Artikel

Jerin Littafan Shi’a Na 8


Mugun Nufin


‘Yan Shi’a


ga


Al’umma


Umar Labxo


1


بسم الله الرحمن الرحيم


Gabatarwa


‘Yan Shi’a suna da baqin tarihi wanda yake cike da ta’addanci da rura wutar


fitina tsakanin Musulmi da taimakon kafirai a kansu wajen yaqar su da cinye


qasashensu, domin su, kamar yadda Ibnu Taimiya yake faxi, “A koda yaushe suna


neman taimako da kafirai da fajirai wajen biyan buqatunsu kamar yadda suke


taimakon kafirai da fajirai wajen biyan nasu buqatun.”1 Wannan shi ne halin


Rafilawa a tsawon tarihinsu, a ko wane zamani, kuma a ko wane wuri.


A nan Nijeriya, an ruwaito madugunsu, Ibrahim Yaqub Alzakzaki, yana


faxa wa Kiristoci, waxanda yake gayyata wajen Maulidinsa: “Ba da ku muke faxa


ba,” yana nufin su da Musulmi suke yaqi; ba da kafirai ba. Su kafirai abokan tafiya


ne; saboda haka Kiristoci suke halartar Maulidin ‘yan Shi’a, inda suke xaga Kuros,


watau suna nuna alamar addininsu a fili ba a voyewa.


Baqin tarihin ‘yan Shi’a aiwatarwa ne ga miyagun aqidojinsu na qiyayya da


gaba ga Ahalus Sunna, da ma duk wani Musulmi wanda ba ya bin tafarkinsu.


Malaman Shi’a suna qoqarin cusa gaba da qiyayya da mugun nufi a zukatan


mabiyansu ta hanyar ruwayoyin qarya da suke dangana wa Imamansu, waxanda


suke nuna halaccin jinin duk wanda ba xan Shi’a ba,2 da yin albishir da mummunar


makomar da take jiran sa.


A wannan taqaitaccen littafi, za mu fara da bayanin mugun nufin ‘yan Shi’a


ga al’umma kamar yadda yake a cikin aqidunsu da littafan manyan malamansu.


Sa’an nan daga bisani mu kawo misalai na baqin tarihinsu wanda yake tabbatar da


qaddamar da wannan mugun nufi a aikace.


1 Minhajus Sunna na Ibnu Taimiyya, bugun Darul Kutubil Ilmiyya, Bairut, ba tarihi, mujalladi na 2 shafi na 195.


2 Duba littafinmu, Matsayin Musulmi a wajen ‘Yan Shi’a.


2


Babi na Xaya


Mugun Nufin ‘Yan Shi’a ga Al’umma


‘Yan Shi’a suna qudure mugun nufi ga Musulmi da Musulunci kuma


wannan yana bayyana a fili daga abinda yake rubuce a cikin littafansu da abinda ke


fitowa daga bakin manyan malamansu. Manufarsu ta qarshe ita ce ganin bayan


Musulunci baki xayansa, da hallaka Musulmi, da rushe xakin Ka’aba da


Masallacin Annabi na Madina, da mayar da alqiblar Musulmi zuwa birnin Kufa.


Wannan mugun nufi nasu yana bayyana a cikin aqidarsu ta Mahadi da irin


abubuwan da Mahadin nasu zai yi idan ya bayyana.


Aqidar Mahadi a tushenta aqida ce ta Musulunci, amma malaman Shi’a sun


sauya ta, inda suka cusa qiyayyar Majusawan Farisa a cikinta, suka mayar da ita


wani mataki na tanadin rama gayya da xaukar fansa a kan Larabawa (watau


Sahabban Annabi) waxanda suka rusa daular Majusawa ta Iran a zamanin Sarkin


Musulmi Umar binul Khaxxabi, Allah ya qara masa yarda.


Hadisan Annabi (SAW) ingantattu masu yawa sun taho da bayanin Mahadi


da sunansa da sunan mahaifinsa da sifofinsa da wurin da zai fito da lokacin da zai


bayyana da kuma ayyukan da zai gabatar idan ya bayyana. Bayyanar Mahadi tana


cikin alamomin qarshen zamani da kusantar tashin alqiyama, kuma quduri da shi


vangare ne na aqidojin Ahalus Sunna, saboda hadisan da suka zo da shi ingantattu,


mutawatirai.


Mahadi zai bayyana a qarshen zamani. Zai fito daga zuri’ar Annabi (SAW),


daga ‘ya’yan Faxima, Allah ya qara mata yarda, ta vangaren xanta Hassan (RA).


Sunansa zai zama Muhammad binu Abdillah, zai bayyana daga gabashin duniya,


kuma za’a yi masa mubaya’a a xakin Ka’aba. Zai yi mulki shekara bakwai kuma a


zamaninsa Annabi Isa (AS) zai sauko zuwa duniya ya yi sallah a bayansa. Mahadi


3


zai cika duniya da adalci a bayan an cika ta da zalunci, zai kashe alhanzir kuma zai


karya kuros. Waxan nan abubuwa uku, watau sallar Annabi Isa a bayansa da kisan


alade da karya Kuros, nuni ne ga qarshen addinin Kirista da shafewarsa. Wannan


shi ne abinda hadisai suke tabbatar da shi dangane da al’amarin Mahadi.


Abu Sa’id Alkhudri, Allah ya qara masa yarda, ya ruwaito cewa Annabi


(SAW) ya ce, “Mahadi daga gere ni yake, mai qarancin gashin goshi, mai doron


hanci. Zai cika duniya da adalci bayan an cika ta da zalunci. Zai yi mulki shekara


bakwai.”1 Jabir binu Abdillah, Allah ya qara masa yarda, ya ruwaito, ya ce: Na ji


Manzon Allah (SAW) yana cewa, “Wata tawaga daga al’ummata ba za su gushe ba


suna yaqi a kan gaskiya, suna masu rinjaye, har tashin alqiyama…Sai Isa xan


Maryamu, tsira da aminci su tabbata a gare shi, ya sauko, sai sarkinsu ya ce: Wuce


ka yi mana sallah. Sai ya ce: A’a, lallai sashenku shuwagabanni ne a kan sashe,


saboda girmamawar Allah ga wanan al’umma.”2 Har yau, Abu Sa’id, Allah ya qara


masa yarda, ya ruwaito, ya ce: Manzon Allah (SAW) ya ce, “Isa xan Maryamu zai


sauko, sai Sarkin Musulmi Mahadi ya ce: Wuce ka yi mana sallah. Sai ya ce: A’a,


lallai sashenku shugabannin sashe ne don girmamawar Allah ga wannan


al’umma.”3


Wannan shi ne labarin Mahadin Musulunci, da yadda zai bayyana, da yadda


zai shugabanci duniya, ya shafe addinin Kirista, kuma ya kawo adalci da zaman


lafiya a bayan qasa.


Mahadin Shi’a ya sha bamban da Mahadin Musulunci a sunansa da


haihuwarsa da ayyukan da zai qaddamar a yayin bayyanarsa. Da farko, shi sunansa


Muhammad binul Hassan Al’askari, kuma ba haihuwar sa za’a yi a nan gaba ba,


a’a shi an riga an haife shi tun kimanin shekaru dubu da xari biyu da suka wuce.


Kuma a duk tsawon waxan nan shekaru, yana nan a voye a wani kogo a birnin


1 A duba Sunan Abi Dawud, Kitabul Mahadi.


2 Sahih Muslim, Kitabul Iman, Babu nuzuli Isa.


3 A duba Almanarul Munif na Ibnu Qayyimil Jauziyya, shafi na 147-148.


4


Samarra wanda a yau yake a qasar Iraqi. Wannan shi ne abu na farko da ya mayar


da Mahadin Shi’a almara.


