani a lokacin da mutane suka


kafurta dani kuma ta gasgatani a lokacin da mutane suka


karyata ni, kuma ta yalwatani da dukiyar ta a lokacin da


mutane suka hanani nasu, kuma Allah ya azurtani da yaro


daga dagare a lokacin daya hanani yara daga sauran mata


” Ahmad ne ya rawaito shi, kuma shu'aibu al arnu'ut yace:


wannan hadisi ne ingantacce kuma silsilan sa ingantacce ne


cikin littafin mutabi'at.


6. Manzon Allah s.a.w yana tsabta domin kyautata


zama na auratayya:


Karantarwan musulunci yana nuni akan cewa Allah madaukaki


me kyau ne kuma yana son kwalliya kuma me karamci ne da


kyauta kuma yana son masu karamci da kyauta, me tsabta ne


kuma yana son masu tsabta kamar yadda manzon Allah s.a.w


ya bada labari kuma wannan umurni ne ga musulmi ya kasance


cikin yanayi me kyau da shiga me kyau tare da mutane 


musamman ga iyalin sa, saboda haka ne manzon Allah s.a.w


yayi umurni da himmatuwa da wannan bangare kuma ya


jaddada hakan:


“ idan dayanku ya kusanci iyalin sa kuma yana so ya koma


to yayi alwalla ” Muslim ne ya rawaito shi.


Ya kuma kara fadi har wayau: “ wannan shi yafi tsabta da


tsari da kuma tsarki ” abu dawud ne ya rawaito shi kuma


albani ya inganta shi.


7. Manzon Allah yana musayar soyayya da iyalin sa:


Lallai soyayya ta hakika ita cw wadda take lizimtar mutum


cikin dukkanin halinsa baya canzawa cikin wani lokaci kuma


wannan shine halin manzon Allah s.a.w tare da iyalin sa yadda


Aisha Allah ya kara mata yarda take cewa:


“ na ksance ina wanka tare da manzon Allah s.a.w cikin


kwarya daya, dukkanin mu muna da janaba. Ya kasance


yana umurtata dana daura zani daga kirjina zuwa gwewata


sai yayi wasa dani na debe sha'awa ina cikin al'ada. Kuma


ya kasance yana fitomun da kansa ya mikomun yana cikin


ittikafi na wanke masa ina cikin al'ada ta ” buhari ne ya


rawaito shi.


8. Manzon Allah s.a.w baya yada sirrin iyalan sa:


Lallai alaka ta aure da abunda ke cikin ta sirri ne cikin sirrori


wanda musulunci ya tsananta akan kiyaye su da kuma rashin


yada su musamman ma irin wanda babu kunya a cikin jin su


kuma tana tafiyar da mutuncin mutum, manzon Allah s.a.w


yana cewa:


“ lallai daga cikin mafiya sharrin mutane a wurin Allah


ranan alkiyama shine mutumin da yake kwanciya da matar


sa sai yazo ya yada sirrin ta ” muslim ne ya rawaito shi.


9. Manzon Allah s.a.w yana magana ta soyayya da ban


mamaki ga matan sa:


Hakika manzon Allah s.a.w ya kasance me saukin hali ne me


kyauwun siffa ne yana jiyar da iyalan sa magana wacce take


nuna soyayya da tausayi kuma yana kiran ko wanne daga cikin


su da abunda yake so na sunaye ya kasance yana kiran Aisha


Allah ya kara mata yarda da suna:


“ yake iyar fara ” kuma ya kaiwa matuka wurin tausasa masu


magana na soyayya ya wani lokaci kuma ya kankanta sunan su


domin ya bayyana masu abunda zuciyar sa yake masu suna


dashi na soyayya sai yace “ yake iyar Aisha… ” Muslim ne ya


rawaito shi.


10. Manzon Allah s.a.w yana kusantar iyalan sa hatta a


lokacin uziri na shari'a:


Hatta a lokacin uziri na shari'a ga iyalan say a kasance yana


zama dasu kuma yaci abinci tare dasu da shan ruwa da kuma


wasa dasu na debe sha'awa ba tare dayin jima'i dasu ba domin


ya kosar da raunin zuciyar su kuma ya bayyana hukunce


hukunce na shari'a cikin irin wannan matsaloli, da kuma abunda


ya halatta ga miji tare iyalin sa da kuma abunda zayyi daidai da


halinta da yanayin ta, wanda yake sabanin karantarwa da kuma


shari'a na littafi me tsarki na kiristoci wacce take mace me


al'ada a matsayin najasa kuma tana umurtan miji da nisantar


matanshi a halin uziri na shari'a (ka duba cikin littafin safar


allaween 15:19), Aisha uwar muminai Allah ya kara mata yarda


tana cewa:


“ manzon Allah s.a.w ya kasance yana wasa da ita na debe


kewa a cikin rigan ciki na mutum ina cikin al'ada, sai dai


kuma shi yafi ku mallakar kansa cikin halin da kame kansa


” baihaqi ne ya rawaito shi.


11. Manzon Allah s.a.w ya kasance yana kiyaye yanayi


na damuwar iyalan sa:


Bukatar mace ga namiji da kuma bukatar maniji ga mace abune


na fidira kuma dawwamamme bawai abu bane na dan lokaci 


kamar sauran halittu na daban wanda suke da wani lokata


wanda suke aure a cikin sa sai kuma a rabu kowa ya tafi


harkokin sa, kada na miji ya kaurace masu alokacin uzirin su na


shari'a ya kwana tare dasu kuma yaji dadi dasu suma suji dadi


dashi banda yin jima'a, Aisha Allah ya kara mata yarda tana


cewa:


“ manzon Allah s.a.w ya kasance yan asallar dare ni kuma


ina gefen sa kuma ina cikin al'ada na lulluba da mayafi


wanda akayishi daga sufi shima ya lullaba da gefen wannan


mayafi “ muslim ne ya rawaito shi.


12. Manzon Allah s.aw ya kasance yana debe kewa tare


da iyalan sa:


Lallai dukkanin ayyukan sa baki dayan su karantarwa ne ga


al'ummar sa da kuma bayanin hukunce hukunce na fiqihu


wanda acikin su mutanen sa zasu iya aiwatar da rayuwan su na


addini, was an da yakeyi da iyan san a debe kewa a lokacin


al'adar su da bacci tare dasu yana nuni ne ga hakan a shari'an ce


na bayanin tsarkin jikin mace da kuma tsarkin wurinta da


halaccin bacci tare da ita cikin bargo daya da sauran sun a


hukunce hukunce wanda za'a ciro daga cikin wannan aiki nasa,


Aisha Allah ya kara mata yarda tana cewa:


“ manzon Allah s.a.w ya kasance yana kishin gida akan


kirjina ina al'ada ya karanta alkur'ani ” Muslim ne ya


rawaito shi.


13. Manzon Allah s.a.w yana wanka da iyalin sa:


Lallai manzon Allah s.a.w ya kasance me kwadayin shigar da


farin ciki ga zuciyar iyalan sa cikin dukkanin yanayi hatta a


bayan gama jima'I wanda mafiya yawan lokuta mutum yana


kasancewa ne a cikin su karancin nishadi na jikin sa da kuma


rashin karfi na jiki da sanyi manzon Allah s.a.w ya kasance yan


awanka tare da iyalin sa kuma harda wasa da zaulaya a lokacin


wankan, Aisha Allah ya kara mata yarda tana cewa: 


“ na kasance ina wanka ni da manzon Allah s.a.w cikin


kwarya daya, muna rigangeniya wani lokaci na rigashi


wani lokaci ya rigani ta fuskan wasa, har yace a cikin wasa:


ki ragemun ruwan. Nima nace: ka ragemun ruwan ” nisa'i


ne ya rawaito shi kuma albani ya ingantashi.


14. Manzon Allah s.a.w yana sunbatar iyalin sa:


Debe kewa lamuni ne ga ci gaban rayuwan ma'aurata bayan


gam da katar din Allah kuma da biyan dukkanin abunda yake


fado mata ta hanyar wasa yan kadan da kuma magana yar


kadan zaka samu soyayyar iyalin ka kuma zaka kashe mata


kishin ruwan ta na damuwa kuma ka zama dalili na tabbatan


kwanciyar hankalin su hakika manzon Allah s.a.w ya kasance


yana lura da wannan bangare dan karami baya mantawa dashi,


Aisha Allah ya kara mata yarda tana cewa: “ manzon Allah


yazo zai sunbace ni sai nace masa ina azumi fa sai yacemun


ai nima ina azumin sai ya sun bace ni. Nisa'i da Ahmad da


Ibn kuzaima ne suka rawaito shi kuma hadisi ne ingantacce.


