Labarai

Da sunan Allah me rahama me jin kai.


Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah ubangijin talikai,


tsira da amincin Allah su tabbata ga Annabi Muhammad da


iyalan sa da sahabban sa baki daya.


Kasancewar magana akan soyayya a cikin musulunci ga


mata, ya zama dole ya kasance Muhammad manzon Allah s.a.w


shine tushen wannan magana kasancewar sa manzon allah


wanda aka aiko shi zuwa ga mutune baki dayan su domin ya


karantar dasu abunda Allah ya shar'anta kuma su samu ginshiki


da dabi'un sa, shine abun koyi ga musulmai wanda ya wajaba a


garesu su bishi da kuma koyi da sunnar sa domin aiki da


umurnin Allah madaukaki wanda yake cewa:


“ hakika ya kasance kuna da abun koyi me kyau daga


manzon Allah s.w.a ga wanda ya kasance yana kwadayin


haduwa da Allah da rana ta karshe kuma ya ambaci Allah


dayawa ” suratul ahzab ayata 21.


Shine me isarwa game da Allah saboda haka ne babu


wani abu daya buya ga musulmai game da al'amuran rayuwan


sa baki daya kananan su da manyan su, ke bantaccen su da


game garin su face an sansu kuma ya shahara a tsakanin su


kuma a rawaito shi daga wannan jama'ar zuwa wata jama'ar


kasancewar maganganun sa da ayyukan sa hukunce hukunce ne


da shari'a wanda ta hanyar su ne musulmi yake sanin addinin sa


wanda yake isar dashi zuwa ga soyayyar Allah da yardan sa da


aljannar sa, Allah madaukaki yace:


“ kace masu idan kun kasance kuna son Allah to ku bini


Allah zai so ku kuma zai gafarta maku zunuban ku, Allah 


ya kasance me gafara kuma me rahama (31) ” . Surat Aal


‘Imran ayata 31


Lallai ginshikin musulunci shine soyayya wanda zata


sanyaka ta sanadiyyar ta kayi biyayya ga wanda kake so kuma


kabi umurnin sa da kuma hanuwa daga abunda ya hana , kuma


kayi kokari matukar iyawan ka na ganin ka kusance sa ta


hanyar aikata abuuwan da yake so, lallai mafi girman so da


daukaka shine son Allah madaukaki wacce ta hanyar hakan ne


ake samun damar fadakar da musulmi halaye na gari wanda zai


rabu son kai kuma ya samu daukaka da alamomin sa sai ya


yada soyayya da rahama ga halittun Allah ba tare da jiran wani


ladaba na kudi daga gare su, sai ya rabu da son kai wacce ta


ginu akan maslaha da amfanin karon kan mutum shi kadai,


daga ita kuma sai soyayyar manzon Allah s.a.w ya biyo baya


soyayya tsarkakakkiya wacce ake gabatar da ita akan son ran


mutum da dukiya da yara kasancewar sa shine sababin shiriya


da kuma nuni zuwa ga Allah da kuma addini na gari wanda


Allah ya sanya shi tsira daga wuta ga duk wanda ya bishi da


kuma shiga aljanna saboda hakane ya cancanci wannan matsayi


da daraja me girma tare kuma da ajiye shi a matsayin da Allah


ya ajiye shi watan matsayi na bauta da Kankan dakai ga Allah,


Allah madaukaki yana cewa:


“ kace idan ya kasance cewa iyayen ku da yaran ku da ‘yan


uwan ku da matayen ku da dangin ku da dukiyoyin ku


wanda kuka tara da kasuwancin ku wanda kuke tsoron


karyewan sa da kuma gidajen ku wanda suke burgeku da


son rayuwa a cikin su sunfi soyuwa a gare ku sama da Allah


da manzon sa da kuma jihadi domin daukaka addinin sa to


ku saurara ku jira har Allah yazo maku da al'amarin sa,


lallai Allah baya shiryar da mutane fasikai ” suratul taubah


ayata 24.


Duk wanda ya qudurce cewa musulunci addini ne na


tsanani da kausasawa to hakika yayi kuskure, gaskiyar itace


musulunci addini ne wanda ya kunshi komai watan ma'ana be


bar kananan abubuwa ba ko kuma manya na rayuwan musulmi


shin hakan ya shafi kudi ne ko kuma zuciya face ya fadakar da


ita fadakarwa me kyau ya kuma sanyata a wurinta daya dace,


musulunci ba addinin aqida bane da hukunce hukunce da dabi'u


bane kadai a'a addini ne kuma har wayau na soyayya ta fuskar


fahimtar sa a musulunce wanda ya kunshi komai hakan ya


tattaru cikin so da kauna da rahama da tausayi da kyautatawa


da dajara alamomi da dabi'u masu daraja da mu'amala masu


kyau ga dukkanin abunda yake kewaye da mutum cikin wannan


duniya na halittu bawai kawai ya takaitu bane akan wani


bangare guda bane wanda ya tattaru tsakanin namiji da mace na


mu'amala na magana ko kuma na aiki kawai, baya cikin


soyayya ka kasance me kyakyawan mu'amala ga wanda kakeso


kadai ba da kuma munana mu'amala ga wanin sa, saboda haka


ne zamu kawo wasu daga cikin siffofi da dabi'u na musulmi,


har mu gane ma'anar so cikin musulunci ga dukkanin wanda


yake kewaye da musulmi.


WWW.ISLAMLAND.COM


info@islamland.com


• Musulmi shine wanda mutane suka amintu dashi aminci


wanda ya kunshi komai akan rayukan su da dukiyoyin su da


mutuncin su dashi saboda fadin manzon Allah s.a.w cewa:


“ shin na baku labarin wanene mumini shine wanda


mutane suka amintu dashi akan dukiyar su da rayukan su


shi kuma musulmi shien wanda mutane suka tsire daga


harshen sa da hannun sa ” . Hadisi ne ingantacce Ahmad da


Ibn hibban ne suka rawaito shi (al sahihah) (549).


• Bawannan bane kawai musulmi shine wanda yakeson


alheri kuma yake yadashi ga mutane kuma yana aiki tukuru


domin isar dashi zuwa gare su ba tare da amsan wani hasafi ba


daga garesu akan hakan, saboda fadin sa manzon Allah s.a.w:


“ ka kiyaye abubuwan da Allah yayi umurni dasu da kuma


wanda yayi hani dasu zaka zama cikin mutane masu bauta,


ka yarda da abunda Allah ya baka zaka zama mafi arzikin


mutane kuma ka kyautata wa makwabcin ka zaka zama


mumini, kasoma mutane abunda kake soma kanka zaka


zama musulmi… ” (Ahmad da Tirmizi ne suka rawaito shi


kuma albani ya ingantashi).


• Musulmi shine wanda yake kasancewa me adalci a


kansa da kuma al'ummar sa hatta makiyan sa, baya daukan


fansa akan wani da zunubin wanin sa manzon Allah s.a.w ya


kasance idan zai tura rundunar yaki cikin musulmai zuwa ga


mushrikai wanda suka cutar dashi kuma suka fitar dashi daga


gidan sa da kuma taimakawa wasu akan fitar dashi suka kuma


kashe sahabban sa da azabtar da duk wanda yabi addinin sa


yanayin wasiyya ga shugaban wannan runduna gareshi karan


kansa da jin tsoron Allah da kuma wanda suke tare dashi cikin


musulmai da alheri. Sa'annan yace (kuyi yaki da sunan Allah


domin Allah. Ku yaki wanda ya kafurcewa Allah. Kuyi yaki 


kada ku wuce gona da iri kuma kada kuyi yaudara kuma kada


kuyi gunduwa gunduwa kuma kada ku kashe yara kanana)


(sahihu muslim)


• Musulmi shine wanda yake kiyaye mahallin da yake


kewaye dashi da dukkanin abunda ke cikinta na dabbobi, baya


yarda da azabtar da ita domin kuwa an wuce gaban manzon


Allah s.a.w da wani jaki wanda aka masa zane a fuskar sa sai


yace:


“ Shin be isa gare ku bane cewa na tsinema wanda yayi ma


dabba zane a fuskanta ko kuma ya duke ta a fuska? ” .