Mahadin Shi’a zai fara da Larabawa, domin su ne tushen Musulunci, ya


gama da su. Muhammad Baqir Almajalisi, xaya daga cikin manyan malaman


Shi’a masu yawan talifi, ya ruwaito cewa idan Mahadinsu ya bayyana zai zubar da


jinin Larabawa kuma ya hakaito shi yana cewa, “Babu abinda ya rage tsakaninmu


da Larabawa sai yanka.”1


Dangane da sauran Musulmi Ahalus Sunna waxanda ba Larabawa ba, ‘yan


Shi’a suna da fatawa mai qarfi daga imaminsu na shida Abu Abdullahi Ja’afar


Sadiq, kan halaccin jininsu. Wani mai ruwayarsu da ake kira Dawud binu Farqad


ya ce: Na tambayi Abu Abdillahi(A.S): Me za ka ce dangane da kisan nasibi


(watau Ahalus Sunna)? Sai ya ce, “Jininsa halal ne sai dai ina jiye maka tsoro.


Idan ka samu iko ka rusa masa gini a ka, ko ka nutsar da shi a ruwa don kada a


samu shaida, to ka aikata.”2


Da yake sharhi a kan wannan ruwaya, imamin Shi’a na wannan zamani,


Ayatullahi Ruhullahi Khumaini ya yi qari kamar haka: “Idan ka samu iko ka karvi


dukiyarsa, karve ta ka aiko mana da khumusi.”3 Wannan qarin bayani daga


Khumaini yana nuna cewa wannan aqida ta ‘yan Shi’a tana nan ba ta sauya ba;


abinda kurum yake hana su aiwatar da ita shi ne rashin iko.


Wani abinda yake qara tabbatar da haka shi ne abinda Khumaini ya faxa wa


Sayyid Hussain Musawi a lokacin da ya ziyarce shi a birnin Teheran, bayan


1 Biharul Anwar na Muhammad Baqir Alajalisi, bugun Muassasatul Wafa, Bairut, 1403, mujalladi na 52 shafi na


318 da 349.


2 Biharul Anwar, mujalladi na 27 shafi na 231.


3 Kashful Asrar wa Tabri’atil A’immatil Adhar na Sayyid Hussaini Musawi, bugun Darul Iman, Iskandariyya,


2002, shafi na 89.


5


nasarar juyin juya halin ‘yan Shi’a na Iran a shekarar 1979. Musawi ya ce: A


wani zama na musamman tare da Imam ya ce mini: “Sayyid Hussain, lokaci ya yi


na zartar da wasiyar imamai, amincin Allah ya tabbata a gare su. Za mu zubar da


jinin nasibawa (Ahalus Sunna), mu karkashe ‘ya’yansu maza, mu raya matansu.


Ba za mu bar xaya daga cikinsu ya kuvuta ba daga wannan uquba. Da sannu


dukiyoyinsu za su zama ganima ga Shi’ar Ahalul Baiti. Kuma za mu shafe Makka


da Madina daga doron qasa saboda waxan nan birane biyu sun zama mafakar ‘yan


Wahhabiya. Kuma lallai ne Karbala, qasar Allah mai tsarki, ta zama ita ce alqiblar


mutane a cikin sallah. Za mu tabbatar da burin imamai, aminci ya tabbata a gare


su.”1


Kafin mu ci gaba, bari mu tuna wa mai karatu cewa, a koda yaushe ‘yan


Shi’a suka ruwaito irin wannan tavargaza suka dangana ta ga imamai, ya sani cewa


imamai barrantattu ne daga wannan qarya wacce take nuna kafirci da munafinci da


qin Allah da Manzonsa da Musulmi baki xaya. Malaman Shi’a jikokin Majusawa


suna fakewa da son imamai da Ahalul Baiti, suna xaukar wannan a matsayin wani


mayafi wanda suke lulluve kafircinsu da zindiqancinsu da shi.


Amma faxin Khumaini cewa za su rushe Makka da Madina saboda sun


zama mafakar ‘yan Wahhabiya, to wannan dalili da ya bayar na rushe Ka’aba


qarya ce kawai. Tun kafin a haifi Muhammad xan Abdulwahhab, ko a san


Wahhabiyanci, Rafilawa suna da aqidar rushe Ka’aba da Masallacin Annabi


(SAW) na Madina.


Wani mugun nufi da ‘yan Shi’a suka daxe da shi a zuci, kuma suke da niyar


zartar da shi har gobe, shi ne rushe Masallaci mai Alfarma, watau Xakin Ka’aba,


da Masallacin Annabi (SAW) a Madina da kuma sauya alqiblar Musulmi zuwa


1 Kashful Asrar na Musawi, shafi na 91-92.


6


Karbala. Malaminsu Majalisi ya ruwaito kamar haka: “Lallai Mahadi zai rushe


Masallaci mai Alfarma har sai ya mayar da shi ga harsashensa. Kuma zai rushe


Masallacin Annabi zuwa harsashensa.”1 Har yau, a wani wurin dabam, Majalisi


ya ruwaito kamar haka: “Farkon abinda zai fara da shi – yana nufin Mahadi – shi


ne ya fitar da waxan nan biyun (watau Abubakar da Umar daga kabarinsu) suna


xanyu shataf (kamar yanzu aka bunne su) ya watse su a iska, sa’an nan ya rushe


Masallacin.”2


Ita Karbala da suke burin mayar da ita sabuwar alqibla bayan rushe Ka’aba


wuri ne kusa da birnin Kufa (a yanzu tana qasar Iraqi) inda a nan ne aka kashe


Sayyidina Hussaini xan Ali binu Abi Xalib, Allah ya qara musu yarda. A


gwargwadon aqidar Shi’a, kasancewar Hussaini ya yi shahada a wannan wuri shi


ya ba wurin falala da xaukaka waxanda Rafilawa suka yi ta kambamawa har daga


qarshe suka fifita shi a kan garin Makka da Xakin Ka’aba. Daga qarerayin da suka


laqa wa wannan wuri domin su qawata shi ga jahilai, sun ce wai masallacin


annabawa ne kuma za’a kawo dutsen Hajarul Aswadu wurin bayan rushe Ka’aba.


Sun ruwaito xaya daga imamansu yana huxuba, yana cewa: “ Ya ku mutanen


Kufa, lallai Allah mai girma da xaukaka ya ba ku abubuwan da bai ba wani ba na


falala. Masallacinku shi ne xakin (Annabi) Adamu da (Annabi) Nuhu da (Annabi)


Idrisu, kuma shi ne masallacin (Annabi) Ibrahimu… Kuma kwanuka ba za su tafi


ba sai an kafa (dutsen) Hajarul Aswadu a cikin sa.”3


Girmama Karbala da xaukan ta a matsayin qasa mai tsarki da fifita ta a kan


Ka’aba qaryatawa ne qarara ga Alqur’ani mai girma. Allah Maxaukaki yana cewa:


1 Biharul Anwar na Majalisi, mujalladi na 52 shafi na 338; kuma a duba Kitabul Gaiba na Abu Ja’afar


Muhammad binul Hassan Aldusi, bugun Madabi’ul Nu’uman, ba garin bugu, ba tarihi, shafi na 282.


2 Biharul Anwar, tushen da ya gabata, mujalladi na 52 shafi na 386.


3 Alwafi na Faid Kashani, bugun Almaktabatul Islamiyya, Tehran-Iran, ba tarihi, mujalladi na 1 shafi na 215.


7


“Kuma lalle ne, Xaki na farko da aka aza domin mutane, haqiqa, shi ne wanda ke


Bakka mai albarka kuma shiriya ga talikai.” (Suratu Ali Imrana: 96).


Kuma masallacin Ibrahim wanda ya gina da umarnin Allah shi ne Xakin


Ka’aba, kamar yadda Allah ya bayyana: “Kuma a lokacin da muka iyakance wa


Ibrahim wurin Dakin (muka ce masa), “Kada ka haxa kome da ni ga bauta, kuma


ka tsarkake Xakina, domin masu xawafi da masu tsayuwa da masu ruku’u da masu


sujada. Kuma ka yi yekuwa ga mutane da wajabcin Hajji, su je maka suna masu


tafiya da qafafu da kuma a kan kowane maxankwarin raqumi masu zuwa daga


kowane rango mai zurfi.” (Suratul Hajji: 26-27). Kuma Ubangiji Maxaukaki ya


ce, “Kuma a lokacin da Ibrahim yake xaukaka harsashin gini ga Xakin, da Isma’ila


(suna cewa), “Ya Ubangijinmu, ka karva daga gare mu, lalle ne kai, kai ne mai ji,


mai sani.” (Suratul Baqara: 127).