• Manzon Allah s.a.w tare da iyalan sa ta


bangaren dan adamtaka:


• Manzon Allah s.a.w mutum ne kamar sauran mutane an


bashi falala ne akan mutane da annabta ya kuma samu daukaka


ne akan su da isar da sako kuma an aiko shi zuwa garesu domin


ya fitar dasu daga bautan bayi zuwa bautan Ubangijin bayi


kuma ya sanar dasu shari'ar Allah wannan falala ce ta Allah


wanda yake ba wanda yaso cikin bayin sa saboda fadin sa


madaukaki:


“ kace masu ni ba komai bane face mutum irin ku anyi


mani wahayi cewa Allahn ku shi daya ne duk wanda yake


kwadayin haduwa da ubangijin sa sai ya aikata ayyuka na


kwarai kuma kada ya hada Allah dawani cikin ibadar sa ”


suratul kahafi ayata 110.


• Bashi da wani siffa na allantaka besan gaibu ba kuma


baya amfanar wa baya kuma cutarwa kuma baya juya komai


cikin duniyan nan, Allah madaukaki yana cewa akan sa:


“ kace masu bana mallakawa kaina amfani ko kuma


cutarwa sai abunda Allah yaso kuma da ace nasan gaibu da


ban yawaita aikata alheri kuma da wani mummunan abu


be same nib a nib a komai bane face me gargadi da bishara


ga mutane muminai ” suratul a'araf ayata 188.


• Duk da falalar sa da daukakan sa da kuma matsayin sa


da darajar daya samu da sakon annabta yana kin a wuce gona


da iri akan yabon sa ko kuma a kaishi matsayi wanda ba


matsayin bawa ba ga Allah wanda Allah ya zaban masa shi


domin girmamashi da ita, manzon Allah s.a.w yana cewa:


“ kada ku rika kurantani kamar yadda kiristoci suka


koranta dan maryan, lallai ni bawa ne, dan haka kuce:


bawan Allah kuma manzon sa ” buhari ne ya rawaito shi.


• Siffofin sa na mutum ne dukanin abunda ke gudana akan


mutane ya gudana masa masu bijirowa, shi bame dawwama


bane cikin wannan duniya, Allah madaukaki yace akan sa:


“ Muhammadu be kasance ba face manzo wanda manzanni


sun gabata gabanin sa yanzu shin idan yam utu ko kuma


aka kashe shi zaku juya akan duga duganku ne? duk


wanda ya juya akan duga dugan sa to bazai cutar da Allah


ba da komai kuma da sannu Allah zai sakama masu godiya


” suratu al'imran ayata 144.


• Abunda yake samun su na cuta da rashin lafiya shima


yana samun sa yana rashin lafiya da cuta kuma yana neman


magani, Abdullahi dan mas'ud yana cewa:


“ na shiga wurin manzon Allah s.a.w yana zazzabi sai nace:


ya manzon Allah kana zazzabi ne me zafi? Sai yace: “ eh


mana ina zazzabi kamar yadda wanin ku yake yi ” sai nace:


hakan kana da lada biyu kenan? Sai yace: eh kwarai haka


ne, babu wani musulmi wanda wata cuta zata same shi na 


kaya ne zuwa saman ta face Allah ya kankare masa


zunuban sa dashi kamar yadda bishaya take kankare


ganyen ta ” buhari ne ya rawaito shi.


Abin nufi cikin wannan hadisi wanda ya gabata cikin fadin sa


cewa: hakan kanada lada biyu kenan? Ma'anar hakan zai fito


fili ne cikin hadisi me girma wanda Sa'ad dan Abi waqqas


Allah ya kara masa yarda yace: “ nace ya manzon Allah


wanene yafi mutane girman bala'i sai yace “ annabawa sai


wanda suke biye masu a wurin imani haka har zuwa kasa


ana rajabtan mutum ne gwargwaon addinin sa idan


addinin sa ya kasance tsantsa to bala'in sa zaifi tsanani idan


kuma akwai tauni a cikin addinin sa za'a jarabe sa ne


gwargwadon addinin sa kamar yadda bala'i yake wanke


bawa har sai ya barshi yana tafiya a kasa bashi da zunubi


ko daya ” “ hadisi ne ingantacce Tirmizi ne ya rawato shi.


• Yana so kuma yana ki, Umar dan kaddab yana cewa


wani mutum yazo wurin manzon Allah s.a.w sai yace:


“ bani da abunda zan baka amma ka dan nemo bashi har


na samu abunda zan baka ” sai Umar dan kaddab yace: ya


manzon Allah baka mahaifi na da mahaifiyata fansa


agareka Allah be daura maka wannan b aka bashi abunda


kake dashi idan baka da komai kada ka daurama kanka sai


yace: sai manzon Allah s.a.w yaki maganar, sai Umar yace:


idan yayi fushi kuma ana gane hakan daga fuskar sa sai


wani mutum ya mike cikin mutanen madina yace: na bada


mahaifin ada mahaifiyana fansa a gareka ya manzon Allah


ka bayar kada kaji tsoron takaitawa domin wani me mulki


sai yace: sai manzon Allah s.a.w yayi murmushi yace: “ da


wannan ne aka umurce ni ” dabari ne ya rawaito hadisin cikin


littafin tahazib da kuma Barraz cikin littafin san a sanadi.


• Yana murna kuma yana bakin ciki, a lokacin da yaron sa


Ibrahim ya rasu sai manzon Allah yayi kuka sai me ta'aziyya


yace masa: 


“ kodai Abubakr ko Umar lallai kaine mafi cancantan


wanda Allah ya girmama hakkin sa sai manzon Allah s.aw


yace: “ lallai idanu sunayin hawaye kuma zuciya tana bakin


ciki amma bazamu fadi abunda zai fusata Ubangijin mu ba


badan yayi alkawari na gaskiya ba da kuma lokaci na taro


kuma lallai karshe yana bin na farko ne da mun samu akan


ya Ibrahim mafificin abunda muka samu kuma lallai muna


bakin ciki dakai ” Ibn majjah ne ya rawaito shi kuma albani ya


ingantashi.


• Yana dariya kuma yana kuka, Usama dan zaid yace wani


yaro na daya daga cikin yaran manzon Allah s.a.w mata ya


rasu, sai ta aika masa domin yazo mata, sai ya aiko mata:


“ lallai ga abun ya Allah ya amsa nashi ne kuma abunda ya


bayar nashi ne kuma dukkan komai a wurin sa yana


kasancewa ne zuwa wani lokaci sananne kiyi hakuri kuma


jure ” .


Sai ta aiko masa tayi masa rantsuwa sai manzon Allah s.a.w


ya tashi sai na mike nima nabishi da mu'azu dan jabal da


ubayyu dan ka'ab da ubadata dan samit a lokacin da muka


shiga sai manzon Allah s.a.w ya dauki yaron ransa yana


jijjiga da motsi a cikin zuciyar sa sai yace: ran ya fita sai


manzon Allah s.a.w yayi kuka sai ubada dan samit yace


masa: menene wannan ya manzon Allah? Sai yace: “


rahama ce wanda Allah ya sanya cikin zukatan dan adam


kuma lallai Allah yanayin rahama ne ga bayin sa musu jin


tausayi ” buhari da muslim ne suka rawaito shi da kuma Ibn


majjah kuma lafazin nashi ne.


• Yana farin ciki kuma yana jin radadi , a lokacin da jafar


yazo gun manzon Allah s.a.w daga kasan habasha, sai idanun


manzon Allah suka gashi sai yace: “ bansan da zuwan jafar


ba shin dashi ne zanyi farin ciki ko kuma da bude garin


khaibara? ” hakan sai yayi daidai da bude garin khaibara.


Silsilatul sahiha.