(Sunan Abi dawud kuma albani ya inganta shi.)


Kuma yana mu'amala da ita da tausayi da rahama, Aisha Allah


ya kara mata yarda tana cewa: “ manzon Allah s.a.w yana


karkatawa mage kwarya tasha ruwa ” . (hadisi ne


ingantacce) dayalisi ne rawaito shi kuma yana cikin littafin


sahihul jami'u 4958.


Kuma yana kiyaye abunda dake cikinta na tsuntsaye baya


tsorata su kuma baya farautan su haka kawai ba tare da wani


amfani ba, Ibn mas'ud Allah ya kara masa yarda yana cewa


mun kasance tare da manzon Allah s.a.w cikin tafiya sai ya tafi


domin biyan wata bukatar sa sai mukaga wata tsuntsuwa


karama tare da ita akwai jaririyan ta sai muka dau wannan


jaririya nata sai wannan tsuntsuwa tazo tana bude fuka fukanta


tana goga su a kasa sai manzon Allah s.a.w yazo sai yace: “


wanene ya tinzira wannan da jaririnta? Ku mayar mata da


jaririnta ” sai kuma yaga wani gidan tururuwa wanda


muka kona sai yace:


“ wanene ya kona wannan? ” sai mukace mune sai yace: “


lallai baya halatta yin azaba da wuta sai ga ubangijin wutan


” (abu dawud ne ya rawaito shi kuma albani ya inganta shi).


• Musulmi shine wanda yake kiyaye wuraren mutane da


wurin shakatawar su, baya samar da wani abu a wurin wanda 


zai hana su amfanuwa dashi ta hanyar jefar da bola a wuraren


da makamantan su, saboda faduin manzon Allah s.a.w:


“ ku kiyaye abunda suke jawo tsinuwan mutane: shine


wanda yake bayan gida a kan hanyar mutane ko kuma a


wurin inuwar su ” (abu dawud ne ya rawaito shi kuma albani


ya ingantashi).


• Hasalima musulmi shine wanda yake kawar da dukkanin


wani abu wanda yake cutar da mutane saboda fadin manzon


Allah s.a.w:


“ .. kawar da cuta daga kan hanya sadaka ce ” (abu dawud


ne ya rawaito shi kuma albani ya ingantashi).


• Musulmi shine wanda yake kiyaye abunda yake da


amfani ga muhalli da mutane kamar bishiya saboda fadin


manzon Allah s.a.w: “ kada ka sare bishiyar da take iyaiya,


kuma kada ka kashe dabbar da baka da bukatar ta, kuma


ka kiyaye cutar da mumini ” (abu dawud ne ya rawaito shi


cikin littafin “ marasil ” , da Sa'id dan Mansur cikin littafin san


a “ sunan ”).


• Musulmi shine wanda yake kira zuwa ga kiyaye muhalli


ta hanyar fadakarwa akan dasa bishiya da gyara kewayenta,


saboda fadin manzon Allah s.a.w:


“ da ace duniya zata tashi a hannun wanin ku akwai


karamin bishiyar da binu wanda ta fado daga jikin


mamanta to idan ya samu daman shukata ya shukata kafin


duniyar ta tashi ” (buhari ne ya rawaito shi).


• Musulmi shine wanda yake kiyaye ruwa baya lallatashi


ko kuma sanya masa datti da kazanta, Jabir Allah ya kara masa


yarda yana cewa:


“ manzon Allah s.a.w yayi hani da mutum yayi fitsari a


cikin ruwan da baya tafiya ” (muslim ne ya rawaito shi).


Yana kuma yin kokari wurin kiyaye ta da kuma yi mata dukkan


hidima wanda take bukata, saboda fadin manzon Allah s.a.w: 


“ musulmai suna tarayya cikin abubuwa uku: tsirrai ko


karare, da ruwa da kuma wuta ” hadisi ne ingantacce


(ahmada ne da abu dawud suka rawaito shi).


Yana kuma yin kokari iyakan iyawan sa domin kiyaye


hanyoyin samun ruwa da kuma raya su domin al'umma su


amfanu da ita da dabbobi da shuka ta hanyar rashin yin


almubazaranci da bannatar da ita ta hanyar da bashi da amfani


saboda fadin manzon Allah s.a.w ga Sa'ad lokacin daya


wuceshi yana alwalla:


“ wannan wane irin barnan ruwa ne? ” sai yace: yanzu


akwai barnan ruwa ne a cikin alwalla, sai yace: “ eh akwai


koda kuwa ka kasance ne a wurin rafi me gudana ” . (Ibn


majjah ne ya rawaito shi kuma albani ya ingantashi).


Kasancewa an umurce mu dabin Manzon Allah Muhammad


s.a.w wanda ya tattara halaye da dabi'u masu daraja na dukkafin


ma'ana wanda ya kunshi haka da mu'amala me kyau da


dukkanin abunda kewaye dashi na halittu wannan bin da koyi


ya zama aqida ga musulmi wanda yayi imani da ita kuma yake


kokarin aiwatar da ita cikin ayyukan san a rayuwan sa domin


neman yardan Allah, Allah madaukaki yace:


“ kace masu idan kun kasance kuna son Allah to ku bini


Allah zai so ku kuma zai gafarta maku zunuban ku, Allah


ya kasance me gafara ne me rahama (31) ” Surat Aal


‘Imran ayata 31


Wannan shine musulunci soyayya ga dukkanin abunda


Allah ya halitta wanda ake aiwatar dashi ta hanyar umurnin


Allah mutum kamar yadda yake raya gangan jikin sa daci da


shah aka yake raya zuciyar sa da addini wanda yake daukaka da


ita cikin duniyan falala ya kuma nisanta shi daga cikin duniyar


dabbobi da sha'awa ya kuma tace alamomin sa , a cikin wannan


littafi karami zamuyi magana akan bangare guda cikin


bangarori na soyayya cikin rayuwan manzon Allah s.a.w tare


da mata wanda aiko shi ya zama haske me kyau ga duniya baki


dayanta da kuma mata a kebance ya daukaka darajarta ya kuma


wajabta girmamata ya kuma kawar da zulumci akanta, hakika


mata sun kasance gabanin zuwan musulunci suna rayuwa ne a


mataki na can kasa yadda Umar dan kaddab Allah ya kara masa


yarda shugaban muminai kuma khalifa na biyu na manzon


Allah s.a.w ya sawwarata cikin fadin sa cewa:


“ wallahi mun kasance cikin jahiliyya bama daukan mace a


bakin komai, har zuwa lokacin da Allah ya saukar da


abunda ya yasaukar akan su ya kuma raba ya basu abun


da zai basu na gado ” . (Buhari da muslim ne suka rawaito


shi).


A lokacin da musulunci yazo fadakarwan sa akan mata ya


kaance bayyananne ya kuma bayyana cewa daga cikin mafi


alherin maza da dabi'u masu kyau shine kyautata mu'amala tare


da mata, manzon Allah s.a.w yace:


“ mafi alherin ku shine wanda yafi alheri ga mata ” (hakim


ne ya rawaito shi kuma albani ya inganta shi).


Sai mace ta rabautu da daraja me girma a karkashin


musulunci da kuma matsayi kololuwa wanda be ba maza ba


kuma wasu mata na wata al'umma na daban basu same shi ba, 


manzon Allah s.a.w ya kasance yana son mace a matsayin san a


mutum, sai manzon Allah s.a.w yace:


“ an samun son wannan abubuwan a cikin kayan duniya:


mata da turare kuma an sanya mun natsuwana da farin


cikin rayuwa na a cikin sallah ” (Ahmad da nasa'I da Baihaki


ne suka rawaito shi kuma albani ya inganta shi cikin littafin


mishkat 5261).


Soyayya wacce take zagaye da tausayi da so da tausasawa


yadda yace s.a.w:


“ ….. ina maku wasiyya na kyautatawa ga mata ” (muslim


ne ya rawaito shi).