Dangane da alqibla kuwa, Allah Maxaukaki yana cewa, “Lalle ne, muna


ganin jujjuyawar fuskarka a cikin sama. To lalle ne, mu juyar da kai ga Alqibla


wadda kake yarda da ita. Sai ka juyar da fuskarka wajen Masallaci Tsararre.”


(Suratul Baqara: 144). Watau Masallaci mai Alfarma, Xakin Ka’aba. Har yau,


yana cewa, “Kuma daga inda ka fita, to, ka juyar da fuskarka a wajen Masallaci


Tsararre, kuma inda kuke duka, to, ku juyar da fuskokinku a wajensa.” (Baqara:


150).


Wannan shi ne abinda Alqur’ani mai tsarki yake faxi dangane da qasa mai


tsarki da kuma alqiblar Musulmi wacce ba ta canjawa kuma ba ta sauyawa har


abada. Daga wannan kuma babu wata qasa mai tsarki sai Baitil Maqadis wanda


Allah yake cewa dangane da shi: “Tsarki ya tabbata ga wanda ya yi tafiyar dare da


bawansa da dare, daga Masallaci mai Alfarma zuwa ga Masallaci mafi nisa, wanda


muka sanya albarka a gefensa.” (Suratul Isra:1). Sai kuma Masallacin Annabi


8


(SAW) na Madina. Waxan nan su ne masallatai guda uku masu alfarma waxanda


ambatonsu ya zo a cikin hadisin da Manzo (SAW) yake cewa: “Ba’a xaura sirada


(domin tafiya) sai zuwa masallatai uku kawai: Masallaci mai Alfarma, da


Masallaci Mafi Nisa, da Masallacina wannan.”1


Don haka Karbala ba ta da wata alfarma kuma ba ta da tsarki, sa’an nan


babu bambanci tsakaninta da ko wace irin gama-garin qasa a duniya. Muna roqon


Allah ya buxe basirarmu tare da Shi’awa waxanda ba su yi nisa ba. Ya bayyana


mana gaskiya ya ba mu ikon bin ta. Waxanda suka yi nisa kuma, Allah ya isar wa


Musulunci sharrinsu.


Har yau, wani mugun nufi da Rafilawa suka daxe da shi a zuci kuma suke da


niyyar zartar da shi a aikace, shi ne kashe Musulmi Ahalus Sunna mafi munin kisa


ta yadda ba abinda zai rage a cikinsu sai kaxan. Qasurgumin malamin ‘yan Shi’a


wanda suke yi wa laqabi da Shaikhul Xa’ifa , watau Shaihin Qungiya, mai suna


Abu Ja’afar Muhammad binu Hassan Alxusi, ya ce, “Wannan al’amari (yana nufin


mulkin ‘yan Shi’a) ba zai tabbata ba sai ushuri tara na mutane sun tafi.”2


Duba ka gani, malam mai karatu, wannan qeta da mugun nufi da baqin


alkaba’i da yake cikin zukatan malaman Shi’a da manyan mabiyansu. Mulkinsu ba


zai tabbata ba sai sun kashe ushuri tara na mutane, watau casa’in bisa xari ke nan


(90%).


Ruwayar Majalisi ta fi ban tsoro da kaxa zuciya da tsuma jiki. Ga yadda ya


hakaito daga imaminsu na shida, Abu Abdullahi, wai ya ce, “Da mutane sun san


abinda Mahadi zai yi idan ya bayyana da mafi yawansu sun yi fata kada su gan shi


saboda yawan mutane da zai kashe… Har mutane da yawa za su riqa cewa:


1 Bukhari da Muslim.


2 Duba Kitabul Gaiba na Aldusi, tushen da ya gabata, shafi na 135.


9


Wannan ba ya cikin iyalin Muhammad; da yana cikin iyalin Muhammad da ya yi


jin qai.”1


Idan mai karatu yana so ya san su wane ne waxan nan mutanen da wannan


shu’umin Mahadi, Mahadin Yahudawa da Majusawa, zai kashe, to sai ya koma ga


maganar Ayatullahi Khumaini da muka naqalto a baya kaxan inda ya sarraha da


cewa Ahalus Sunna suke nufi. Muna fata Allah ya raba mu da ganin wannan baqin


Mahadi mai baqar aniya da mugunyar manufa.


Har ila yau, wani mugun nufi da ‘yan Shi’a suka daxe da shi a zuci kuma


suke da niyar tabbatar da shi a aikace, shi ne sauya addinin Musulunci da wani


addinin sabo da sauya Shari’arsa da wata shari’a sabuwa da kuma sauya littafinsa


da wani littafin sabo. Majalisi ya ambata a cikin littafinsa kamar haka: “Mahadi


zai bayyana da al’amari sabo, da littafi sabo, da hukunci sabo.”2


Idan kana da wani kokwanto dangane da wannan sabon al’amari, bari ka ji


ruwayar Kulaini, wanda ‘yan Shi’a suke xaukar sa kamar yadda Ahalus Sunna


suka xauki Imamul Bukhari, daga Abu Abdullahi, imamin Rafilawa na shida, cewa


wai ya ce: “Idan Mahadin iyalin Muhammadu ya bayyana, zai yi hukunci da


hukuncin (Annabi) Dawud da (Annabi) Sulaiman kuma ba zai tambayi shaida ba.”3


E, ba zai tambayi shaida ba; saboda tambayar shaida yana daga cikin sifofin


Musulmi, shi kuwa wannan Mahadin Bani Isra’ila ne ya yafa mayafin iyalin


Muhammadu (SAW), Ahlul Baiti, domin vad da bami. Saboda haka zai bar


Shari’ar Annabi Muhammad (SAW), shugaban Ahalul Baiti, ya kama ta


annabawan Bani Isra’ila.


1 Biharul Anwar na Majalisi, tushen da ya shude, mujalladi na 52 shafi na 303.


2 Biharul Anwar, tushen da ya shude, mujalladi na 52 shafi na 354.


3 Usulul Kafi na Abu Ja’afar Muhammad binu Ya’aqub Alkulaini, ta’aliqin Ali Akabar Gifari, bugun Darul Kutubil


Islamiyya, Teheran-Iran, ba tarihi, mujalladi na 1 shafi na 397.


10


Wannan shi ne mugun nufin ‘yan Shi’a ga al’ummar Musulmi kamar yadda


yake a cikin littafan malamansu waxanda suke izna da su. Kuma cewa wannan


mugunyar manufa sai Mahadinsu ya bayyana za su zartar da ita, wata dabara ce ta


koya wa mabiyansu juriya da haqurin jira da dako. Gaskiyar lamari shi ne, duk


lokacin da dama ta samu, ‘yan Shi’a suka kafa daula, ko suka samu qarfi, to


wannan ne lokacin zartar da wannan manufa. Ba sai Mahadi ya bayyana ba.


Idan mai karatu yana son tabbatar da haka, sai ya koma ga maganar Imam


Khumaini inda yake cewa, jim kaxan bayan kafa Jumhuriyar Islama ta Iran,


“Sayyid Hussain, lokaci ya yi na zartar da wasiyar imamai, amincin Allah ya


tabbata a gare su. Za mu zubar da jinin nasibawa (Ahalus Sunna), mu karkashe


‘ya’yansu maza, mu raya matansu. Ba za mu bar xaya daga cikinsu ya kuvuta ba


daga wannan uquba. Da sannu dukiyoyinsu za su zama ganima ga Shi’ar Ahalul


Baiti. Kuma za mu shafe Makka da Madina daga doron qasa saboda waxan nan


birane biyu sun zama mafakar ‘yan Wahhabiya. Kuma lallai ne Karbala, qasar


Allah mai tsarki, ta zama ita ce alqiblar mutane a cikin sallah. Za mu tabbatar da


burin imamai, aminci ya tabbata a gare su,”1 kamar yadda muka gani a baya kaxan.


Bayan kafa Jumhuriyar Islama ta Iran, ‘yan Shi’a ba su jira zuwan Mahadi


ba, amma sun ci gaba da zartar da mugun nufinsu ga al’umma, kamar yadda za mu


gani a qarshen babi mai zuwa, in Allah ya yarda.