• Yana rafkana kuma yana mantuwa, hakika yayi


mantuwa cikin sallar sa kuma aka tunatar dashi, Abdullahi dan


Umar yana cewa:


“ manzon Allah s.a.w yayi mana sallah cikin daya daga


sallar azahar ko kuma la'asar raka'a biyu sai zul yadaini


yace: ya manzon Allah ka manta ne ko kuma an rage


raka'ar sallar ne? sai yace: “ banyi mantuwa ba kuma ba'a


rage raka'ar sallar ba ” . Sai yace: ai raka'a biyu kayi, sai


ya juyo ya kalli mutane yace: “ shin abunda zul yadaini ya


fada haka ne? ” sai suka ce: eh haka ne, sai ya mike ya ciko


raka'a biyun sa'annan yayi sujjada biyu na rafkanuwa ”


buhari ne ya rawaito shi.


• Kuma ba ma'asumi bane cikin mu'amular sa da ijtihadin


san a mutum ta yadda yana dacewa yana kuma yin kuskure, sai


dai ma'asumi ne cikin abunda yake isarwa na wahayi akan


Allah, hakika manzon Allah ya wuce wurin bishiyan dabino sai


yaga mutane suna barbarian dabino, sai yace:


“ menene haka suke aikatawa? ” sai sukace suna daukan


namiji ne su hadashi da mace, sai yace: “ bana tunanin


hakan yana amfanar da wani abu ” sai hakan ya isa zuwa


garesu, sai suka daina aikata hakan, sai dabinon su ya


lalace suka sanar da manzon Allah s.a.w sai yace: “ ai


tsammani ne, idan yana amfanar da wani abu ku aikata, ni


mutum ne irin ku, kuma me zato yana dace wa kuma


yanayin kuskure, sai dai bance maku Allah yace ba, saboda


bazanyi karya ga Allah ba ” muslim ne ya rawaito shi.


• Manzon Allah s.a.w yana tsayawa a matsayin mutum


cikin mu'amalar sa da mutane, yadda yake cewa:


“ ya Allah! Lallai Muhammad mutum ne yana fushi kamar


yadda mutane ke fushikuma lallai na rike alkawari agunka


wanda baka sabamun shi ba, duk wani muminin da na


cutar dashi ko kuma na zage shi ko na duke shi kasanya


hakan ya zama kaffara ce a gareshi da kuma kusanci 


wanda zaka kusanto shi zuwa gareka dashi rana alkiyama ”


muslim ne ya rawaito shi.


• Kuma mutum ne cikin hukuncin sa dayake masu da


kuma akan sa, yadda yake cewa:


“ lallai ni mutum ne kuma kuna kawomun sa'in san ku na


maku hukunci, me yuwa wasu sufi wasu karfin hujja sai na


bashi gaskiya na hukunta mashi wannan abu gwargwadon


abunda naji, to duk wanda ya bashi hakkin dan uwan sa


kada ya amsa saboda yanki ne na wuta nabashi ” buhari ne


ya rawaito shi.


• Kuma mutum ne cikin rayuwan sa na al'umma yana aure


kuma yanason zuriya kmaar yadda sauran annabawa suke


wanda suka gabace shi, Alah madaukaki yana cewa:


“ hakika mun aika da manzanni gabanin ka kuma mun


sanya masu mata da zurriyya, kuma babu wani manzo da


zai iya zuwa da wata aya sai da izinin Allah, ko wani ajali


an rubuta shi cikin littafi ” suratul ra'ad ayata 38.


• Kuma a wannan gabar zamu kawo wasu bangarori na


mu'amalar sa a matsayin mutum da iyalan sa:


1. Manzon Allah me karamci yana yin yafiya game da


kurakuran iyalan sa:


Kishi dabi'a ce ta mutum manzon Allah s.a.w ya kasance yana


tunkaran sa daga iyalan sa da budaddiyar zuciya annan kuma ya


magance shi da hikima da kuma hakuri, Anas Allah ya kara


masa yarda yana cewa: manzon Allah s.a.w ya kasance a


wurin daya daga cikin matan sa, sai daya daga cikin su ta


aika masa da kwano da abinci aciki, wai matar dayake


gunta ta bigi hannun dan sakon sai wannan kwano ya fadi


ya fashe, sai manzon Allah s.a.w ya tattara shi sai ya fara


tattara abincin cikin kwanon yana cewa: (mahaifiyar ku


tana kishi) sa'annan ya tsayar da wannan dan sako har sai


da aka kawo sabon kwano irin wannan wanda yake gidan


wannan mata inda yake, sai yaba wannan dan sakon 


wannan kwanon me kyau ya rike wannan wanda ya fashe a


wannan gidan wacce ta fasa. Buhari ne ya rawaito shi.


2. Manzon Allah me karamci ya kasance yana cika


alakwari ga iyalan sa:


Cika alkawari da kiyaye soyayya da kuma rashin inkarin me


kyau sifface wacce take nuna akan asalin me ita da kuma


kyauwun halayen sa hakika manzon Allah s.a.w ya kasance:


“ idan aka ambaci Khadija sai ya yabe ta kuma ya kyautata


yabon ta, sai yace: wata rana sai kishi ya kamani akan sai


nace me yasa kake yawan ambaton me jan haba bayan


Allah ya canza maka da wacce ta fita alheri. Sai yace Allah


be canzamun ba da wanda tafita alheri ba hakika tayi


imani dani a lokacin da mutane suka kafurce mun kuma ta


gasgatani a lokacin da mutane suka karyta ni, kuma ta


yalwatamun da dukiyar ta a lokacin da suka haramtamun


dukiyar su kuma Allah ya azurtani da yaronta a lokacin


daya haramtamun yaron sauran mata. Bayanin ingancin


hadisin ya gabata a baya.


3. Manzon Allah s.a.w yayi mu'ama me kokoluwan


kyau da iyalan sa:


Cikin rayuwan sa baki daya tun gabanin bashi annabta zuwa


bayan bashi annabta ba'a taba hakaitowa ba cewa ya daga


hannun sa masu albarka ya duki mace wannan kenan mu'amalar


sa da jama'an gari yaya kake gani to zai kasance tare da iyalan


sa kuma mun sani cewa gidan ma'aurata dai baka raba shi da


yar matsala kuma gidan manzon Allah s.a.w irin haka ne shima


bawai ya sabama asali bane amma kasancewar be taba dukan


daya daga cikin matar sa ba ko kuma ya fada mata magana


mara dadi Aisha Allaha ya kara mata yarda tace:


“ manzon Allah be taba dukan wata mace ba ko sau daya ”


sahihu Ibn hibban da baihaqi da nasa'I ne suka rawaito shi.


Kuma Aisha ta kara fadi har wayau Allah ya kara mata yarda: “


be taba dukan wani dan aiki ba ko sau daya ko kuma wata


mace, kuma manzon Allah be taba dukan wani abu ba da


hannun sa ko sau daya sai dai yayi jihadi domin Allah,


kuma ba'a taba bashi zabi ba tsakanin abu biyu face ya


zabi wanda yafi sauki daga cikin su matukar bas abo bane


hakan, idan hakan ya kasance sabo ne to ya kasance wanda


yafi koma nisantar haka, kuma manzon Allah s.a.w be taba


daukan fansa ba akan laifin da akayi mashi a karon kansa


sai dai idan an keta hurumin Allah madaukaki sai ya dau


fansa akan hakan ” silsilatul sahiha.


Taya hakan bazai faru ba bayan shine wanda aka aiko shi


rahama ga talikai, wannan Sahal ne dan Sa'ad yana cewa: “


naga manzon Allah s.a.w a lokacin da aka karya masa


hakoran sa na gaba da ji masa rauni a fuska aka kuma


karya kariyan da yasa akai, lallai nasan wanda ya wanke


masa jinin fuskan sa, da wanda yake zuba masa ruwa da


abunda da aka sanya masa a raunin har jinin ya tsaya,


fadima diyar manzon Allah s.a.w ta kasance tana wanke


jinin fuskan sa Aliyu kuma yana zuba mata ruwa, bayan ta


wanke jinin fuskan mahaifinta sai ta kona ciyawa bayan ya


zama toka sai ta dauka wannan toka ta sanya masa a


fuskan say a tsayar da wannan jini, sa'annan yace: a


wannan rana fushin Allah ya tsananta akan mutanen da


suka jima fuskan manzon Allah s.a.w rauni, sa'annan ya


zauna na tsawan awa daya, sai yace: ya Allah ya gafartawa


mutane na lallai basu sani bane ” silsilatul sahiha.