Sannan kuma an kare mata hakkokin ta daga lalace aka kumayi


umurni da yin mu'amala dasu me kyau da karrama su da kuma


hana wulakanta su, kuma tana kiransa da yi mata taushi tare da


ita da kuma darajata, manzon Allah s.a.w yana cewa:


“ wanda yafi cikin imani cikin muminai shine wanda yafisu


kyaukyawan dabi'u, kuma zababben mu shine zababbe ga


matan sa ” Tirmizi ne ya rawaito shi, kuma yace: (hadisi ne


me kyau kuma ingantacce) kuma albani ya ingantashi.


Sai ya daurata a matsayinta wanda aka haramta mata gabanin


zuwan musulunci ya daidaita ta da maza cikin komai sai


abubuwan da shari'a ya kebance kamar gado da bada sheda da


sauran su cikin abubuwan da dalilai suka nuna akan hakan ya


sanyata ta zama abokiyar na miji kuma rabin jikin sa wanda


yake samun kamala da ita, sai manzon Allah s.a.w yace:


“ lallai mata iyan’uwan maza ne ” Ahmad da abu dawud da


tirmizi ne suka rawaito shi kuma albani ya inganta shi.


Hasalima manzon Allah s.a.w ya sanya ta cikin mafi falalar


kyautan Allah cikin wannan duniya sai yace:


“ duniya jin dadi ne kuma mafi alherin jin dadin duniya


itace mace ta gari ” muslim ne ya rawaito shi.


Ya kuma sanyata mubudin farin ciki cikin wannan duniya, sai


yace: 


“ abubuwa hudu suna cikin farin ciki, mace ta gari da


wurin zama yalwatacce da makwabci na gari da abun hawa


me lafiya ” Ibn hibban da hakim ne suka rawaito shi kuma


albani ya inganta shi cikin “ littafin al sahihah ” (282).


Ya kuma sanyata s.a.w rabin addinin mutum itace mace ta gari


wacce take sababi wurin gfadakar da mijinta fadakarwa na gari


sai yace:


“ idan mutum yayi aure to hakika ya ciki rabin addinin sa


sai yaji tsoron Allah cikin sauran rabin ” baihaki ne ya


rawaito shi kuma yana cikin sahihul jami'u: 6148.


Kuma kamar yadda manzon Allah s.a.w yaso mace a


matsayinta na mutum ya kuma so ta a matsayin uwa sai ya


wajabta girmamata da kuma wajabta mata biyayya da kuma


damuwa da kula da ita ya kuma sanya hakan cikin sababi na


shiga aljanna, hakika Jahimatu al salami yazo wurin manzon


Allah s.a.w sai yace masa:


“ ya manzon Allah nazo ne neman shawararka inason zuwa


yaki, sai yace masa: kanada mahaifiya? Sai yace: eh sai


yace: kaje ka lazimce ta domin lallai aljannarka tana


karkashin tafikan kafarta ne ”. nisa'I ne ya rawaito shi kuma


albani ya ingantashi.


Ya kuma sanyata tana gaba da namiji wurin biyayya da sada


zumunci yadda hakan ya kasance umurnin manzon Allah s.a.w


ga mutumin daya tambaye shi:


“ ya manzn Allah wanene mafi cancantan mutane ga mafi


kyawun zamana? Sai yace: mahaufiyar ka, sai yace: sai


kuma wa? Sai yace mahaifiyar ka, sai yace: sai kuma wa?


Sai yace mahaifiyar ka, sai kuma wa? Sai yace: mahaifin ka


” buhari ne ya rawaito shi.


Kamar kuma yarda manzon Allah yaso mace a matsayin uwa


ya kuma sota a matsayin mata, yadda yace ma Amru dan Aas


lokacin daya tambaye shi:


“ wanene kafi so cikin mutane? sai yace: “ Aisha ” ,sai yace


cikin maza fa? Sai yace: “ mahaifinta ” sai yace: sai kuma 


wa? Sai yace: “ Umar ” , sai ya irga maza sai nayi shiru


saboda tsoron kada yasanya ni a karshen su ” . Buhari ne ya


rawaito shi.


Kuma kamar yadda manzon Allah s.a.w yaso mace a matsayin


mata yaso ta a matsayin diya, Aisha tana cewa Allah ya kara


mata yarda:


“ bantaba ganin wani mutum ba wanda yaki kama da


manzon Allah ta wurin dattaku da kama da shiriya cikin


tsayuwarta da zamanta kamar fadima diyar manzon Allah


s.a.w sai tace: ka kasance idan ta shiga wurin manzon Allah


s.a.w sai ya tashi ya rungume ta sannan ya zaunar da ita a


wurin zaman sa kuma manzon Allah s.a.w ya kasance idan


ya shiga wurinta sai ta tashi daga wurin zamanta da


rungume shi ta zaunar dashi a wurin zamanta… ” Tirmizi


ne ya rawaito shi kuma albani ya inganta shi.


Wannan mu'amalar ta kwarai ga dukkanin mutane da kuma


mata a kebance ya samu asali ne daga fadakarwan Allah ga


dukkanin musulmai na tausayi da rangwame da tausasawa ga


mata da kuma girmama su yadda yace:


“ … kuma ku zauna dasu da kyawawan dabi'u wanda aka


sani, idan kun kyamace su to kusani fa sau dayawa kuna


kyamatar abu kuma sai Allah ya sanya masa alheri me


yawa ” surat an-nisa' ayata 19.


Ibn kasir yace cikin tafsirin wannan ayar: watan ku kyautata


maganar ku a garesu sannan kuma ku kyautata ayyukan ku da


adonku gwargwadon ikonku a garesu kamar yadda kuke son


haka daga garesu, ka aikata kwatankwacin haka a gareta, kamar


yadda Allah madaukaki yace:


“ suma suna da kwatankwacin abunda ke kan su na


kyautatawa ” . [suratul bakar ayata: 228]


Kuma hakika sahabban manzon Allah s.a.w sun kasance suna


rigegeniya wurin aiwatar da wannan manhaji da fadakarwa na 


Allah, wannan dan Abbas ne malamin wannan al'umma yana


cewa:


“ lallai na ksance ina yin kwalliya ga matata kamar yadda


takemun, kuma banason amsan hakkokina duka dake


kanta saboda kada hakkokinta dake kaina ya wajaba


akaina saboda Allah madaukaki yace: “ suma suna da


kwatankwancin abunda suke dashi akan su na kyautatawa


” [suratul bakar ayata: 228]. Qurdubi an Ambato haka cikin


littafin sa na Jami'un li ahkamul kur'an.


Lallai cefanen soyayya da kyautata mu'amala da tausayi da


hakuri da mutane shine manhajin musulmi na gari wanda yake


tafiya akan sa da kuma aiwatar dashi da aiki dashi da kuma


tallar sa domin aiwatar da umurnin Allah, wanann shugaban


Ahlussunah ne waljama'a yakeyima dansa wasiyya ranan


angoncin sa yana sanar dashi hakkokin matar sa akansa da


cewa:


“ ya kai dana ka sani fa bazaka taba samun farin ciki ba a gidan


ka sai da wannan abubuwa guda goma wanda zaka rika yima


matarka dan haka ka kiyaye su kuma ka himmatu dasu:


Na farko da na biyu:


Lallai mata suna son shiryarwa kuma suna son ka nuna masu


soyayya a bayyane, kada kayima matarka rowan wannan,


saboda idan kayi mata rowa zaka sanya shamaki ne tsakanin ka


da ita na tsanani da kuma tawayan soyayya.


Na uku kuma:


Su mata suna kyaman namiji me tsanani mara sakin fuska kuma


suna bautar da namiji me rauni da taushi saboda haka ka sanya


ko wace siffa a wajenta saboda hakan yana kawo soyayya da


natsuwar zuciya.


Na hudu:


Lallai mata suna son irin abunda miji yake so daga gare su na


kyautata magana da sura da kuma tsafta na kaya da kamshi


saboda haka ka kasance haka cikin dukkanin lokutan ka.


Na biyar:


Lallai gida mulki ne na mata kuma acikinsa ne takejin cewa


lallai ita tana da gadara da akan kujeran mulkin ta kuma ita


shugaba ce, saboda haka kashedin ka da ruguza wannan


mallaka nasu wanda take rayuwa aciki, kuma kashedin ka dayin


kokarin nesantar da ita daga wannan kujeran mulki, saboda


idan ka aikata haka ka kwace mata mulkinta, kuma babu


adawar da tafi adawa ga mutumin da zai kwace maka mulki


koda kuwa ya bayyana maka akasin haka.