1 Kashful Asrar na Musawi, shafi na 91-92.


11


Babi na Biyu


Baqin Tarihin ‘Yan Shi’a


‘Yan Shi’a suna aiwatar da mugun nufinsu, wanda yake qunshe a cikin


aqidunsu kamar yadda muka gani, a duk lokacin da suka samu damar yin haka.


Koda yake sun dangana yawancin miyagun manufofinsu da bayyanar Mahadi,


amma tarihi ya tabbatar da cewa bayyanar Mahadi a wajensu shi ne kawai samun


iko. A duk lokacin da ‘yan Shi’a suka samu damar kafa daula, ko bayyanar wani


shugabanci mai qarfi, to suna yin amfani da wannan don cimma manufofinsu. Don


haka muke gani a yau, qasar Iran, bayan juyin juya halin Rafilawa, ta zama babban


jigo na fitina da rashin zaman lafiya a qasashen Musulmi, musamman a Gabas ta


Tsakiya.


A wannan babi na biyu, za mu gabatar da misalai na baqin tarihin Shi’a a


qasashe dabam-daban da lokuta dabam-daban.


Kisan Shugabanni da ta da Fitinu


Kasancewar qungiyar Shi’a an kafa ta don yaqar Musulunci daga ciki,


mabiyan tafarkin Rafilanci sun qaddamar da ayyukan ta’addanci a kan Musulmi a


tsawon tarihi. Wannan ya haxa da kashe-kashe da zagon qasa ga marayar Musulmi


da kafa qungiyoyin asiri iri-iri domin yaqar Musulunci da rusa aqidarsa. Wani salo


na yaqi da suka daxe suna yin amfani da shi, shi ne kisan shugabanni


Ba ‘yan Shi’a ne suka fari kisan shugabanni ba a tarihin bil Adama, amma


sun qware a kansa, kuma sun shahara da shi. Wannan ya sa su Turawa daga wajen


su ne suka samu kalmarsu ta assassination, wacce take nufin kisan shugabanni,


kamar yadda za mu gani a nan gaba, in Allah ya yarda.


12


Abu ne da aka sani cewa shugabanni su ne kai ga ko wacce al’umma, kuma


kamar yadda jiki ba shi da amfani idan babu kai, to haka al’umma idan ba ta da


shugabanci. Wannan ya sa ‘yan Shi’a, a matsayinsu na rantsattsun masu gaba da


Musulunci, suka mayar da kisan shugabannin Musulmi sana’a wacce suka shahara


da ita


Shugaba na farko da suka kashe a tarihin Musulunci shi ne Sarkin Musulmi


Umar binul Khaxxabi, Allah ya qara masa yarda. Abu Lu’ulu’atal Majusi ne ya


kashe shi domin rama gayya ga rushe daular Farisa ta Majusawan Iran da khalifan


ya yi. Abu Lu’ulu’ata Bamajuse ne da aka ribato shi a wajen yaqi, kuma ya zama


bawan Sahabin Annabi, Mugira binu Shu’uba, Allah ya qara masa yarda, yana


zaune tare da shi a Madina. Ya shiga sahun sallah a Masallacin Annabi(SAW) da


asuba, ya soki Umar da wata wuqa mai baki biyu wacce ya sa mata dafi, a lokacin


da Umar yake limancin mutane a cikin sallah. Sa’an nan ya yi ta sukan masallata


dama da hagu sai da ya soki mutum goma sha uku, waxanda bakwai daga cikinsu


suka yi shahada.


Saboda wannan aika-aika da ya yi, ‘yan Shi’a na ko wane zamani suna


xaukar Abu Lu’ulu’ata a matsayin gwarzo, kuma suna yi masa laqabi da Baba


Shuja’uddin, watau Baba Sadaukin Addini! Gwamnatin Musulunci (wai ma!) ta


qasar Iran ta gina masa Hubbare a birnin Kashana dake tsakiyar qasar. Wannan


Hubbare da ta qunshi makeken gini mai babbar qofa, ma’abota jahilci suna ziyarar


ta daga ko ina a duniya domin tunawa da Bamajuse Abu Lu’ulu’ata da babban


aikin da ya gabatar na kashe Khalifa Umar! Har yau, gwamnatin qasar Iran ta


sanya hoton wannan Hubbaren a kan irin katin nan na aikewa da saqo (postcard)


da kuma kan-sakri na aike wasiqu (stamp) don a yaxa ta kuma a jawo hankalin


masu ziyara, da masu yawon buxe idanu, zuwa gare ta.1


Mai son ya ga hoton Hubbaren Abu Lu’ulu’ata sai ya shiga sashen Google


na yanar gizo, ya sanya sunan “Abu Lu’ulu’ah” ko “Fairuz” sa’an nan ya latsa. Zai


ga abin mamaki. Mai karatu, me zai hana ka gwada don ka gane wa idanunka!


Shugaba na biyu da Rafilawa suka kashe shi ne Sarkin Musulmi Usmanu


binu Affan, Allah ya qara masa yarda. Abdullahi binu Saba’i Bayahude, wanda ya


aza tubalin farko na ginin tafarkin Shi’anci, shi ya fari fitinar da ta kai ga kisan sa.


1 A duba Kashful Asrari na Musawi, tushen da ya shude, shafi na 88.


13


Kashe-kashen Rafilawa ga shugabannin Musulunci bai tsaya a kan Sahabbai


da magabatan Ahalus Sunna ba kawai, a’a ya haxa har da imaman Shi’a da


shugabannin Ahalul Baiti. Mafi shahara a cikinsu shi ne Imam Hussaini, Allah ya


qara masa yarda, wanda mabiyansa ‘yan Shi’a ne suka yi sanadin mutuwarsa.1


Haka nan, su suka yi sanadin mutuwar Imaminsu na bakwai, Imam Musa Alkazim,


kamar yadda su da kansu suka tabbatar.2


A taqaice kisan shugabanni, ko kuma abinda ake kira da Turanci


assassination, ya zama wata hanya ta yaqar Musulunci wacce Rafilawa suke


amfani da ita a ko wane zamani. A nan kusa-kusa sun kashe manyan malamai


kamar su Muhammad Hussaini Azzahabi mai littafin Attafsiru wal Mufassirun da


Ihsan Ilahi Zahir sanannen marubuci xan qasar Pakistan wanda ya shahara da


rubutu a kan ‘yan Shi’a. Kamar yadda suke kashe duk wani malaminsu da ya tuba


ya koma Sunna irin su Sayyid Ahmad Kasarawi da Dr Musa Musawi wanda ya


rubuta littafin A Critical Revision of Shi’ah yana kira da a yi gyara a tafarkin


Shi’anci.


A nan Nijeriya, a cikin ‘yan shekaru kaxan da suka gabata, ‘yan Shi’a sun


kashe malamai, na qarshensu Malam Umaru Xan Maishiya wanda suka kashe a


Sakkwato. Wataqila ba zai zama adalci ba idan muka dangana wa ‘yan Shi’a kisan


Malam Ja’afar kai tsaye; saboda shi yana da maqiya masu yawa. Amma muna iya


dangana musu kisan Malam Umar Xan Mai Shiyya saboda shi ba shi da abokan


gaba sai ‘yan Shi’a.


Kuma ina cikin gyaran wannan littafi don miqa shi ga masu bugu, sai aka


qara tafka ta’asar kisan gilla ga Malam Muhammad Auwal Adam Albani a ranar


Asabar 1 ga watan Rabi’ul Thani, 1435/ 1 ga Fabrairu, 2014. Muna roqon Allah


Maxaukaki ya karve shi a cikin masu shahada waxanda suka bi turbar annabawa


da magabata na-gari.


“Ya Ubangijinmu, ka yi gafara gare mu, kuma ga ‘yan uwanmu waxanda


suka riga mu yin imani, kada ka sanya qulli a cikin zukatanmu ga waxanda suka yi


imani. Ya Ubangijinmu, lalle kai mai tausayi ne, mai jinqai.”(Suratul Hashri: 10).