4. Manzon Allah s.a.w yana tausayin iyalan sa:


Manzon Allah s.a.w ya kasance mijin mata tara wanda yake da


dalilai da kuma abunda ya sanya shi hakan daga cikin dalilan


hakan shine rahama da tausayi da kuma sanin da aka masa da


kyautatawa ga wanda yayi imani dashi ya kuma bishi ya kuma 


hadu da cutarwa ta sanadiyyar haka daga cikin irin wannan


dalili ne yasa ya aure Saudat diyar zam'ata Allah ya kara mata


tana da shekaru hamsin da biyar a lokacin kuma hakika


mutanen makka sunyi mamaki akan wannan aure saboda bata


kasance ba tanada kyau ko kuma wani abunda da maza suke so


ba tare da ita kuma tana da yara biyar amma tausayin sa na


mutum ya sanya tausayama halin ta, da kuma tausayi akanta da


karramata da kuma dauke mata hatsarin dake biye da ita na


dawowan ta daga habasha da kuma rasuwan mijin ta, manzon


Allah yaso ya sake ta bayan wasu lokuta masu yawa saboda


tausayin dayake yi nata na ganin kada ya daura mata nauyi na


rayuwan aure wanda bazata iya dauka ba amma alokacin da taji


haka sai tace manzon Allah s.a.w: kada ka sake ni ka rike, ka


sanya ranaku na ga Aisha, sai ya aikata hakan sai aya ya sauka


cewa:


“ babu laifi a garesu da suyi sulhu atsakanin su kuma sulhu


alheri ne ” saboda kwadayin da takeyi na ganin an tashe ta


cikin matan manzon Allah s.a.w ranan alkiyama ” . Tirmizi


ne ya rawaito shi kuma albani ya inganta shi.


5. Manzon Allah s.a.w da rahamar sa ga iyalan sa:


Manzon Allah s.a.w ya shiga masallaci sai yaga igiya an


daura su a tsakanin ginshikin masallaci guda biyu sai yace:


wannan igiyar kuma fa, sai sukace: igiyar Zainab ce ta


daura idan tana salla ta gaji sai ta jingina ajiki domin ta


dawo cikin nishadin ta, sai manzon Allah s.a.w yace: “ ku


kwancw ta lallai dayanku ya rika salla cikin nishadin sa


idan ya gaji sai ya zauna ” sahihu muslim da Abu dawud da


nasa'i da Ibn Hibban ne suka rawaito shi.


Addinin ne daga Allah manzon Allah bayason iyalan sa su


daurama kan su wani Ibadan da bazasu iya ba wanda hakan zai


tasirantu cikin harkokin sun a rayuwa taya hakan bazai faru ba


bayan shine me fadin ga sahabin sa wanda ya shagaltu da aikin


bauta yabar duk wani abubuwan dadin rayuwan duniya na 


halal: “ lallai idanun ka suna da hakki akan ka, kuma jikin ka


yana da hakkin akanka, kuma matar ka tanada hakki akanka,


kuma bakon ka yanada hakki akanka, kuma abokin ka yanada


hakki akanka ” hadisi ne ingantacce Nisa'i ne ya rawaito shi


kuma albani ya ingantashi.


6. Manzon Allah s.a.w yana neman yardan iyalan sa:


Hakika manzon Allah s.a.w ya kasance wanda yafi kowa hakuri


musamman ga iyalan say a kasance yanajin abunda zai bata


masa rai daga garesu sai ya kawar dakai kuma yana ganin


cutarwa daga garesu yayi hakuri da yin yafiya daga abunda


suke aikatawa na laifi matukar be sabama shari'a ba yana


tunkarar haka da murmushi wacce take kara dankon soyayya da


yafiya da tausayi, kayi nazarin wannan tsabar hakuri na manzon


Allah s.a.w ka gani akan matan sa lokacin da Aisha Allah ya


kara mata yarda ta daga muryanta akansa cikin wani magana da


suke yi a tsakanin su sai Abubakar Allah ya kara masa yarda


yaji haka sai ya shiga yana neman ta ya bugeta yace mata bazan


ina ganinki ba kina daga sautin ki ga manzon Allah s.a.w ya


kyale ki, sai manzon Allah s.a.w ya koma kareta kada ya duketa


sai Abubakar ya fita cikin fushi sai manzon Allah s.a.w yace a


lokacin da Abubakar ya fita:


“ ya kika ganni ina kareki daga wani kada yadukeki ” sai


Abubakar ya zauna na tsawon wasu kwanaki sa'anan ya


nemi izinin manzon Allah s.a.w na shigowa sai ya same su


sun sasanta sai yace masu: ku sanya ni cikin sulhun ku


kamar yadda kuka sanya ni cikin fadan ku sai manzon


Allah s.a.w yace: “ hakika mun aikata hakika mun aikata ”


Abu dawud ne ya rawaito shi.


7. Manzon Allah s.a.w yana saukakawa iyalan sa:


Ya kasance manhajin manzon Allah s.a.w na mu'amala tare da


mutane yin sauki da rangwane da tausasa masu, an karbo daga


Abu huraira Allah ya kara masa yarda yace:


“ wani bakauye ya shiga masallaci… kawai ba'a farga ba


sai akaga yana fitsari a wani bangare cikin masallaci, sai


mutane sukayi masa ca akai, sai manzon Allah s.a.w ya


hanasu yace: lallai an aiko ni ne domin saukakewa ba dan


tsanantawa ba, ku zuba bokitin ruwa akan fitsarin nasa ”


hadisi ne ingantacce Abu dawud ne ya rawaito shi.


Aisha Allah ya kara mata yarda uwar muminai tana cewa game


da saukin da tausayin manzon Allah akan iyalan sa:


“ an kawo mana kyautan abinci ni da Hafsa kuma muna


azumi sai daya daga cikin su tace ma dayar: shin zaki iya


karya azumin? Sai tace: eh, sai suka karya azumin su biyu,


sai ga manzon Allah s.a.w ya shigo sai tace mashi: ya


manzon Allah! An kawo mana kyautan abinci sai ya bamu


sha'awa muka karya azumin mu, sai yace: babu komai


akan ku, ku azumci wani rana a maimakon sa ” Ibn hibban


ne da abu dawud suka rawaito shi, albani yace: hadisi ne me


rauni, shu'aibu alarnut yace: silsilan sa ingantacce ne akan


sharadin muslim.


8. Manzon Allah s.a.w yana tausasawa wajen mu'amala


da iyansa:


Lallai daukan abinci da hannun ka zuwa bakin matar ka da


kuma bata ruwa bawai kawai aiki ne wanda yake nufin


mallakan zuciyar matar ka da kuma nuni akan kyakyawan


mu'amala tare da ita da nuna mata so bane kawai hakan sadaka


ne wanda ake baka lada akai daga Allah kuma a sanadiyyar


haka akwai kulla akala tsakanin abunda yake na duniya ne da


kuma na lahira wanda yake ci gaba da dauke kewa kuma yana


tafiyar da damuwa da kuma samarwa iyalai da natsuwa da


kwanciyar hankali, manzon Allah s.a.w yace ma Sa'ad dan abi


waqqas:


“ kuma baka ciyar da wani ciyarwa wanda kake neman


yardan Allah d ahakan face an baka lada akanta hatta 


lomar da kake sanyawa abakin iyalinka ” buhari ne ya


rawaito shi.


9. Manzon Allah baya nuna rashin kula ga iyalan sa:


Lura da yanayi dalili ne na tsabtar zuciyar mutum manzon


Allah s.a.w ya kasance yana lura da yanayin iyalan sa baya


daure fuskan sa daga labarin da suke bashi wanda ya fita daga


abunda suke so, Ammar dan yasiri Allah ya kara masa yarda


yana cewa:


“ manzon Allah s.a.w ya yada zango domin baccin karshen


dare da hutawa cikin tafiyar sa sai mutane suka sauka cikin


wani wuri da ake kira da suna aulatul jaishi tare dasu


akwai Aisha matar sa sai sarkanta ya fadi wanda aka kawo


mata daga kasar yeman sai ya tsare mutane anan wurin


domin neman wannan sarka nata har hasken alfirir ya fito


kuma mutane basu da ruwan yin alwalla sai abubakar ya


kausasa mata mata yace mata kawai kin rike mutane a


wurin nan kuma basu da ruwa sai Allah ya saukar da ayar


sauki dayin taimama da kasa sai musulmai suka tashi tare


da manzon Allah s.a.w suka shafi kasa da hannun su ba


tare da sun goge dattin ba suka shafa a fuskar su da


hannun su har zuwa kafada da kuma cikin hannun su har


zuwa hammatan su ” . Ahmad da abu dawud da nasa'I ne suka


rawaito hadisin kuma albani ya inganta shi.