Na shida:


Lallai mace tana son ta mallaki mijinta ba tare da tayi asarar


iyalanta ba, saboda haka kashedin ka da sanya kanka da


iyalanta a ma'auni daya, kodai kai ko kuma iyan’uwanta, domin


kuma koda ta zabe ka akan iyalanta to zata kasance cikin bakin


ciki wanda zai rika haifar da gaba zuwa ga rayuwan ka na


kullum.


Na bakwai:


Lallai mace an halicceta ne daga kasha karkatacce wannna


kuma shine sirrin kyau dinta, da kuma sirrin jayuwa zuwa


gareta wannan kuma ba aibu bane a gareta “ girakarkacewarta


shi ne kyawan ta ” , kada kayi kokarin daura mata kaya me


nauyi idan tayi kuskure domin kokarin gyara wannan lankwasa


nata sai ka karyata kuma karyata shine sakinta, kuma kada ka


kyaleta idan tayi kuskure sai ya kara karkacewan kuma ka


rufema kanka koma a kanta wanda bazata kara maka taushi ba


kuma bazata saurare k aba, ka kasance a koda yaushe tare da ita


a matsayin me mata bayani.


Na takwas:


Lallai mata an halicce su ne akan kafurcewa zaman takewa na


aure da kuma inkarin abun alheri, idan ka kyautatawa dayan su


na shawan shekaru sai ka saba mata na lokaci daya zatace: ban


taba ganin alheri ba a tare dakai duk zamana dakai ko sau daya 


ba saboda haka kada wannan hali ya sanya ka kyamatar ta da


nisantarta, domin idan ka kyamace wani hali daga gareta zaka


yarda da wani hali daga gareta wanda bashi ba.


Na tara:


Lallai mace tana wuce wa cikin wasu yanayi na raunin jiki da


ciwon zuciya, har Allah madaukaki ya dauke mata wasu daga


cikin wasu wajibai akanta na ibada wanda ya daura mata cikin


wannan yanayi ya dauke mata salla baki dayan sa cikin wannan


yanayi ya kuma dakatar mata da azumi a cikin su har sai ta


dawo cikin lafiyar ta yanayinta ya daidaita, dan haka ka


kasance da ita cikin wannan yanayi da tarbiyya na Allah kamar


yadda ya saukaka mata wajibobi kaima ka saukaka mata neman


tayi maka wasu abubuwa da kuma bata umurni.


Na goma:


Kasani cewa mace baiwa ce a wurin ka, ka tausayawa wannan


bauta nata kuma ka kawar dakai daga raunin ta zata kasance


maka mafi alherin abun jin dadi da abokiyar zama..


Kamar yadda maza ke cefane a tsakanin su na soyayya ta


musulunci haka suma mata musulmai suna da rabo cikin


wannan cefane a tsakanin su al'amarin kyautata zamantakewa


da mu'amala me kyau tare da miji, wannan Ummu Iyas ce diyar


Auf dan Alamul shaibani lokacin da Amru dan Hajar sarkin


kasar Kanada ya nemi auren yarinyanta daren amarcin ta yazo


sai ta kebe da ita tayi mata wasiyya wacce ta bayyana mata


ginshinkin rayuwan aure na farin ciki a cikinta, da kuma


abunda ya wajaba agareta na hakkin mijinta, tace mata: yake


diyata da ace ana barin nasiha saboda falalar ladabi da nabar


maka haka, sai dai tana tunatar da wanda ya manta, da guzuri


game hankali, da ace mace tana wadatuwa daga miji da


iyayenta sun wadatu, saboda kuma tsananin bukatar su zuwa


gareta yasa ta zama mafiya wadatan mutane akan sa, sai dai


mata saboda maza aka halicce su, kuma suma saboda su ne aka


halicci maza.


“ Ya diyata: lallai zaki bar wani wuri da rayuwan da kika fito


daga ciki, kuma zaki bar rayuwa wacce aka tarbiyyance ki aciki


zuwa ga wani wuri da gida wanda baki sanshi ba, da gari


wanda bakyasomn sa, zai wayi gari da mulkin sa akanki a


matsayin me sa ido da iko, saboda haka ki zaman masa baiwa


zai zaman maki bawa da maki hidima, ki kiyaye masa wannan


abubuwa goma zai zaman maki madogaro:


Abu na farko dana biyu: Kankan da kai a gareshi da qana'a,


da kyakyawan biyayya da jin maganar sa.


Abu na uku da hudu: ki kiyaye ganin sa da hancin sa akanki,


kada ki kuskura ya ganki a cikin mummunan siffa ko kuma ya


shaka daga gareki sai kamshi me dadi.


Abu na biyar da shida: ki kiyaye lokacin baccin sa da abincin


sa, domin zafin yunwa akwai tunzurar wa kuma yunwan bacci


yan ahaifar da kiyayya


Na bakwai da na takwas: ki tsare masa dukiyan sa, da kuma


kula da hidimar sa da iyalan sa, kuma hikimar mallakan dukiya


shine: kyautata kimantawa, a cikin iyali kuma shine kyautata


tafiyar dasu.


Na tara dana goma: kada ki saba masa umurnin sa, kuma kada


ki yada masa sirrin sa, saboda idan kika saba umurnin sa


zuciyar sa zatayi kunci kuma idan kika yada sirrin sa bazaki


samu aminci ba daga tarkon sa, sa'annan kashedin ki dayin


farin ciki a gaban sa idan ya kasance yana cikin damuwa da


bakin ciki kuma kada ki rika nuna bakin ciki a gaban sa idan


yana cikin farin ciki. “


A cikin wannan dukan sa zai bayyanan mana girman


matsayi da daraja na kololuwa wanda mace take dashi a


karkashin inuwar shari'ar musulunci wannan kuma raddi ne ga


wanda yace lallai musulunci ya zalumci mace, taya wanda yaso


ta ya kumadayaw adaga cikin fadakarwan sa tattare da kula da


himmatuwa da ita zai zalumce ta da take mata hakki, wannan


shine abunda zai bayyanan maka yakai me karatu me daraja


cikin wannan littafi dan karami wanda zayyi magana a cikinta a


bangaren soyayya cikin rayuwan rahama na shiriyan


Muhammad dan Abdullahi s.a.w tare da iyalan sa wand


akasancewar sa me isar da addini da kuma shugaban al'umma


be sanya shi ba ya manta da kula da iyalan sa yadda ya takaita


wannan himmatuwa cikin kalmomi kadan wanda suka kunshi


ma'anoni daya ya kuma sanya shi wasiyya ga al'ummar sa


yadda yace:


“ mafi alherin ku shine mafi alheri ga iyalan sa kuma ni ne


mafi alherin ku ga iyalai na ” buhari ne ya rawaito shi.


An kiyasta alherin maza da gwargwadon alherin su ga


iyalan su da kuma kyautata zamanta kewa dasu wannan alheri


wanda take kaiwa ga soyayy da rahama shine s.a.w mafi alherin


mutane wanda alherin sa yasanya sa cikin kololuwan tsani na


kamalar mutum cikin rahama da soyayya da kyautata mu'amala


tare da mutane baki daya da kuma iyalansa musamman kuma


daga cikin abunda zayyi nuni akan haka shine lokacin da ayar


zabi ya sauka akan matar sa lokacin da suka tambaye shi


ciyarwa sama da abunda yafi karfin sa da kyalkelin rayuwan


duniya sai suka zabe shi suka kuma yarda da zama dashi cikin


rayuwa kamewa Aisha Allah ya kara mata yarda tana cewa:


lokacin da aka umurci manzon Allah s.a.w da yaba matan sa


zabi sai ya fara dani, yace:


“ lallai zan Ambato maki wani abu amma babu laifi ki


shawarci mahaifin ki akai ” sai tace: hakika kasan cewa


mahaifina bazai taba umurtana da rabuwa dakai ba, sai


tace: sai yace: “ lallai Allah madaukaki yace: ((yakai


wannan annabi kace ma matan ka idan kun kasance kuna


son rayuwna duniya ne da kyalekelinta to ku zo zan jiyar


daku kuma sai na sake ku saki mekyau. Idan kuma kun


kasance kuna son Allah da manzon sa da gidan lahira to


lallai Allah ya tanadar da wani irin lada me girma ga masu


kyautatawa daga cikin ku)) [suratul ahzab ayata: 28-29] sai


nace tab yanzu akan wannan abu ne zan shawarci mahaifi


na? lallai ni inason Allah da manzon sa da gidan lahira. Sai


tace: sa'annan matan manzon Allah s.a.w suka aikata irin


abunda na aikata nima ” muslim ne ya rawaito shi.