1 Duba littafinmu, Wa Ya Kashe Hussaini? bugun Zomo Press, Kaduna, 2010, shafi na 7-18.


2 Duba Rijalul Kasshi na Muhammad binu Umar Alkasshi dan Shi’a, shafi na 229.


14


Shaihu Ali Muhammad Sallabi ya zana wani kwami da sunayen


shugabannin Musulunci waxanda ‘yan Shi’a suka kashe a zamuna dabam-daban,


da qasashe dabam-daban, a qarshen litafinsa mai suna Daulatus Salajiqah. Kwamin


ya qunshi sunayen fitattun shugabanni 42 waxanda suka haxa da khalifofi da


sarakuna da alqalai da kwamandojin soji da manyan malamai da attajirai.1


Imam Suyuxi ma ya zana sunayen shugabannin Musulmi da ‘yan Shi’a suka


yi wa kisan gilla a cikin littafinsa, Tarikhul Khulafa.


Abinda wannan yake nunawa shi ne cewa, ‘yan Shi’a an san su da sana’ar


kisan shugabannin Musulmi waxanda ba sa bin tafarkinsu, musamman Ahalus


Sunna waxanda suke ganin jininsu ya halatta.2


Haddasa Fitina A Tsakanin Musulmi


Rafilawa suna xaukar haddasa fitina tsakanin Musulmi a matsayin wata


hanya ta yaqar Musulunci da qoqarin rusa shi. Kuma wannan abu ne da suka


shahara da shi a tsawon tarihi. Fitina ta farko da suka haddasa ita ce tawayen da


aka yi wa Sarkin Musulmi Usmanu binu Affan(RA) wanda ya qare da kisansa


kisan gilla, kuma ya haifar da faruwar savani a tsakanin al’umma wanda ya kai ga


yaqoqa masu yawa. Yaqin Jamal da yaqin Siffain da yaqin Nahrawan, da wasu


gomomi da xaruruwan yaqoqa da suka biyo bayan waxan nan, duka sakamakon


fitinar Abdullahi binu Saba’i ce wanda ya assasa tafarkin Shi’a.


Wani salon fitina da ‘yan Shi’a suka shahara da shi, shi ne taimakon kafirai a


kan Musulmi koda yaushe yaqi ya tashi a tsakanin vangarorin biyu. Misalan irin


wannan aiki nasu ba za su qidayu ba, amma wanda ya fi shahara a tarihi shi ne


yaqin Tattar a kan Bagadaza.3 A wannan zamani da muke ciki ya tabbata cewa


Rafilawan Iran sun taimaka wa Amurkawa da sauran kafiran Turai a kan yaqin


Afganistan da Iraqi, banda samar da makamai da horon soji ga qungiyoyin Shi’a


‘yan ina-da-kisa na Iraqi waxanda suke karkashe Ahalus Sunna na qasar. Waxan


nan duka abubuwa ne waxanda suke an tabbatar da su ta hanyar bincike na zahiri,


1 Duba Daulatus Salajiqah na Sallabi, bugun Darul Ma’arifa, Bairut, 1430/2009, shafi na 654-656.


2 Domin ganin fatawoyin malaman Shi’a da nassoshin imamansu da suke nuna halaccin jinin Musulmi a addinin


Shi’a, sai a duba littafinmu, Matsayin Musulmi a wajen ‘Yan Shi’a.


3 Za mu fayyace bayani a kan wannan a nan gaba kadan, in Allah ya yarda.


15


kuma bayanansu suna nan a cikin kundayen bincike na hukumomi da qungiyoyi


daban-dabam.


Kafa Qungiyoyin Asiri


Wani salon ta’addanci da ‘yan Shi’a suka xauka don yaqar Musulunci shi ne


kafa qungiyoyin asiri domin yaxa hayaniya da dambarwa da vata aqidojin


Musulunci da hana zaman lafiya a marayar Musulmi. Baqin tarihin Shi’a yana cike


da irin waxan nan qungiyoyi.


Wataqila mafi daxewa kuma mafi sharrin waxan nan qungiyoyi ita ce


qungiyar Isma’iliyya. ‘Yan wannan qungiya suna dangana kansu ga Isma’il binu


Ja’afar Sadiq, xan imamin Shi’a na shida, kuma sun yi qaurin suna da yawan


tashin-tashinar siyasa, tawaye da bore da kisan shugabanni. Bayan sun yi tawaye


ga imamin Shi’a na bakwai, Musa binu Ja’afar Sadiq, sun goyi bayan xan uwansa


Isma’il, shi ma sun ya da shi suka koma ga Almusta’ali Billah, khalifan Faximawa


‘yan Shi’a na tara a Misira, wanda shi ma suka yi masa tawaye qarqashin


jagorancin shaqiqinsa, Nizar binu Ma’ad, suka kafa wata ‘yar qaramar daula a


garin Iskandariyya na Masar.


A shekarar 1090 miladiyya, wannan ‘yar daula tasu ta rushe, sai suka yi


qaura qarqashin jagorancin shugabansu, Hassan binul Sabbah, zuwa lardin


Almautu na qasar Iran inda suka kafa qungiyar ta’addanci ta Hasshashun. Wannan


suna nasu an samo shi daga kalmar hashish wacce take nufin ganye, watau wiwi,


wanda ake sha don buguwa.


A wannan lokaci ne Isma’iliyya suka kai qololuwar ta’addancinsu, inda suka


bazu a dazuka da kan duwatsu, suna tare hanya, su kashe maza, su kame mata da


yara, su kora dabbobi waxanda suke gasawa su ci bayan sun yi maye. Idan wani


sarki ko hakimi ko mai mulki ya yi qoqarin magance ta’addancinsu, sai su aike


wanda zai yi shigar burtu ya kashe shi kisan gilla. Daga nan sunan hasshashun ya


yi dai-dai da masu kisan shugabanni, wanda Turawa suka ara suka mayar


assassins. Wannan sai ya zama wani abin “alfahari” a cikin baqin tarihin ‘yan


Shi’a cewa su ne suka koya wa Turawa, sarakan kisa, yadda ake kashe shugabanni!


16


A wannan zamani namu, qungiyar Isma’iliyya ta rikixe, ta fito da sunan


Agha Khan Foundation, inda take gina makarantu da asibitoci, tana da’awar


taimakon Musulmi marasa galihu, amma manufarta ita ce juye kansu da vata


aqidarsu. Turawa ‘yan mishan sun rungumi wannan qungiya (hedukwatarta tana


London) kamar yadda suka rungumi qungiyar Ahmadiyya, saboda manufarsu xaya


ce.


Cibiyar Agha Khan tana gudanar da nashaxinta yawanci a gabashin Afrika.


Na gani da idona irin makarantu da asibitoci da take ginawa a qasashen Uganda da


Kenya da Tanzaniya. A vangarenta na Turai kuwa, cibiyar tana lulluve ayyukanta


da mayafin bincike na ilmi da kimiyya, kamar yadda cibiyoyin Yahudawa masu


miyagun manufofi suke yi. A shekarar 2011, wannan vangare na qungiyar ya bai


wa sarkin Masarautar Qaxar dake Tekun Fasha “Lambar Yabo ta Inganta Gineginen


Musulunci Masu Tarihi.” Wannan wata hanya ce da qungiyoyin ta’addanci


(irin ta’addancin da kafiran Turai suke maraba da shi) suke sa wa kawunansu rigar


mutunci, kuma kafafen labarai na duniya su riqa kambama su, don su ji daxin


zambatar gafalallu.


Banda ta’addanci na kashe-kashe, qungiyar Isma’iliyya ta qaddamar da


ta’addancin aqida kuma, inda ta shigo da miyagun aqidu na Maguzanci cikin wasu


qungiyoyin Musulmi. Aqidar Faila ta ‘yan Tijjaniyya, ko kuma mu ce ‘yan


Inyasiyya, tana cikin irin waxan nan aqidu.1


Wata qungiyar ta’addanci da Rafilawa suka kafa ita ce qungiyar


Qarmaxiyya. Wanda ya kafa wannan qungiya shi ne Qarmax Hamdan. Asalinsa


daga lardin Khuzistan na qasar Iran yake, ya valle daga qungiyar Isma’iliyya,


kuma ya yi qaura zuwa Kufa a Iraqi inda ya kafa tasa qungiyar. Yawancin


ta’addancin Qarmaxiyya na aqida ne. Ita ce ta xauki tutar yaxa aqidar Baxiniyya


wacce take koyar da cewa Alqur’ani yana da ma’ana biyu: ta voye da ta sarari,


kuma babu wanda ya san ta voyen daga imaman Shi’a sai gausayen Xariqa.2


Addinin Baha’iyya shi ma ya samo asali daga aikin ta’addancin aqida na


‘yan Shi’a. Wanda ya kafa wannan addini shi ne Baha’ulla, wanda ya rayu tsakanin


1 Domin ganin dangantakar akidun Shi’a da Darika sai a duba Muqaddimatu Ibni Khaldun na Abdurrahman binu


Khaldun, bugun Darul Kutubil Ilmiyya, Bairut, 2003, shafi na 254 da 386. Kuma domin darasun tushen akidar Faila


a cikin kungiyar Isma’iliyya, sai a duba Altuhfatus Saniyya na Dr Tahir Maigari, shafi na 133. Na fassara wannan


littafin zuwa harshen Hausa da taken Jana’izar Tijjaniyya. Littafin ya fito a shekarar 2015; nemi kwafenka.