10. Manzon Allah s.a.w yana kwalliya da tsabta da sanya


turare domin iyalin sa:


Lallai shiga me kyau da kamshi yana daga cikin abunda yake


dadada rai da kawo natsuwar zuciya da kuma ido ke jin dadi da


natsuwan kallon sa, Aisha Allah ya kara mata yarda tana cewa:


“ kaman ina kallon farfashi na turaren miski akan manzon


Allah s.a.w yana cikin haraman aikin hajji a cikin gashin


kansa s.a.w ” . buhari da muslim ne suka rawaito shi kuma


lafazin na buhari ne.


Kuma a lokacin da aka tambayi Aisha Allah ya kara mata


yarda cewa: dame manzon Allah s.a.w yake faraway idan


ya shiga gida wurinku? Sai tace yakasance idan ya shigo


asuwaki yake farawa dashi ” . Ahmad da abu dawud da Ibn


majjah ne suka rawaito shi kuma albani ya ingantashi.


Kuma hakika turare tsabta ya kasance dabi'ar manzon Allah


s.a.w cikin dukkanin halin sa hatta a halin baccin sa baya


kwanciya sai da tsarki da tsabta, me masa hidima Anas dan


Malik wanda ya samu daukaka da masa hidima na shekaru


goma yana cewa:


“ ban tama jin wani irin kamshi ba wanda yafi kamshin


manzon Allah s.a.w. kuma bantaba taba wani abuba me


taushi hatta Hariri wanda yakai hannun manzon Allah


s.a.w taushi ” muslim ne ya rawaito shi.


11. Manzon Allah s.a.w yana bayyana soyayyar sag a


iyalan sa:


Kunya baya zuwa sai da alheri kamar yadda manzon Allah


s.a.w ya fadi sai wanda ya kasance sababi na buye wani


al'amari cikin addinin musulmai ko kuma na rayuwan sun a


duniya, manzon Allah s.a.w ya kasance yana bayyana soyayyar


sag a iyansa domin bada tarbiyya ga mabiyan sa dan su rika


babbaya son su akan iyalan su domin daurewar soyayya da


rayuwan aure, Amru dan Aas yana cewa:


“ nazo wurin manzon Allah s.a.w sai nace masa: wani ne


kafi so cikin mutane? Sai yace: “ Aisha ” , sai nace cikin


maza fa? Sai yace: “ mahaifinta ” , sai nace sai kuma wane?


Sai yace: “ Umar ” , sai ya irga mutane sai nayi shir daga


nan ina tsoron kada ya sanyani a karshen su ” . Buhari da


musulim ne suka rawaito shi kuma lafazin na buhari ne.


12. Manzon Allah s.a.w yana tsoron wani abunda zai


cutar da iyalan sa:


Tsoro abune na dabi'ar mutum kuma abune na fidira matukar be


wuce tsoro na dabi'a ba amma abunda ya wuce hakan to ciwo


ne, kuma manzon Allah s.a.w ya kasance yana tsoron abunda


zai cutar da iyalan sa kuma yana kokarin ganin wani abun ki be


same su ba, Anas yana cewa:


“ sun fita tare da manzon Allah da Abu dalha, kuma tare


da manzon Allah akwai safiyyat wanda ya daurata a bayan


sa akan rakumi, akan hanyar su sai wannan rakumi ta


zauna sai manzon Allah s.a.w ya firgita da matar, kuma


abu dalha yace: ina tsammanin sun fadi a kasa, Sai yazo


wurin manzon Allah s.a.w yace: ya annabin Allah Allah ya


sanyani fansa a gareka, wani ya sameka? Sai yace: “ a'a


babu abunda ya same ni amma dai ka kula da matar ” sai


abu dalha ya jefa rigan sa akan fuskar matan ya nufi wurin


ta, sai ya jefa mata rigan sa, sai ta tashi, sai ya daura su


akan abun hawar sa. buhari ne ya rawaito shi.


13. Manzon Allah s.a.w yana himmatuwa akan tsarin


iyalan sa:


Manzon Allah s.a.w ya kasanc eyana son alheri ga iyalan sa


yana kuma kokari wurin kara masu alheri musamman ma


abunda zai gadar masu da yardan ubangijin talikai da kuma


kusantar dasu zuwa aljanna ya kuma nisantar dasu daga wuta


wannan shine rabon da Allah yayi bayanin sa cikin fadin sa


cewa:


“ ko wace rai sai ta dandani mutuwa kuma ana baku ladan


ku ne a ranan alkiyama duk wanda aka nisantar dashi daga


wuta aka shigar dashi aljanna to hakika ya rabauta rayuwa


duniya kuma ba komai bace face jin dadi na rudu ” suratu


al'imran ayata 185.


Manzon Allah ya kasance yana bibiyan iyalan sa da nuna masu


hanyar alheri da kuma shiryar dasu zuwa gareta, Ummu


salmata matar manzon Allah s.a.w tana cewa: manzon Allah


s.a.w ya tashi cikin dare a firgice yana cewa:


“ tsarki ya tabbata ga Allah menene abubuwan da Allah ya


saukar na dumbin rahamar sa, kuma menene ya saukar na


fitina! Wanene zai tayar da mutanen dakin sa watan iyalan


sa suyi salla, me yuwa kaga mutum cikin ni'ima a duniya


amma a lahira ya kasance cikin akasin haka ” buhari ne ya


rawaito shi.


14. Manzon Allah s.a.w baya shigo ma iyalan sa babu


sanarwa ko izini:


Manzon Allah s.a.w ya kasance yana kyamar bazata ko kuma


kishi wanda ya wuce iyaka na dabi'a kuma yanason ganin


iyalan sa cikin yanayi me kyau da kamala hakan yan afaruwa


ne domin kwadayin say a ganin ya tabbatar masu da alaka na


soyayya tare dasu, ya kasance baya zuwa masu bazata idan ya


dawo daga tafiya, dabi'ar sa shine sanar da isowar sa domin ya


kasance iyalan sa sunada lokaci me yalwa wanda zasuyi


kwalliya da tsabta da kuma shiryawa tarban sa sai yaga iyalan


sa cikin siffa me kyau da yanayi domin tabbatar da alakar


soyayya, jabir dan Abudllahi yana cewa mun kasance tare da


manzon Allah s.a.w cikin tafiya lokacin da muka kusa shigiwa


gari sai yace:


“ ku sassauta tafiyar ku domin mu isa cikin dare domin


masu gashi su gyara kuma macen da mijinta yayi tafiya ta


aske gashin jikin su ” buhari da muslim ne suka rawaito shi.


15. Manzon Allah s.a.w yana gabatar da alheri ga iyalan


sa:


An daura shi akan dabi'a na karamci da kyauta ya kasance yana


gabatar da iyalan sa akan karon kansa yana kuma basu abunda


aka kawo mashi kyauta ko kuma wanda ya samu, taya bazai


zama haka ba bayan shine me fadin cewa:


“ idan Allah yaba dayanku alheri to ya fara da kansa da


iyalan gidan sa ” dabari ya rawaito shi kuma albani ya


ingantashi.


Maganar sa bawai kawai na fatan baki bace a'a ya kasanc eyana


aiwatar da abunda da yake fadi a kasa, Anas Allah ya kara


masa yarda yana cewa:


“ Ummu sulaim ta aikeshi da kwano a ciki akwai dabino


yakaima manzon Allah s.a.w, sai ya rika debo wannan


dabino da hannun sa yana aikawa zuwa ga matan sa kuma


yana sha'awar wannan dabino ya aikata hakan sau da


dama alhali yana sha'awar abun ” Ahmad da Ibn Hibban ne


suka rawaito shi kuma albani ya inganta shi.


16. Manzon Allah s.a.w ya kasance yana Kankan dakai


ga iyalan sa:


Duk wanda ya Kankan dakan sa domin Allah, to zai daga


darajar sa da wannan kalmomi ne manzon Allah s.a.w yake


yima sahabban sa magana kuma ya kasance yana aiwatar da


haka a aikace cikin mu'amalar sa tare da mutane kuma be


haramtawa iyalan sa haka ba, maganar Anas:


“ Cikin hadisin san a dawowar su madina tare da manzon


Allah daga khaibara tare da manzon Allah s.a.w akwai


matar sa safiyya Allah ya kara mata yarda yana rike da


abayarta a bayanta, sa'annan yana tsugunawa ta taka shi


tahau kan abun hawa ” buhari ne ya rawaito shi.