Wannan idan yana nuni akan wani abu to hakika nuni yake


akan so da suke masa da yarda da kuma rikon da suke masa na


abunda suka samu daga gareshi na halaye masu girma da kuma 


kyawu cikin mu'amala da so da kaskantar dakai wanda suka


kunsa dukan su kuma sun samun yakini cewa fa bazasu taba


samun Kaman sa ba, hakika manzon Allah s.a.w ya kasance


yana da mata tara wanda suke rayuwa a karkashin sa kuma


suna rayuwa me kyau da farin ciki, Ha'inata tace game dashi


wata marubuciya yar kasar italiya L.Veccia Vaglieri cikin


littafin ta me suna kariya game da Musulunci wacce take kare


sag a wanda ya zargesa da sha'awa: lallai Muhammad a tsawon


shekarun san a samar taka wanda sha'awar mutum yafi karfi a


cikin sa kuma dukda cewa ya rayu cikin al'ummar larabawa


wacce aure ya zama kamar wata cibiya ce ta zamanta kewa


wacce aka rasa ko kuma ace babu kuma auren mata da yawa


shine ka'aida a wurin su, kuma saki abu ne me sauki wanda


bashi da wani iyaka amma dukda haka be aura ba face mace


daya kawai wacce itace Khadija Allah ya kara mata yarda


waccce shekarun ta ya kasance sama da nashi shekarun ya


kasance yana da shekaru ashirin da biyar ya aure ta ne saboda


tsabar so kuma be sake aure ba har sai bayan rasuwan ta bayan


yakai shekaru hamsin da haiwuwa kuma hakika auren sa dayayi


ya kasance dalilin zaman ta kewa ne ko kuma siyasa saboda


burin sa cikin wannan auren shine karrama wannan matan


wanda suka siffatu da tsoron Allah zuwa samar da alaka ta aure


tare da wasu jama'a da kabilu na daban saboda fatan hada wani


hanya sabuwa na yaduwan musulunci da hakan idan aka cire


Aisha Allah ya kara mata yarda a cikin su, manzon Allah s.a.w


ya aure matan da ba masu kyau bane sosai ko kuma halitta me


ban sha'awa ko kuma budurwa shin idan haka ne ya kasance


mutum me yawan sha'awa ne kenan? Ina bah aka abun yake ba


hakika ya kasance mutum ne me tauhidi, kuma ta yiwu cewa


kwadayin da yake dashi na yara shi yasa shi yin wani aure


sabo, saboda yaran da Khadija ya haifa Allah ya kara mata


yarda sun mutu bama ba tare da cewa yana da dukiya ba me


tarin yawa ya dauki wannan nauyi na iyalai masu yawa sai dai


kuma ya lazimci daidai to cikakke tsakanin su cikin ko wani 


hali be taba karkara ba ko sau daya wurin nuna banbanci na


hakki tare da daya daga cikin su kuma hakika yayi harkokin sa


ne yana me koyi da sunnar annabawa wanda suka gabata


amincin Allah ya tabbata a garesu kamar musu da makamantan


sa wanda be bayyana ba cewa wani daga cikin mutane yana


kalubalantar su akan yawan matan da suke dashi shin


sakamakon hakan zai iya koma wa zuwa da cewa mun jahilci


daya ne daga cikin yanayin rayuwan su ta yau da gobe kamar


yadda muka san komai na rayuwan manzon Allah s.a.w tare da


iyalan sa.


Lallai manzon Allah s.a.w me daraja mutum ne me girma


wanda tarihi tasan shi wacce take da tasiri me girma wurin


canza yanayin duniya a cikin shaidar masu adalci cikin


mutanen da ba musulmai ba da kuma wanda suka kwarai wurin


karanta tarihin sa suka kuma yi dubi me zurfi zuwa ga sakon sa


da kuma yaduwar ta da tasirin ta da misali ana cewa gaskiya


shine abunda makiya suka shaida yadda (Mickel Hart) yake


cewa cikin littafin sa me sunan mutum dari wanda sukayi tasiri


cikin rayuwan dan adam: lallai zabi na ga Muhammad shine na


martaban farko cikin jerin mutanen duniya da sukayi tasiri ga


mutane zai iya batama wasu makaranta rai wasu kuma zasu iya


ja da hakan sai dai ya kasance shine mutum daya tilo cikin


tarihi wanda yacimma nasara a bayyane a fannin addini da


kuma duniya.


Wannan shine abunda da mutanen da suke tare damu suke gani


na saurin yaduwar da'awar sa da kuma kwadayin mabiyan sa


akan riko da shari'ar sa da kuma kokari tukuru wajen yada


sunnar sa mutane dayawa suna shiga addinin sa kuma yan


kadan ne matuka masu fita daga cikin sa ita gaskiya idan ta taba


fadin zuciya ta hadu ruhi sai su zama suna bin ta, Bilal ,utumin


habasha a lokacin daya musulunta an azabtar dashi da bulala an


kuma daura masa dutse me zafi akan kirjin sa kuma an kifa


fuskar sa akan sahara me zafi na makka domin ya bar addinin 


sa amma hakan be kara masa komai ba face tabbatar dashi da


kara masa kwarin gwewa yana maimaita kalamar sa ta tabbata


akan haka na tauhida Allah daya ne Allah daya ne.


Haka shima Sa'ad dan abi Waqqas ya kasance mutum ne me


tsananin biyayya ga mahaifiyar sa, mahaifiyar sat ace masa a


lokacin daya musulunci bazan kara cin abinci ba ko shan ruwa


har sai na mutu, sai a rika tozarta ka dani a rika cewa: ya wanda


ya kashe mahaifiyar sa. sai yace: kada ki aikata haka ya


mahaifiyata domin ni dai bazan bar wannan addini ba. sai yace:


sai ta zauna rana daya bataci abinci ba, sai ta fara rashin lafiya,


sai yace: ta kara zama rana na biyu bataci abinci ba sai wannan


rashin lafiya nata ya karu. Sai yace: a lokacin dana ga haka sai


nace: ki sani fa wallahi ya mahaifiya ta da ace kina da rai guda


dari zasu rika fita daya bayan daya har su gama fita bazan taba


barin wannan addinin nawa ba domin wani abu ba, idan kin so


kici abinci, idan kuma kinso kada kici, a lokacin da taga haka


sai taci abinci.


• Manzon Allah ta fuskan shakatawa da


iyalan sa.