2 Domin karin bayani, duba littafinmu Bankaurar Sufaye.


17


shekarun 1817 zuwa 1892. An haife shi a birnin Teheran na Iran, kuma ya rasu a


garin Akka a kan gavar kogin Bahar Maliya. Asalin Baha’ulla xan Isma’iliyya ne,


amma daga bisani ya yi shelar kafa sabon addini mai zaman kansa. Aqidojin


wannan addinin da ibadojinsa gamin-gambiza ne na aqidun Musulunci da


Kiristanci da tsoffin addinan Gabas Mai Nisa, kamar Budanci da Barhamanci da


Komfusanci da sauransu. Suna gina xakin ibada a kewaye kamar rumbu, babu


mihirabi ko alqibla, saboda su sama suke kallo idan suna sallah.


Turawan mulkin-mallaka suna yabon Baha’iyyanci saboda, a faxinsu, yana


da sassauci kuma ya tattare alheran dake cikin dukkan addinai!! Yahudawa ma


suna tallan wannan addinin, suna taimaka masa da dukiya, saboda ya dace da


manufarsu ta yaqar Musulunci. A yau, hedukwatarsa ta duniya tana can a kan


dutsen Mount Carmel dake bayan garin Haifa a Isra’ila.


Durzawa, ko kuma Duruz, wata tsohuwar qungiyar ta’addanci ce da ‘yan


Shi’a suka kafa. Ta shahara da yin biyayya ga khalifan Faximawa ‘yan Shi’a na


shida, Alhakim bi Amrillah, wanda ya yi mulkin Misira tsakanin shekarun 996


zuwa 1021 miladiyya. Bayan raunin daular Faximawa, Durzawa sun zauni


duwatsun Lebanon inda suka mayar qasarsu har zuwa yau. Sun taimaka wa


Yahudawan Isra’ila a kisan qare-dangin da suka qaddamar a kan Falasxinawa a


Lebanon a shekarar 1982, kuma a yau su ne qashin bayan qungiyar ta’addanci ta


Hizbullah wacce Hassan Nasarallah yake jagoranta. Qungiyar Hizbullah ‘yan


Shi’ar Nijeriya qarqashin jagorancin Zakzaki suna da alaqa ta qut-da-qut da ita.


Har ma idan suka fito jerin gwanonsuna Maulidi, wanda wasu ‘yan xariqa da


Kiristoci suke taimaka musu, sukan xaga tutocin qungiyar don bayyana wannan


alaqar a fili.1


Wani abu da bai kamata mu wuce ba tare da mun ambace shi ba, shi ne cewa


vurvushin Durzawa suna nan a cikin mutanen nan da muke kira Kwarori waxanda


suke zaune a Nijeriya, musamman a biranen Kano da Ikko. Kuma koda yake suna


kauwame kansu, ba sa gauraya da mutane ta hanyar auratayya ko mu’amala, amma


babu laifi mu yi gargaxi da cewa suna xauke da aqidar Shi’a kuma suna taimakawa


wajen yaxa ta a fakaice.


1 Duba hoton ‘yan Shi’a suna dauke da tutocin Hizbullah a jaridar Daily Trust, fitowar Talata, 22 ga watan Mayu,


2012, shafi na 3.


18


Taimakon Kafirai wajen Yaqar Musulmi


Daga cikin abinda ‘yan Shi’a suka shahara da shi a baqin tarihinsu akwai


taimakon kafirai a wajen yaqar Musulmi, da cin qasashensu, da take haqqoqinsu,


da zubar da jininsu, da keta alfarmarsu. Wannan qaramin littafi ba zai iya tattare


abinda ya faru ba a wannan fanni, amma za mu ba da misali guda kawai.


A wajejen qarshen daular Abbasiya a qarni na bakwai bayan hijira, an yi


wani sarki Mushriki mai suna Holako, sarkin Tattar. Wannan sarki ya yaqi daular


Musulmi mai faxi, ya riqa cin gari bayan gari. Duk garin da ya ci yana rushe shi


baki xaya, ya kashe mazauna garin, ya qone gidaje da gonaki da dabbobi, ba ya


barin kome. Saboda tsananin varnar waxan nan kafirai, har wasu mutane a


zamanin sun zaci ko yajuju da majuju ne suka bayyana. Amma duk da haka,


babban birnin daular Musulmi, watau Bagadaza, tana yi wa wannan sarkin kwarjini


saboda girmanta da yawan mutanen dake cikinta da kuma qarfin sojan dake tsaron


ta. A wannan lokaci, duk duniya babu birni kamar Bagadaza. Don haka da ya iso


qasar Farisa sai ya tsaya yana tararrabi, yana shawara ya kawo wa Bagadaza hari


ko a’a.


A wannan lokaci Sarkin Musulmi shi ne Musta’asim, Khalifa na qarshe a


daular Abbasiya. Babban wazirinsa mai suna Muhammad binu Ahmad binu


Alqami xan Shi’a ne amma masu mulki sai suka yi sakaci da shi tun yana saurayi,


ya yi ta hawa muqamai har ya kai matsayin waziri. Saboda iya munafunci da


amfani da taqiya, Binu Alqami ya samu amincewar kowa a wannan daula. Amma


duk tsawon shekaru, shi dama yake jira ta rusa daular. Sai zuwan Holako da


rundunarsa ya ba shi wannan damar.


Binu Alqami ya aike wa Holako da bayanan sirri a voye, ya yi bayanin


raunin daular kuma ya yi alqawarin taimakon maharan da sharaxin cewa za su kafa


19


daular Shi’a bayan sun kawar da Khilafar Abbasiya. Lokacin da rundunar Tattar


suka iso Bagadaza suka kafa sansani a bayan gari, Khalifa Musta’asim ya tsorata


ainun, amma sai wazirinsa ya kwantar masa da hankali kuma ya nemi izini ya fita


zuwa sansanin abokan gaba domin neman sulhu da su. Bayan ya je ya qara


tabbatar da yarjejeniyarsa ta sirri da Holako, sai ya komo wajen sarkin Musulmi da


wata qarya. Ya ce Holako ya yi farin ciki da zuwansa, ya amince da sulhu da barin


yaqi kuma har ma yana son ya aurar da xiyarsa ga xan sarkin Musulmi, Yarima


mai jiran gado Abubakar. Sarki ya yi murna, aka sa ranar da za a je xaurin aure


kuma daula duka ta fita zuwa sansanin Holako domin yin shagali.


Babu wanda aka bari a baya, Sarki da Yarima da manyan wazirai da


kwamandojin soja da malamai da limamai da alqalai da attajirai da duk wani mai


faxi a ji sun fita baki xaya. Isarsu sansanin Holako ke da wuya, da ma ya shirya.


Sai ya sa aka kange mafita duka aka yanke shugabannin nan baki xaya, sai


abokinsu waziri Binu Alqami kawai ya rage. A yammaci guda sai Bagadaza, da


sauran al’umma, suka zama jiki ba kai.


Su kuwa yajuju da majuju suka shiga aiki. Kwana arba’in suna kisa, suna


qone gidaje da kasuwanni da masallatai da makarantu da xakunan karatu (laburare)


sai da kogin Dajla ya rikixe ya zama ja saboda jini. Suka kame mata da yara, suka


yi ta zina da mata sharifai Hashimawa a cikin masallatai.