17. Manzon Allah s.a.w ya kasance yana yafema iyalan


sa laifin da sukayi:


Manzon Allah s.a.w ya kasance yana daraja kishin matar sa


baya fushi idan suna kishi kuma baya kyamatar sakamakon


wannan kishin na ayyukan su sai dai yana magance hakan ne da


salo na daki daki wanda yake nuni akan kwarewa da kuma


hikima, Anas dan Malik yana cewa:


“ manzon Allah s.a.w ya kasance a dakin daya daga cikin


matar sa sai daya daga cikin su ta aiko maa da kwano da


abinci aciki sai ta bigi hannun manzon Allah s.a.w wannan


kwano ya fadi ya fashe, sai manzon Allah s.a.w hada 


wannan kwano wanda ya fashe ya fara tattara abincin yana


cewa: “ mahaifiyar ku tayi kishi kuci sai sukaci! Sai ya rike


wannan kwano anan gidan ya aikama wancen matar da


kwanon wannan gidan me kyau ita kuma ya bata wannan


kwanon data fasa ya zama nata ” buhari ne ya rawaito shi.


18. Manon Allah s.a.w yana sanin labarin zuci wanda


iyalan sa ke ciki:


Saukin sa ta kula da kuma aikin say a sanya manzon Allah


s.a.w yana jin damuwar iyalan sa kuma yana jin abunda sukeji


sai ya tare abunda yake mara kyau aciki da lafiya da hakuri,


Aisha uwar muminai Allah ya taka mata tarda tace manzon


Allah s.a.w yace mata:


“ ni ina sanin idan kina cikin annashwa dani, kuma idan


kina fushi dani shima nasani ” sai tace: sai nace taya kasan


haka? Sai yace: “ idan kina cikin fara'a kina cewa ne: a'a


ina rantsuwa da ubangijin Muhammad, amma kuma idan


kina cikin fushi cewa kikeyi: a'a ina rantsuwa da ubangijin


Ibrahim ” , sai tace: sai nace kwarai kuma wallahi haka ne


ya manzon Allah bana kaurace maka sai sunan ka kawai ”


buhari ne ya rawaito shi.


19. Manzon Allah s.a.w ya kasance yana adalci a


tsakanin iyalan sa:


Hakika adalcin sa tare da iyalan sa yakai kololuwa ya kasance


yana masu adalci cikin dukkanin al'amuran sa cikin tafiyar sa


da lokacin da yake gida, Aisha Allah ya kara mata yarda tace:


“ manzon Allah s.a.w ya kasance baya fifita wasun mu akan


wasu wurin raba kwana kuma ya kasance cikin ko wani


rana yana kewaya mu sai tsuguwa har sai ya koma zuwa


dakin wacce yake wurin ta… ” abu dawud ne ya rawaito shi


kuma albani ya inganta shi.


Kuma baya sakace ina bada mahaifiyata da mahaifina fansa a


gareshi wurin yin adalci wanda Allah ya halicce sa akan haka 


hatta a lokacin rashin lafiyar sa, Aisha Allah ya kara mata yarda


tana cewa:


“ lallai manzon Allah a lokacin rashin lafiyar sa wanda


mutuwa yazo masa aciki, yana cewa: “ a ina nake gobe, a


ina nake gobe ” yana son yaji ance dakin Aisha, sai matan


sa suka masa izini daya zauna a inda yake so, sai ya


kasance a gidan Aisha har mutuwa yazo mashi anan ”


buhari ne ya rawaito shi.


• Manzon Allah s.a.w ta bangaren


zamantakewa da iyalan sa.


1. Mazon Allah s.a.w ya kasance me sauki da tausayi ga


iyalan sa:


Sauki be taba shiga cikin wani abu ba face ya daga darajarsa


kuma sauki be taba fita daga cikin wani abu ba face sai abun ya


lalace, karantarwan manzon Allah me daraja wanda ya


tarbiyyanci mutanen sa akai, ya kasanc eme sauki cikin


dukkanin al'amuran sa yanason sauki kuma yana umurtan


iyalan sa dashi baya umurtan su kuma baya sauraro daga wurin


su kuma baya daura masu abunda zai tsananta masu, Aisha


Allah ya kara mata yarda tana cewa manzon Allah s.a.w yace


mata:


“ ya Aisha ki saukaka domin lallai Allah idan ya so


mutanen wani gida da alheri sai ya shigar masu da sauki ”


Ahmad ne ya rawaito shi kuma albani ya inganta shi cikin


littafin al sahiha 523.


2. Manzon Allah s.a.w ya kasance yana hidimar iyalan


sa:


Daga cikin kyawawan halayen sa ya kasance baya barin


hidimar iyalan sa da kuma tayasu wasu ayyuka, hakika an


tambayi Aisha Allah ya kara mata yarda:


“ menene manzon Allah s.a.w yake aikatawa a gidan sa? sai


tace: yana dinke takalmin sa kuma yana aikata abunda


namiji yake aikatawa agidan sa. acikin wata ruwaya kuma


tace: abunda wanin ku yake aikatawa agidan sa: yana


dinke takalmi kuma yana wanke kayansa da dinki. [buhari


ne ya rawaito shi cikin littafin adabul mufrad.


3. Manzon Allah s.a.w yana yima kansa hidima:


Kowa a cikin mu yana da lalurorin sa wanda suka shafe shi


manzon Allah s.a.w ya kasance yana ayyukan san a hidimar sa


domin saukakewa iyalan sa da kuma taimakon su, Aisha Allah


ya kara mata yarda tana cewa a lokacin da aka tambayeta:


“ menene manzon Allah yake aikatawa a gidan sa? sai tace:


ya kasance mutum ne cikin mutane yana duba kayansa ko


akwai datti, kuma yana tatsan nonon daga akuya da kan sa


da kuma yima kansa hidima ” . [Buhari ne ya rawaito shi


cikin littafin adabul mufrid].


4. Manzon Allah s.a.w yana ciyar da iyalan sa:


Kyauta da ciyarwa shi ginshiki ne wanda yake dasasu cikin


zukatan mabiyan sa yana cewa:


“ lallai Allah me karamci ne kuma yana son masu karamci


kuma me yalwa ne da kyauta yana san masu yalwata wa ”


silsilatul sahiha 1378 da 1626.


Ya kasance yana yalwatawa iyalan sa wurin ciyarwa baya masu


rowa yana cewa:


“ dinarin da ka ciyar domin daukaka Kalmar Allah da


kuma dinarin da ka ciyar wurin yanta wuya da kuma


dinarin da kayi sadaka dashi ga miskini da dinarin daka


ciyar da iyalan ka dashi, wanda yafisu lada shine wand aka


ciyar da iyalan ka dashi ” muslim ne ya rawaito shi.


Be tsaya nan ba kawai ya sanya shi hakki ne na wajibi akan


namiji ga iyalan sa a lokacin da wani sahabi ya tambaye shi 


cewa ya manzon Allah menene hakkin matan dayan mu akan


shi? Sai yace:


“ ya ciyar da ita idan yaci abinci kuma ya tufatar da ita


idan ya tufatar da kan sa ” Ahmad ne da abu dawud da nasa'I


da ibn majja suka rawaito shi kuma albani ya inganta shi.


5. Manzon Allah s.a.w yana son iyalan sa su rika


hutawa:


Ya kasance s.a.w yana neman hutun iyalan sa yana kuma aiki


wurin ganin ya tabbatar dashi musamman a halin tafiya wanda


ya kasance matattarin wahalada gajiya yana ji masu tsoron


gajiyan tafiya, Anas dan malik yana cewa: manzon Allah s.a.w


ya kasance acikin tafiya sai wani yaro yana ya fara masu waka


da sauti me kara wanda ake kira da suna Anjashata sai manzin


Allah s.a.w yace masa: “ bi a hankali ya Anjashata kada ka


karya kwalabe - anan wurin kwalabe ana nufin mata


saboda zuciyar su saurin karaya yake dashi kamar kwalba


shi yasa manzon Allah s.a.w daya ga yana sauri yace masa


yabi a hankali saboda mata kada su gaji - ” buhari ne ya


rawaito shi.


hakan saboda iyalan manzon Allah sun kasance cikin wata yar


bukka akan rakumi idan kuma ana masu waka da sauti babba


sai rakumi ta fara sauri wurin tafiya sai manzon Allah s.a.w yaji


tsoron kada wani abu ya sami iyalan sa.