Musulunci yana koyar da musulmi laluran bawa kai hakkinta


na hutu da shakatawa na halal cikin iyaka na shari'a domin ka


nisantar da ita daga kosawa da kuma samun kwarin gwewa na


kaiwa zuwa ga hanyar Allah madaukaki cikin nishadi da


kokari, sai dai hakan yana da sharadin cewa kada mutum ya


wuce gona da iri cikin wannan bangare na wasanni sama da


bangaren rahiran sa sai rayuwan musulmi ta canza zuwa ga


wasa wanda bashi da wani amfani ya kuma mantar da mutum


abunda aka halicce sa domin sa, hakika sahabban manzon Allah


s.a.w Allah ya kara masu yarda sun kasance a farkon musulunci


suna kudurce cewa lallai musulunci addini ne wanda baisan


hutu ba da wasa na halal ba da kuma shakatawa hanzalat dan


hazim al hanafi yana cewa:


“ Abu bakar ya hadu dani sai yace mun yaya kake? Ya


hanzalata! Sai nace masa ni hanzalata nayi munafunci. Sai


yace subhanallah (tsarki ya tabbata ga Allah)! Me kake


cewa? Sai nace: idan muna wurin manzon Allah s.a.w yana


tunatar damu wuta da aljanna kamar muna ganin su da


idanun mu, amma idan muka bar wurin sa sai ya shagala


da wasa da matan mu da yaran mu da kuma neman duniya,


sai mu manta abunda makaji a wurin manzon Allah


dayawa. Sai Abubakar yace: wallahi muma haka yake


faruwa damu. Sai muka tafi gun manzon Allah s.a.w ni da


Abubakar bayan mun shiga wurin sa sai nace: hanzalata


yayi munafurci ya manzon Allah s.a.w! sai manzon Allah


s.a.w yace ” me yayi? ” sai nace: ya manzon Allah! Mun 


kasance idan muna wurin ka kan atunatar damu wuta da


aljanna kamar muna ganin su da idanun mu amma idan


mun bar wurin ka sai mu shagala da matan mu da yaran


mu da neman duniya mu manta da dayawa. Sai manzon


Allah s.a.w yace: “ ina rantsuwa da wanda raina ke hannun


sa! da zaku dawwama akan halin da kuke ciki a wurina da


kuma tunanin wuta da aljanna da mala'iku sun rika


gaisawa daku hannu da hannu akan hanyar ku da kuma


gadon baccin ku. Sai dai ya hanzalata! Lokaci bayan lokaciwatan idan kayi tunanin lahira da bautan Allah ka huta


sannan ka sake haka dai ” ya fada masa hakan har sau uku.


Muslim ne ya rawaito shi.


Sai dai wannan mahanga ta canza a lokacin da musulunci ya


sanya wasa tare da iyalai da kuma sanya masu farin ciki arai


cikin addini kuma ba bu mamali akan haka kasancewar


musulunci addini ne wanda ya kunshi komai domin ya tattara


jiki da ruhi da rai da hankali manzon Allah s.a.w yana cewa:


“ dukkan abun da ba anbaton Allah bane to wasa ne da


bata okaci sai abu hudu kawai: wasan mutum da matar sa,


da koyan hawa doki, da koyan harbi da kuma koyan


nunkaya cikin ruwa ” . Hadisi ne ingantacce Ahmad da nasa'I


da baihaqi ne suka raaito shi.


Kuma wannan mahangar ta kara canzawa har wayau a


lokacin da suka gani daga manzon Allah s.a.w a bunda yake


nuni akan haka, jabir dan samurata yana cewa: manzon Allah


s.a.w ya kasance baya tashi daga inda yayi sallar asuba har sai


rana ta fito, idan rana ta fito sai ya tashi. Sun kasance suna fira,


har fira yazo kan al'amuran lokacin jahiliyya sai suyi daria da


murmushi. Muslim ne ya rawaito shi.


Bawai wannan bane kuma kawai a'a ya tsananta akan


awajabcin bama kai hakkinta na shakatawa da kuma hutu


wannan shine abunda manzon Allah s.a.w yace ma Abdulahi


dan Umar:


“ yakai Abdullahi, an bani labarin cewa kana azumi kullum


da rana sannan da daddare kayi sallar dare. Sai yace haka


ne ya manzon Allah, sai manzon Allah s.a.w yace:


“ kada ka aikata haka, ka rika yin azumi kana hutawa,


kuma ka rika sallar dare kana yin bacci, domin jikinka


yana da hakki akanka, idon ka shima yana da hakki


akanka, sannan matarka itama tanada hakki akanka, haka


bakonka shima yana da hakki akanka ” buhari ne ya rawaito


shi.


1. Manzon Allah me daraja s.a.w yana shakatawa da


iyalan sa:


Manzon Allah s.a.w ya kasance yana shakatawa da iyalan sa


domin canza yanayi da kuma samun dama ya sanya masu farin


ciki da kuma kore masu kosawa da damuwa, Aisha matar


manzon Allah s.a.w tana cewa: yan habasha sun shigo


masallaci suna wasa aciki sai manzon Allah s.a.w yace:


“ yake iyar fara kinason ki kalli wasan su? ” sai nace eh


inaso sai ya tashi ya tafi bakin kofa nazo na sameshi a bakin


kofa sai ya sanya gemuna akan kafadar sa, tace: daga cikin


abunda suke fadi a wannan rana itace: baban kasim


mutum ne na kwarai, sai manzon Allah s.a.w yace: “ ya


isheku haka ” sai nace: kada kayi gaggawa ya manzon


Allah. Aisha tace: banso kallon suba face kawai inason na


nunama mata matsayi na a wurin sa ne da kuma matsayin


sa aguna ”


2. Manzon Allah yana kawar dakai da hakuri domin


farin cikin iyalan sa:


Ubangijin sa ya ladabtar dashi sai ya kyautata masa ladubban


sa, ya kaance cikin dabi'ar sa s.a.w baya yima wani abun da


bayaso kuma yana yafiya da kawar dakai akan wasu abubuwa


wanda iyalan sa suke aikatawa wanda be sabama shari'a ba,


ma'anar kawar dakai shine bayyanar da rashin damuwa da abu 


tare da ilimi da kuma sanin abunda za'a kawar dakai akai, Aisha


matar manzon Allah s.a.w tana cewa: Abubakar Allah ya kara


mata yarda ya shigo wurinta ya tarar da wasu bayi biyu a


lokacin ranakun muna suna mata kida, manzon Allah s.a.w


kuma ya rufe da tufafin sa, sai Abubakar yayi masu tsawa, sai


manon Allah s.a.w ya bude fuskan sai yace:


“ ka kyale su ya Abubakar, domin ranakun idi ne ” ,


ranakun muna kenan. Sai Aisha tace: naga manzon Allah


s.a.w yana kare ni, ina kallon habashawa suna wasa cikin


masallaci, sai Umar ya tsawatar masu sai manzon Allah


s.a.w yace: “ ka kyale su kuyi was an ku cikin aminci yaku


yayan Arfida ” buhari ne ya rawaito shi.


3. Manzon Allah s.a.w ya kasance yana tabbatar da


farin cikin iyalan sa:


Daga cikin alamun soyayya da kuma daidaito da tabbata


tausayi shine neman dukkanin abunda zai shigar da farin ciki


cikin zuciyar wanda kake so, hakika manzon Allah s.a.w ya


kasance yana kokarin ganin ya kawo abunda zai shigar da farin


ciki ga iyalan sa, Aisha Allah ya kara mata yarda tana cewa:


“ ta kasance tana wasa da yara mata a wurin manzon Allah


s.a.w kuma kawayenta suna zuwa mata sai su rika boyewa


cikin gidanta domin kunyan manzon Allah s.a.w. sai tace:


manzon Allah s.a.w ya ksance yana turo su wuri na ”


msulim ne ya rawaito shi.


4. Manzon Allah s.a.w yana wasa da iyalan sa:


Kamar yadda cikin karantarwan musulunci akwai abunda yake


gyara gangan jiki da ruhi haka akwai abunda yake gyara rai na


shigar mata da farin ciki da murna hakika manzon Allah s.a.w


ya kasance baya mantawa da wannan bangaren yana bashi


hakkin sa na himmatuwa dashi yana wasa da sahabban sa da


iyalan sa kuma baya fadi sai gaskiya, kuma an sani cewa wasa


yana daga cikin abunda rai keso wanda yake Koran damuwa da 


kosawa daga zuciya da sharadin iyakance sa da iyakoki da


sharudda na shari'a kada ayi karya acikin sa ko kuma


munanawa wani dashi, Aisha Allah ya kara mata yarda tanan


cewa:


“ manzon Allah s.a.w ya dawo wurina wata rana daga


jana'iza a makabartan baqi'a, sai ya tarar dani ina fama da


ciwon kai ina cewa wayyo kaina! Sai yacemun ya Aisha! ni


nafiki jin ciwon kai dinnan (domin ciwon ki zai wuce ki


warke ni kuma nawa bazai warke ba domin na kusan


mutuwa), sai yace mata: me zai dameki da zaki mutu kafin


ni, zan maki wanka na sanya maki likafani na kuma yi


maki salla da birneki?! Sai tace: ni kuma kamar ina kallon


ka cikin wannan hali wallahi da zaka aikata dukkanin


abunda ka Ambato daka koma gidana ka zama ango da


sauran matan ka! Sai manzo Allah s.a.w yayi murmushi,


sa'annan ya fara rashin lafiyar daya mutu a cikinta ” darimi


ne ya rawaito shi kuma albani ya ingantashi.