Wannan shi ya kawo qarshen daular Abbasiya wacce ta yi shugabancin


duniya xaruruwan shekaru kuma daga nan Musulmi ba su sake samun wannan


matsayi ba na shugabancin duniya. Mutum miliyan xaya da dubu xari takwas


20


(1,800,000) ne suka rasa rayukansu a wan nan kisan kiyashi wanda tarihi bai tava


ganin irinsa ba.1


Marubucin tarihi xan Shi’a mai suna Mirza Muhammad Baqir Khuwansari,


ya kawo wannan qissa a cikin littafinsa, Raulatul Jannat, yana yabon Waziri Binu


Alqami a kan wannan xanyen aiki da ya tafka, kuma ya ce waxanda suka rasa


rayukansu duka suna cikin wutar Jahannama.2 Ayatullahi Khumaini ma ya yaba


wa wannan xan ta’adda, maci amana, kuma ya xauki wannan mummunan aiki nasa


a matsayin babbar hidima ga Musulunci!! Don haka ba ya ambaton sa sai ya ce:


Raliyallahu Anhu, watau Allah ya yarda da shi!3


Wannan yana nuna cewa qissar ba qage aka yi wa ‘yan Shi’a ba; su ma sun


san da ita, sun yi na’am da ita, kuma sun tabbatar da ita a cikin littafansu.


Qaryar Gwagwarmaya ta Qare


Yawancin ‘yan Shi’ar Nijeriya an yaudare su zuwa shiga qungiyar da sunan


GWAGWARMAYA. An nuna musu cewa juyin juya halin qasar Iran na shekarar


1979 juyi ne na Musulunci, kuma manufarsa ita ce qwato haqqin Musulmi da


yaqar zalunci da tabbatar da adalci.


Malam Ibrahim Zakzaki da maqarrabansa, tare da wasu ‘yan boko da wasu


malaman addini masu jimirin sauyi, duka an yaudare su da wannan farfaganda. Sai


suka xauki qasar Iran a matsayin wata jarumar qasa mai bajinta, wacce ta fito


1 Domin ganin wannan kissa, sai a duba Albidaya wal Nihaya na Abul Fida Isma’il binu Kathir, bugun Darul


Kutubil Ilmiyya, Bairut, 1408/1988, mujalladi na 9 shafi na 154; da Almuntaqa min Minhajil I’itidal na


Muhammad binu Uthman Alzahabi, ta’aliqin Muhibbuddin Alkhadib, bugun Maktabatu Daril Bayan, ba tarihi,


shafi na 298.


2 Duba Raulatul Jannat fi Ahwalil Ulama’i was Sadat na Muhammad Baqir Alkhuwansari, bugun Bairut, 1991,


shafi na 578.


3 Duba Kashful Asrar na Sayyid Hussain Musawi, tushen da ya shude, shafi na 90.


21


domin yaqar qasar Yahudu ta Isra’ila da uwargijiyarta Amurka. Ta haka ne, kuma


sannu a hankali, da yawa daga cikin waxan nan mutane suka shiga Shi’a ba tare da


sani ba.


A yau, bayan kimanin shekaru 35 da juyin juya halin na Iran, mahukuntan


qasar ‘yan Shi’a sun yaye mayafin yaudara da taqiyya, kuma sun fito fili suna nuna


mugun nufinsu na yaqar Sunna da yaxa mugunyar aqidarsu ta Shi’a. A yau tarihi


yana maimaita kansa, inda ta’addancin ‘yan Shi’a ya fito fili kuma qiyayyarsu ga


wannan al’umma ta bayyana a sarari. Qasar Iran da masu goyon bayanta a ko ina a


duniya su ke kan gaba wajen yaqar Ahalus Sunna da zubar da jininsu da taimakon


kafirai a kansu.


A nan za mu ba da misalai kaxan na irin wannan ta’addanci don masu


hankali su lura. Amma bari mu fara da bayanin rayuwar Ahalus Sunna a qasar Iran


bayan juyin juya halin ‘yan Shi’a.


Rayuwar Ahalus Sunna A Qasar Iran


Mutane da dama ba su da masaniya cewa akwai Ahalus Sunna masu yawa


dake rayuwa a qasar Iran saboda rashin jin xuriyarsu. Wannan kuwa ya faru ne a


dalilin danniya da take haqqi wanda gwamnatin Iran ta Shi’awa take yi musu.


Bayan samun nasarar juyin juya halin Iran, shugabannin Shi’a sun fara da


zartar da mugun nufin su a kan Ahalus Sunna na qasar, kafin su mayar da


hankalinsu ga sauran Musulmi na wasu qasashe. Bayanai da alqaluma masu


biyowa, waxanda suka fito daga kafafen gwamnatin Iran ita da kanta, suna tabbatar


da haka.


22


A gwargwadon qididdigar san-san ta shekarar 2008, adadin mutanen Iran ya


kai miliyan sittin da biyar, da dubu xari takwas da saba’in da biyar, da xari biyu da


ishirin da uku (65,875,223). A cikin wannan adadi, kimanin miliyan 20 Ahalus


Sunna ne. Gamin gambizar addinan qasar ya kasance kamar haka: Rafilawa: 65%,


Ahalus Sunna: 25%, Yahudawa da Kirista da Majusawa: 10%. Yawancin Ahalus


Sunna na qasar sun kasu izuwa qabilun Qurdawa da Balushawa da Turkumawa.


Akwai Larabawa kaxan a yankin qasar da ake kira Arabistan. Amma yawancin


‘yan Shi’a su Farisawa ne.


Tun kafin juyin juya halin Iran, Ahalus Sunna, kasancewarsu ba Farisawa


ba, sun fuskanci danniya da take haqqi. Wannan ya sa wasu daga cikin su suka


goyi bayan juyin da fatan za su samu sa’ida, amma bayan cin nasara sai Khumaini


ya juya musu baya har suka qwammace gidan jiya. Yawancin shugabannin Ahalus


Sunna da suka marawa juyin baya, kamar su Shaihu Ahmad Mufti Zadah, Imam


Khumaini ya sa an rataye su.


Duk da yawan Ahalus Sunna (kimanin rubu’in ‘yan qasa), kundin tsarin


mulkin qasar bai san da su ba. Maimakon haka, kundin ya bayyana qarara cewa


qasar tana bin tafarkin Shi’awa ‘Yan Dozin. A majalisar qasar mai wakilai 290,


Ahalus Sunna kujeru 12 kawai aka ba su. Wannan yana nufin cewa, ko wane xan


majalisa xaya Ahalus Sunna yana wakiltar kimanin mutane miliyan xaya da rabi


ke nan, a yayin da ko wane wakili xan Shi’a yake wakiltar Shi’awa 200,000 kacal.


Zaluncin wannan tsari ba sai an faxi ba. A haqiqa ma, waxannan kujeru 12 an


bayar da su ne kawai saboda a yi talla da cewa an bayar; idan ba haka ba me 12 za


ta yi a cikin 290?


Babu ‘yancin addini ga Ahalus Sunna na Iran. An haramta musu gina


masallatai a manyan biranen qasar, kamar Asfahan da Shiraz da Yazd. A babban


23


birnin qasar, Tehran, inda ake da Musulmi Ahalus Sunna miliyan guda, an haramta


musu gina masallaci koda guda xaya, a yayin da aka qyale Yahudawa da Kirista da


Majusawa suka gina wuraren ibada xai-xai ko wannensu. Masallatan Ahalus


Sunna da aka ba su damar ginawa a qauyuka da yankunan karkara suna qarqashin


kulawar hukuma ta dun-dun-dun. Haka nan kuma an haramta musu kafa makarantu


na kansu.


A taqaice, Ahalus Sunna a Iran an haramta musu kafatanin haqqoqinsu na


‘yan qasa. A yau, su suka fi kowa ci baya da jahilci da talauci da rashin aikin yi a


qasar.1


Tarihi Yana Maimaita Kansa


Bayan gwamnatin juyin juya hali ta Iran ta shimfixa tsarin danne Ahalus


Sunna a cikin gida, kuma a lokaci guda ta girke na’urar farfaganda domin farauto


na waje, sai ta shiga qaddamar da aikin Shi’a na tarihi: yaqar Musulunci da rushe


tafarkin Sunna.