6. Manzon Allah s.a.w yana hakuri da danniya akan


rikicin iyalan sa:


Manzon Allah s.a.w ya kasance yana kalubalantar rikicin iyalan


sa da tarairaya da kuma musifar su da sakin fuska da kuma


kaurace warsu da soyayya yana masu hakuri da yafiya akan


abunda suka aikata na kura kurai wanda be sabama shari'a ba


kumayawan rashin sani baya kara masa komai a gunsa face


hakuri, Umar dan kaddab Allah ya kara masa yarda yana cewa:


“ mun kasance jama’ar kuraishawa muna da rinjaye akan


mata, amma bayan mun dawo madina sai mukaga su


mutane ne wanda mata ke da rinjaye akan su, sai matan


mu suka fara daukan halayen matan madina, sai nayima


matata tsawa sai ta rika maimaitamun magana tana


kallona sai nayi inkarin haka, sai tace: me yasa kake


inkarin maimaita maka maganar dana keyi? Na rantse


matan manzon Allah s.a.w suna maimaita masa magana,


kuma wata daga cikin su tana kaurace masa na tsawon yini,


sai hakan ya fusatani na tafi wurin Hafsa nace mata: wai


dagaske ne kuna sa'in sa da manzon Allah s.a.w na tsawon


yini? Sai tace: eh, sai nace: hakika kinyi asara kuma kin


tabe, shin yanzu kin yarda da fushin Allah domin fushin


manzon sa sai ki halaka? Ki daina neman dayawa daga


wurin manzon Allah kuma ki daina maimata masa magana


kuma kada ki kaurace masa, ki rika tambayata duk abunda


kike so ” buhari ne ya rawaito shi.


7. Manzon Allah yana tabbatar da abunda iyalan sa


suke so:


Ya kasance mafi gaggawa cikin tabbatar da abunda matar sa ke


so da kuma jawo masu farin ciki hakika Aisha ta tambayi


manzon Allah s.a.w tace: ya manzon Allah dukkan matan ka


suna da sunan shagube bandani sai amnzon Allah s.a.w yace


mata:


“ zan maki sunan shagube da yaron ki Abdullahi yana


nufin dan zubair kece maman Abdullahi ” ya kasance yana


kiranta sa suna mamar Abdullahi har yam utu bata taba


haihuwa ba ” buhari ne ya frawaito shi cikin littfain adabul


mufrid kuma albani ya ingantashi.


8. Manzon Allah s.a.w yana yima iyalansa likitanci:


Mutum yanada bukata matuka da hakan da kuma lura dashi da


tashi tukuru da sha'anin sa cikin halin lafiyar sa wanda a halin


rashin lafiya da rauni yafi bukatar haka, kuma hakika manzon


Allah s.a.w ya kasance be manta da wannan bangare ba yana


bibiyan iyalan sa cikin halin rashin lafiyar su domin yi masu


likitanci da hatsarin da suke ciki da kuma girmama su, Aisha


uwar muminai Allah ya kara mata yarda tana cewa:


“ manzon Allah s.a.w ya kasance idan daya gada cikin


iyalin sa ba lafiya yana mata tofi da kula'uzzai (watan yana


karanta masu suratul ikhlasi da falaki da nasi ya tufa


masu). A lokacin daya kwanta rashin lafiyar sa ta ajali sai


ya fara yi masa tofi ajikin sa sai na tofa a hannun san a


shafa masa domin hannun sa yafi nawa albarka ” muslim ne


ya rawaito shi.


9. Manzon Allah yana nuna kula ga iyalan sa:


Duk da yawan ayyukan da yake dashi masu yawa na


shugabancin mutanen sa amma hakan baisa ya manta da iyalan


sa ba da kuma shagaltuwa da mantawa dasu ba , Umar dan


kaddab yana cewa: manzon Allah s.a.w ya kasance idan yayi


sallar asuba sai ya zauna a wurin da yayi salla mutane su zo su


zauna a gefen sa har sai rana ta fito daganan sai ya tashi ya


shiga gida wurin matan sa yabi dakin kowa cikin su daya bayan


daya yana masu sallama da masu addu'a idan ranan daya ne sai


ya zauna a dakinta. Dabarani ne ya rawaito shi cikin ausat.


10. Manzon Allah s.a.w yana shawarantan iyalan sa:


Manhajin sa da dabi'ar sa itace yin shawara cikin al'amuran sa


wanda suka shafe sa da kuma ayyukan da suka shafi jama'a ya 


kasance yana shawartan iyalan sa da amfana daga ra'ayoyin su


da hangen nesan su yana tarayya dasu har acikin al'amuran sa


shugabancin jama'a sai ya duba shawarar da tafi acikin su da


wanda tafi dacewa kafin ya yanke hukunc na karshe, an karbo


daga Urwata dan Zubair daga Mirwan dan Hakam da miswara


dan makhrama cewa sun fada masa cewa, an Ambato labarin su


a sulhul hudaibiya sunce: bayan an gama rubuta yarjejeniya


na sulhun hudaibiya sai manzon Allah s.a.w yace: yaku


mutane! Ku mike ku yanka dabbobin ku sannan kuma ku


cire ihramin ku, wallahi babu wanda ya tashi saboda abun


haushin daya kama mutane, sai manzon Allah s.a.w yace:


ku yanka dabbobin ku kuma ku cire haraman ku wallah


babu wanda ya tashi daga cikin su, ya kara maimaita


hakan har sau uku babu wanda ya tashi, sai manzon Allah


s.a.w ya tashi ya shiga wurin ummu salimata yace mata: ya


ummu salimata! Bakiga abunda ke faruwa bane ina


umurtan mutane amma sunki aikata abunda na umurce su


dashi? Sai tace masa: ya manzon Allah! Kada ka damu


dasu domin mutane lallai wani abu babba ya shiga cikin


zuciyar sun a ganin ka daura kanka akan sulhun nan,


abunda za'ayi ka fita ne ya manzon Allah! Kada kayiwa


kowa magana har sai ka yanka dabbarka sannan ka cire


haramar ka, domin mutane idan sukaga ka aikata hakan


zasu aikata da sauri, beyima kowa magana ba ya wuce aka


kawo masa hadayar say a yankata sai yayi aski, a lokacin


da mutane sukaga manzon Allah ya aikata hakan sai kowa


ya tashi ya yanka hadayar sa, wasu daga cikin su sukayi


kwal kobo wasu kuma sukayi saisaiye, sai manzon Allah


s.a.w yace: Allah ya gafartawa wanda sukayi kwal kobo, sai


wani yace: ya manzon Allah! Da wanda sukayi saisaye


suma? Sai ya ambaci masu kwal kobo sau uku sannan ya


fadi cikin na ukun da masu saisaye. Buhari ne ya rawaito shi.


11. Manzon Allah s.a.w yana neman izinin iyalan sa:


Allah me girma yayi gaskiya dayake siffata shi da cewa: “


lallai kana kan halaye na kwarai masu girma ” suratul


kalam (4).


Daga cikin girman halayen sa s.a.w be bar yin adalci ba a


tsakanin matan sa hatta a lokacin rashin lafiyar sa be bar raba


masu kwana ba sai bayan ya nemi izinin su suka amince masa


suka yafe masa hakkokin su, Aisha Allah ya kara mata yarda


tace: “ lallai manzon Allah s.a.w ya aika zuwa ga matan sa a


lokacin rashin lafiyar sa suka zo suka taro sai yace:


“ bazan iya yawo ba a tsakanin ku idan kunga zaku iyamun


izini na kasance a gun Aisha ina neman haka sai suka masa


izini da hakan ” abu dawud ne ya rawaito shi kuma albani ya


ingantashi.