5. Manzon Allah yana kewaya dan shakatawa tare da


iyalan sa:


Rayuwan sa baya rabuwa da abunda yake hutar da kai, hakika


manzon Allah s.a.w ya kasance yana fita tare da iyalan sa ya


kewaya dasu, isar da sakon sa da kuma shugabancin al'umma


baya shagaltar dashi daga kula da wannan bangare na rayuwa,


ga Aisha nan tana rawaito mana labarin wani daga cikin tafiyar


ta tare da manzon Allah s.a.w:


“ ….. kuma manzon Allah s.a.w ya kasance idan dare yayi


yana fita tare da Aisha suna fira da ita… ” muslim ne ya


rawaito shi.


6. Manzon Allah s.a.w yana dariya daga wasan da


yakeyi da iyalan sa:


Dariya al'amari ne na fidira tare da mutum yanada rabo cikin


karantarwan musulunci, manzon Allah s.a.w yace:


“ murmushin ka ga fuskar dan uwanka sadaka ce ” tirmizi


ne ya rawaito shi kuma hadisi ne ingantacce.


Haka addinin mu ya koya mana cewa ya dace ga musulmi ya


kasance me sakin fuska ba me murtukewa ba da daure fuska a


koda yaushe, hakika manzon Allah s.a.w ya kasance yana


dariya kuma yana bada dariya domin ya kori daure fuska daga


majalisin say a kuma cika yanayin da farin ciki da natsuwa,


shin me fadin cewa:


“ kada ka raina kankancin aikin lada koda kuwa ka hadu


da dan uwanka ne cikin sakin fuska da murmushi ”


7. Manzon Allah s.a.w yana yada ruhin farin ciki ga


ilayan sa:


Ya kasance daga cikin dabi'ar sa wasa da tsokanar wanda suke


tare, iyalan sa suna da rabo daga cikin saukin sa da fara'ar sa da


tausayin sa da kuma zaulaya tare dasu domin yak ore masu


daure fuska da kosawa daga garesu ya kuma sanya masu farin


ciki cikin zukatan su, Aisha Allah ya kara mata yarda tana


cewa: nazo wurin manzon Allah s.a.w da wani irin abinci


kamar tuwo da miya sai nace ma saudat kici ga manzon


Allah a tsakanin mu sai taki ci, sai nace mata kodai kici ko


kuma na yaba maki shi a fuska, sai taki ci sai na sanya


hannuna cikin wannan abinci na yaba mata shi a fuska sai


manzon Allah s.a.w yayi dariya sai manzon Allah s.a.w ya


daga kafarsa daya daura akan saudat domin ta iya rama


abunda na mata, sai yacema saudat kema ki yaba mata a


fuska, sai ta yaba mata sai manzon Allah s.a.w yayi dariya


sai ga umar ya wuce yana cewa ya Abdullahi ya Abdullahi


sai manzon Allah s.a.w yayi zaton zai shigo ne sai yace


mana ku tashi kuje ku wanke fuskan ku, sai Aisha tace


bangushe ba inajin tsoron Umar saboda kwarjinin sa a


wurin manzon Allah s.a.w ” Abu ya'ala al musili ne ya


rawaito shi kuma albani ya inganta shi.


8. Manzon Allah yana halartan wurin mutane masu


farin ciki:


Daga cikin hikimar sa s.a.w shine yana mu'amala da kuma aiki


da kowa da irin abunda ya dace dashi matukar be sabama


shari'a ba, Aisha Allah ya kara mata yarda tana cewa:


“ manzon Allah s.a.w ya dawo daga yakin tabuka ko


khaibara acikin lalitar ta akwai wani labule sai iska tazo ta


daga gefen wannan labule na kayan was an Aisha sai yace:


“ menene wannan ya Aisha? “ sai tace kayan wasana ne! sai


yaga wani doki a cikin su yana da fuka fukai guda biyu fata


wanda ake rubutu akai, sai yace: menene wannan nake gani


a tsakiyar su? Sai tace: doki ne, sai yace menene akanshi?,


sai tace: fuka fuki ne, sai yace: wani irin doki ne da fuka


fuki? Sai tace: bakiji cewa Sulaiman yanada doki me


fuffuke bane? Sai tace: manzon Allah s.a.w yayi dariya har


hakoran sa na dadashi suka bayyana ” abu dawud ne ya


rawaito shi kuma albani ya inganta shi.


9. Manzon Allah s.a.w yana farin ciki da murnan iyalan


sa:


Shigar da farin ciki da murna a zuciyar iyalai alama ce ta


alherin mutum ga iyalan sa kuma manzon Allah s.a.w ya


kasance na gaba-gaba wurin shigar da farin ciki da murna a


zuciyar iyalan sa, Aisha Allah ya kara mata yarda tana cewa:


“ manzon Allah s.a.w ya kasance yana zaune sai yaji sauti


mabanbanta da kuma sautin yara sai ya mike sai yaga wata


mata yar habasha tana wasa ga yara a gefenta sai yace: “ ya


Aisha zo ki gani ” sai nazo na daura gemuna akan kafadar


manzon Allah s.a.w ina kallon ta sai yacemun: “ ke ishe ki


bane kallon haka ” sai nace eh be isheni ba domin naga


matsayina a wurin sa, sai ga Umar yazo yan akoran mutane


daga wannan mata sai manzon Allah s.a.w yace: “ lallai ina


ganin shedanun aljanu da mutane suna guduwa idan Umar 


yazo ” sai tace sai nadawo ” . Tirmizi ne ya rawaito shi kuma


albani ya inganta shi.


10. Manzon Allah s.a.w yana zama da fira da iyalan sa:


Ya kasance daga cikin al'adar sa cewa yana zama da fira da


iyalan sa wanda yake wanke masu zuciya daga cikin haka daga


cikin abunda sakamakon mu'amalar yau da gobe zai haifar


kuma yanada tasiri me girma wurin kara shakuwa da dankon


soyayya, safiyyat diyar hayiyi matar manzon Allah s.a.w tana


cewa:


“ tazo wurin manzon Allah s.a.w domin masa zaria a


masallaci yana cikin ittikafi, cikin kwanaki gomam karshe


na watan ramadana, sai tazauna suka fira tare na tsawon


awa daya, sa'annan ta tashi zata tafi gida, sai manzon Allah


s.a.w ya tashi yi mata rakiya, bayan ya kawo kofar


masallaci kusa da kofar ummu salmata, sai wasu mutum


biyu cikin mutanen madina suka ganshi, sai sukayi sallama


ga manzon Allah s.a.w, sai manzon Allah s.a.w yace masu: “


ku dakata safiyya ce diyar hayiyi ” . Sai sukace: tsarki ya


tabbata ga Allah ya masnzon Allah, abun yayi masu girma,


sai manzon Allah s.a.w yace: “ lallai shedan yana yawo jikin


mutum kamar yadda jini yake yawo, ina tsoron ya jefa


wani abu cikin zuciyar ku ” buhari ne ya rawaito shi.


• Manzon Allah s.a.w ta bangaren tausayin


sa ga Iyalan sa:


Lallai musulunci yana kula da bangaren mutum wanda aka


halicce sa akai wanda daga ciki akwai bangaren tausayi


tsakanin miji da mata, sai yayi dubi zuwa ga sha'awa na jinsin


mutum akan lalura wacce ya wajaba a kosar da ita da kuma


rashin dadasheta, sai dai kuma dauketa daga kasance warta


sha'awa kawai na dabbanci abun kyama saboda haka ne ya


sanya hanyar biyan wannan sha'awa ta hanyar aure wanda ya 


ginu akan tsarki da kamewa da kuma samar da natsuwar rai da


tabbatar da tausayi da kuma lamunce hakkoki na ma'aurata,


Allah madaukaki yana cewa:


“ kuma daga cikin ayoyin sa ya halatta maku mataye daga


jikin ku domin ku samu natsuwa a garesu kuma ya sanya


soyayya da rahama a tsakanin ku lallai acikin haka akwai


ayoyi ga mutane masu tunani ” suratul rum ayata 21.


Saboda haka ne musulunci ya umurci mabiyan sa da saurin yin


aure idan suka samu ikon haka ya kuma yi bayanin dalilin haka,


sai manzon Allah s.a.w yace:


“ yaku taron samari! Duk wanda ya samu abun yin aure to


yayi aure, domin hakan yafi wurin kame kallo da kuma


kiyaye farji, wanda kuma be samu ba to ya rika yin azumi


domin hakan kariya ne a gareshi ” Muslim ne ya rawaito shi.


Ya kuma yi hani daga ruhubanan ci (kebewa domin bauta


kullum) da kuma barin yin aure da kuma gudun duniya baki


daya, an karbo daga anas dan malik Allah ya kara masa yarda


yace:


“ wani mutum uku sun zo gidan manzon Allah s.a.w suna


tambayar matan sa game da bautan sa bayan sun fada


masu suka jinjina haka sai sukace mu kuma muna ina ace


manzon Allah wanda aka gafarta masa zunuban sa baki


daya wanda ya gabata da wanda zaizo yana aikata irin


wannan bauta, sai dayan su yace ni daga yau kollum sallar


dare zantayu har nabar duniya dayan kuma yace ni daga


yau kullum azumi zantayi har nabar duniya dayan kuma


yace ni daga yau ba ruwa na da mace har Abadan sai


manzon Allah s.a.w yazo yace masu kune wanda sukace


kaza da kaza, ku sani cewa wallahi na fiku tsoron Allah da


takawa amma ni ina azumi kuma ina hutawa kuma ina


bacci da yin sallar dare kuma ina auren mata kuma duk 


wanda ya kyamaci sunnata to baya tare dani ” buhari ne ya


rawaito hadisi.


Muslunci ya girmama bangaren tausayi tsakanin miji da mata


ya sanya shi ya zama ibada wanda ake ba musulmi lada akai


kamar yadda ake bayar da alada akan ayyukan alheri a lahira,


manzon Allah s.a.w yace:


“ …. ” Kuma acikin jima'in dayan ku shima akwai sadaka


” sai sukace: ya manzon Allah yanzu dayan mu zai biya


sha'awar sa kuma abashi lada? Sai yace: “ ku bani labari


yaya kuke gani idan yaje ya biya sha'awar sa ta hanyar


haramun shin za'a bashi zunubi? To Kaman haka ne idan


ya biya sha'awarsa ta hanyar halal za'a bashi lada ” muslim


ne ya rawaito shi.


Ya kuma kwadaitar a wannan bangare saboda muhimmancin


dake cikin sa cikin rayuwan musulmi saboda ta hanyar sa ne


ake samun dawwama na zuciya da natsuwa ta bangaren


soyayya wanda zai bashi damar yin ibadar sa cikin natsuwa


kwakwalwa.


Kuma ya kamata mu kawo wasu daga cikin bangarori na


rayuwar manzon Allah na tausayi da soyayya tare da


iyalansa:


1. Manzon Allah s.a.w baya ha'intar iyalan sa:


Manzon Allah s.a.w ya kasance misali abun koyi wurin


kamewa, ya bayyana abunda ya dace musulmi ya aikata a


lokacin da shedan ya jefa masa abunda zai kaishi zuwa ga


aikata alfasha a cikin zuciyar sa, Jabir dan Abdullahi Allah ya


kara masu yarda yana cewa:


“ idan dayan ku yaga wata mace ta burge shi to ya koma ga


iyalin sa domin itama tanada irin abunda wancan mace


take dashi ” Tirmizi ne ya rawaito shi kuma albani ya


ingantahi cikin littafin al sahiha 235.


2. Manzon Allah s.a.w da shaukin sa ga iyalan sa:


Lallai saurin dawowan mutum ga iyalan sa daga tafiyar sa dalili


ne akan soyayyar sa da shaukin sa a garesu kuma akwai amfani


cikin haka wanda baya boyuwa na tabbatan zuciya da tausayi


da soyayya saboda haka ne ya kasance cikin karantarwan


manzon Allah s.a.w ya kasance a bayyane akan haka a lokacin


day ace:


“ tafiya bangare ce ta azaba, yana hayan ku baccin sa da


abincin sa da abun shansa, saboda haka idan dayan ku y


agama biyan bukatar sa a tafiyar sa to ya gaggauta dawowa


ga iyalan sa ” buhari ne ya rawaito shi.


3. Manzon Allah yana sabanta soyayya da kauna ga


iyalan sa:


Kyauta tana da muhimmanci kuma tana kara daraja idan ta


kasance daga wanda kake so saboda haka ne karantarwan


manzon Allah s.a.w ta kasance a bayya ne a lokacin da yace: “


kuyi kyauta zaku so junan ku ” buhari ne ya rawaito shi cikin


littafin sa na adabul mufrid kuma albani ya inganta shi.


Ya kuma kara fadi har wayau s.a.w: “ yaku matan musulmai


kada wata ta raina wata kyauta da zata ba wata koda kuwa


da misalin akuya ne mara nama ” buhari da muslim ne suka


rawaito hadisin.


4. Manozn Allah s.a.w yana kame kallonsa akan iyalan


sa kawai:


Kiyaye gabbai da kuma rage su akan iyalai dalili ne na


daidaitan mutum kuma shedan yana kokari akan karkatar da


wannan hali da kuma amfani da ita cikin dabi'u makaskanta


hakika an rubutama dan adam rabo na zina wanda dole ya


aikata hakan babu makawa: idanu suna zina kuma zinan su


shine kallo, kunne shima yana zina kuma zinan shi shine


sauraro, harshe ma yana zina kuma zinan shi shine magana,


hannu yana zina zinan shi shine tabawa, kafafuwa suna zina 


kuma zinan su shine tafiya, zuciya yana buri da sha'awa sai farji


ya gasgata hakan ko kuma ya karyata kamar yadda manzon


Allah s.a.w ya bada labari akan haka, kuma hadisin buhari da


muslim ne suka rawaito shi. Wannan kuma lafazin muslim ne,


ruwaiyar buhari a takaici take.


Kuma hakika manzon Allah s.a.w ya kasance abun koyi ne


akan haka, Aisha Allah ya kara mata yarda tana cewa:


“ muminai mata sun kasance idan sunyi hijira zuwa ga


manzon Allah s.a.w yana masu jarabawa da kuma masu


mubaya'a saboda fadin Allah madaukaki cewa yakai


wannan Annabi idan mata muminai sun zo maka suna


maka mubaya'a akan cewa bazasu hada Allah da wani ba


cikin bauta kuma bazasu yi sataba kuma bazasuyi zina ba


har zuwa karshen ayar sai Aisha tace duk wacce ta


tabbatar da hakan cikin wannan mata muminai to hakika


tayi mubaya'a na shari'a manzon Allah kuma ya kasance


idan sun tabbatar da hakan da maganar su sai yace masu


ku tafi hakika nayi maku mubaya'a, kuma wallahi manzon


Allah s.a.w be taba shafan hannun wata mace ba ko sau


daya kawai yana masu mubaya'a ne da magana , Aisha tace


wallahi bai taba amsar komai ba daga wurin mata sai


abunda Allah yayi masa umurni kuma tafin hannun sa be


taba shafan tafin hannun wata mace ba ko sau daya, ya


kuma kasance yana cewa masu idan ya amsa daga garesu


cewa hakika nayi maku mubaya'a da magana ” muslim ne


ya rawaito shi.



Posts na kwanan nan

FALALAR AZUMIN KWANA ...

FALALAR AZUMIN KWANA SHIDA SHAWAL

TAKAITACCEN BAYANI MA ...

TAKAITACCEN BAYANI MAI ANFANI GA SABON SHIGA MUSULUNC

ZIKIRAI WADANDA AKE Y ...

ZIKIRAI WADANDA AKE YIN SU DA SAFE DA KUMA YAMMA

BIDI’AR ‘YAN SHI’A A ...

BIDI’AR ‘YAN SHI’A A RANAR ASHURA