12. Manzon Allah s.a.w yana son sanya farin ciki ga


iyalan sa:


Lallai sanya farin ciki da murna ga zuciyar mutane abune


wanda shari'a tayi umurni dashi kuma wannan umurnin yafi


karfi a bangaren yan uwa wanda yafi kusa haka haka, Aisha


uwar muminai Allah ya kara mata yarda tace alokacin danaga


annashawa a fuskar manzon Allah s.a.w sai nace ya manzon


Allah ka mun addu'a sai yace:


“ ya Allah ka gafartawa Aisha abunda ta aikata na zunubai


da kuma wanda zata aikata da wanda tayi a bayyane da


wanda tayi a asirce ” sai Aisha tayi dariya har dan kwalinta


ya fadi saboda dariya sai manzon Allah s.a.w yace: “


wallahi addu'ar danake yima al'ummata kenan cikin


dukkanin sallata ” ibn hibban ne da hakim suka rawaito shi,


kuma albani ya inganta shi cikin littafin “ al sahiha ” (2254).


13. Manzon Allah s.a.w yana koya ma iyalan sa ladabi:


Duk da irin wannan zaman takewa tashi na taushi da mu'amala


me sauki wada yakeyi ma iyalan sa ya kasance kuma me


hikima cikin mu'amalar sa da kuma ayyukan sa ta yadda


zamanta kewa me kyau ta kasance me amfani wurin tsara zance


idan kuma ya kasance cewa ladabtar tafi cancanta idan akwai


wani kuskure bazai yiwu ba shawo kan hakan da tsawa da


tsoratarwa da kuma hani, Aisha Allah ya kara mata yarda tace


nace ma manzon Allah s.a.w:


“ ai kaza ya isheka daga safiyya- matar manzon Allah


s.a.w- watan kaza da kaza- tana nufin! Ita gajeruwa ce- sai


manzon Allah yace: “ hakika kin fadi wata kalma wacce da


za'a cudanyata da ruwan rafi da sai ta batashi ” abu dawud


ne da tirmizi suka rawaito shi kuma albani ya inganta shi.


14. Manzon Allah s.a.w yana kyautatawa wajen magance


matsalar iyalan sa:


Salon san a magance matsala iyalan sa karkashin hukunce


hukuncen musulunci ya sanya su suna muwafaka da yarda da


ita, dan me yasa hakan ma zabai faru ba bayan yana masu


magana ne ta hankali da fasaha wanda yake magance matsala,


Anas dan malik Allah ya kara masa yarda yana cewa:


“ labari yazo kunnen safiyyat cewa Hafsat tace mata


yarinyar bayahude, sai tayi kuka, sai manzon Allah s.a.w ya


shigo ya sameta tana kuka, sai yace mata me yasa kike


kuka?! ” sai tace: Hafsat ce tace mun ni yarin yan


bayahudiya ce, sai manzon Allah s.a.w yace: “ lallai ke


yarinyar annabi ce kuma baffanki annabi kuma kina auren


annabi, to kuma dame zata maki alfari dashi?! Sa'annna 


yace: kiji tsoron Allah ya hafsa ” tirmizi ne ya rawaito shi


kuma albani ya inganta shi.


15. Manzon Allah s.a.w yana karban uzirin iyalan sa:


Kuskure dole ne musamman ma ga wanda kake zama dashi


kullum kuma karban uzri dalili ne na tsarkin zuciya da kyawun


ta wanene yafi ka kyawun zuciya ya manzon Allah, ya kasance


yana jiran Aisha sai ta bata mashi lokaci sai yace:


“ me ya rike ki ne? ” sai tace ya manzon Allah: na kasance


inajin karatun wani mutum ne wanda bantaba jin murya


me dadin nashi ba, sai manzon Allah s.a.w ya tashi yaje ya


saurare shin a dan lokaci sai ya dawo yace: “ wannan salim


ne maula abu huzaifa godiya ya tabbata ga Allah daya


sanya irin wannan cikin al'ummata ” . Bazzar ne ya rawaito


shi kuma haisimi ya kawo shi cikin littafin “ al mujamma'a ”,


kuma bazzar yace: mutanen cikin hadisin mutanen cikin littafin


sahihul buhari ne.


16. Manzon Allah s.a.w yana sanya farin ciki ga iyalan


sa:


Ya kasance yanason fadama iyalan sa abunda zai sanya su farin


ciki da murna da saukar da natsuwa da kwanciyar hankali a


cikin zukatan su, Aisha Allah ya kara mata yarda tana cewa


manzon Allah yace mata:


“ bazaki yarda ba ace kin zama matata a nan duniya da


kuma lahira? Sai tace zan yarda, sai yace: to ke matatace


anan duniya da lahira ” hakim ne ya rawaito shi cikin


mustadrak kuma albani ya inganta shi.


17. Manzon Allah s.aw ya ksance me tausasawa wurin


mu’amala da iyalan sa:


Hakika mu'amalar manzon Allah s.a.w ya kasance tare da


mutanen da suke rayuwa dashi cikin kololuwan kyawu da sauki


da tausayi da kamala kamar yadda ubangiji ya siffatashi da


hakan yace:


“ hakika kana kan halaye na kwarai masu girma ” suratul


kalam (4).


Iyalan sa sun kasance masu rabo me waya cikin haka, Aisha


Allah ya kara mata yarda tana cewa akan mu'amalar manzon


Allah s.a.w tare da ita: “ na kasance inasha ruwa cikin


kwarya ina cikin al'ada sai mikama manzon Allah sai ya


sanya bakin sa akan wurin dana sa baki na shima yasha


ruwan kuma niacin kasha ina cikin al'ada sai na mikawa


manzon Allah s.a.w yasa bakin sa a wurin dana sa baki na


shima yace ” nisa'I ne ya rawaito shi kuma ingantacce ne


hadisin.


18. Manzon Allah s.a.w ya kasance yana da saukin hali


ga ilayan sa:


Manzon Allah s.a.w ya kasance mutum ne me saukin hali da


saukin kai cikin dukkanin al'amuran sa yana amsan kuskure


koda kuwa da gangan aka aikata kuma har yayi ma mutum uziri


koda kowa daya daga cikin sahabban sa ne ko kuma makiyan


sa ne, iyalan sa ma sun kasance suna da rabo acikin yafiyan sa


me girma, ya kasance yana shiga gida wurin iyalan sa bayan


hantsi sai yace: “ shin kuna da abincin rana? ” sai suce: a'a,


sai yace: “ to ina azumi ” nasa'I ne ya rawaito shi kuma albani


ya ingantashi.


Babu tsawatarwa kuma babu kunyatarwa sai raddi wanda yake


kunshe da sauki da kuma kyauwun amsan uzirin su.


Alaka tsakanin namiji da mace a musulunci alaka ce ta soyayya


da kuma girmama wa da rahama da darajawa, soyayya ga mace


a mastayin mata da tausayi a gareta kamar yarin ce da kuma


girmamata da darajata kamar uwa, lallai mace a cikin


musulunci duk lokacin da shekarunta yaja haka darajata zai


kara da kuma girmamata, a cikin musulunci babu matsala a


tsakanin namiji d mace ko wanne daga cikin su an halice sa ne


domin dayan domin samun kamalar sa ko wanne daga cikin su


yana da siffar sa wanda ya banbanta dashi akwai siffofi na


tawaya ga namiji wanda mace take cike masa shi kuma akwai


siffofi na tawaya ga mace wanda namiji ke cike mata shi


saboda haka ne musulunci ya wajabta wa mace wasu wajibai na


shari'a da zamantake wa wanda zai dace da ita da kuma yanayin


ta na jiki ne ko kuma na zuciya kuma Kaman haka ne shima na


miji an wajabta masa irin haka, sannan kuma ya sanyawa


namiji hakkoki nashi da kuma wanda suka wajaba akan sa


wanda zai dace da dabi'ar sa haka itama mace take nata hakkoki


wanda zai dace da dabi'ar ta a karkashen wannan kwatantawan


da musulunci ya wajabta a tsakanin su ake samun natsuwa da


kwanciyar hankali da so da kauna a tsakanin su, Allah


madaukaki yana cewa



Posts na kwanan nan

FALALAR AZUMIN KWANA ...

FALALAR AZUMIN KWANA SHIDA SHAWAL

TAKAITACCEN BAYANI MA ...

TAKAITACCEN BAYANI MAI ANFANI GA SABON SHIGA MUSULUNC

ZIKIRAI WADANDA AKE Y ...

ZIKIRAI WADANDA AKE YIN SU DA SAFE DA KUMA YAMMA

BIDI’AR ‘YAN SHI’A A ...

BIDI’AR ‘YAN SHI’A A RANAR ASHURA