Kuma da yake a yanzu kixa ya sauya, to sai rawa ma ta sauya. Don haka a ci


gaba da wannan yaqi na tarihi, qasar Iran a matsayinta na mai riqe da kambin yaxa


tafarkin Shi’a a duniya a yau, ta fara da ware dukiya mai yawa, wasu rahotanni


suna faxin kimanin kashi goma bisa xari (10 %) na dukkan dukiyar qasar, don


wannan manufa. (Kada a mance Iran tana cikin qasashe huxu da suka fi yawan


arziqin man petur a duniya.) Ta kafa cibiyoyi na qasa da qasa, kuma ta buxe sassa


a dukkanin ofisoshin jakadancinta dake qasashen qetare don tabbatar da wannan


aiki.


1 Alkaluman da muka bayar a sama sun fito daga Kamfanin Dillancin Labarai na Iran, IRNA. Dangane da sauran


bayanai kuma, sai a duba littafin Alshi’atu Shahidina Ala Anfusihim na Liya’uddin Alkashif, bugun Maktabatu


Ahlil Bait, 1428/2007; da littafin Ahawalu Ahalis Sunna fi Iran na Abdulhaqq Al’asfahani.


24


Sa’an nan qasar Iran ta kafa qawance da ‘yan Shi’a na sauran qasashe,


waxanda ta zama uwa a gare su, su kuma suka zama ‘ya’ya masu biyayya, saboda


haxa qarfi waje guda da samar da wani gagarumin yunquri don farfaxo da yaqin


tarihi tsakanin Sunna da Shi’a wanda ya fara tun a zamanin Sahabbai, lokacin da


aka rushe daular Farisa a qarqashin jagorancin Sarkin Musulmi Umar binul


Khaxxabi, Allah ya qara masa yarda.


Sabon yaqin Shi’a a wannan zamani ya haxe kafatanin fagage: fagen siyasa


da diflomasiyya, fagen tattalin arziki, fagen ilmi da al’adu, da kuma fagen fama.


Haka nan ya haxe dukkan nau’in makamai: makamin kuxi da abin duniya,


makamin kafafen bayanai da yaxa labaru, makamin mutu’a da taqiyya, da


makamin kisa wanda ya fara daga bindiga da bam har ya zuwa nukiliya.


Sabon Ta’addancin Shi’a


A da, qasashen Turai da Amurka suna zargin Iran da cewa ita qasa ce ta


‘yan ta’adda, mai xaurewa ta’addanci gindi, Musulmi na jin ciwo. Sai ga shi


wannan zargi ya bayyana a zahiri, ta yadda duk mai idanu yake iya gani. Sai dai


abin mamaki, a yanzu qasar Amurka tana maraba da ta’addacin Iran; saboda ta lura


cewa yawancin ta’addancin nata a kan qasahen Musulmi mabiya Sunna yake


qarewa. A yau, babu wata qasa a duniyar Musulmi wacce ta’addancin Iran bai


addabe ta ba. Ga ‘yan misalai:


Lebanon: Wannan qasa ita ce mazaunin qungiyar Hizbullah, qungiyar ta’addanci


mafi qarfi a Gabas ta Tsakiya, wacce kuma ita ce hannun daman qasar Iran wanda


take amfani da shi a wajen ayyukanta na ta’addanci a qasashen duniya.


Suriya ko Sham: Qasar Iran tana taimakon gwamnatin Bashar Asad ta tsuraru ‘yan


Shi’a wacce take kafsa yaqi da ‘yan tawaye masu bin tafarkin Sunna, waxanda


kuma su ne mafiya rinjaye, tun farkon shekarar 2011. Gwamnatin Asad ta dogara


kacokan da taimakon Iran, na kuxaxe da makamai da diblomasiyya da qwararrun


soji masu ba da shawara, wajen ta’addancinta a kan ‘yan qasarta wanda ya haxa da


25


rushe kimanin kashi biyu bisa uku na dukkan biranen qasar, kashe sama da mutane


dubu xari biyu da hamsin, kore sama da miliyan shida daga gidajensu, da amfani


da muggan makamai waxanda aka haramta a dokokin qasa da qasa.


Yaman: Qasar Iran tana taimakon ‘yan tawayen Hutsawa marasa rinjare, masu bin


tafarkin Shi’a, a qoqarinsu na vallewa daga qasar Yaman da kafa qasarsu ta ‘yan


Shi’a.


Iraqi: Iran ta taimakawa ‘yan Shi’ar Iraqi wajen kafa qungiyoyin ina-da-kisa


waxanda suka taimaki sojojin Amurka a kan kifar da gwamnatin Saddam Hussaini


da rushe biranen mabiya Sunna, kamar birnin Falluja, da karkashe su mafi munin


kisa. A matsayin sakamako, qasar Amurka ta taimaka wa ‘yan Shi’a su mulki


qasar Iraqi da da’awar cewa wai su ne masu rinjaye.


Baharain: Iran tana tallafawa ‘yan Shi’ar qasar Baharain, waxanda suke da’awar su


ne masu rinjaye wai amma mabiyan Sunna suna mulkinsu mulkin danniya. Yau


kimanin shekaru biyar ke nan babu zaman lafiya a qasar. Shekaru biyu da suka


wuce, ‘yan Shi’ar sun kusa yin nasarar tankwave gwmnatin qasar ba don taimakon


qasar Sa’udiyya ba gare su.


Nijeriya: A cikin watan Oktoba, 2010, jami’an tsaro sun kama kontena goma sha


uku maqare da miyagun makamai a tashar jiragen ruwa ta birnin Legas. Bincike ya


tabbatar da cewa waxan nan makamai sun fito ne daga qasar Iran, kuma ofishin


jakadancin qasar a Abuja ya amsa cewa xaya daga mutanen da aka kama da


makaman ma’aikacinsu ne. Bayan shari’a da ta xauki sama da shekaru biyu, an


samu mutane biyu da laifi, ciki har da jami’in jakadancin na Iran, kuma kotu ta


xaure su shekaru 17 ko wannensu.1


A cikin watan Fabrairy, 2013, jami’an leqen asiri na Nijeriya sun cafke wasu


samari da suka yi karatu a qasar Iran, suna shirin kai hare-haren ta’addanci da


nufin kashe wasu shugabannin Musulmi na qasar nan, ciki har da tsohon shugaban


mulkin soja Ibrahim Babangida, da Sarkin Musulmi mai murabus, Sultan Ibrahim


Dasuqi. Bayan bincike, ya tabbata cewa waxan nan samari suna yi wa qungiyar


1 Domin ganin wannan labari, duba jaridar Dailay Trust, fitowar 15 ga watan Mayu, 2013, shafi na 46.


26


ta’addanci da Iran ke mara wa baya, watau Hizbullah, aiki. Jaridun qasar nan da


kafafen yaxa labarai na qasashen qetare duka sun ruwaito wannan labari.1


Haka nan, a wannan shekara dai ta 2013, an gano makamai masu yawa voye


a wani gida a birnin Kano. Bayan bincike, an zargi wasu qwarori ‘yan qasar


Lebanon, waxanda ake jin suna da alaqa da qungiyar Hizbullah, da mallakar


waxan nan makaman.2 Har yanzu maganar tana kotu.


Wannan qungiya ta Hizbullah, wacce take adana makamai a Kano saboda


mugun nufi ga Musulmin qasar nan, ‘yan Shi’ar Nijeriya qarqashin jagorancin


Ibrahim Alzakzaki suna xaga tutar ta a fili a cikin jerin gwano da suke gudanarwa


a biranen qasar na.3


Abinda muka ambata a nan xan misali ne kawai na sabon ta’addancin ‘yan


Shi’a da uwargijiyarsu, qasar Iran, da kuma mugun nufi wanda suke qudure da shi


ga wannan al’umma. Muna roqon Allah ya tsare mu da sharrin bidi’a wacce take


sunce imanin mutum ba da saninsa ba.


Muhimmiyar Sanarwa


Dukkan littafan malaman Shi’a, da muka yi amfani da su a rubutun wannan


taqaitaccen littafi, akwai su a xakin karatu (laburare) na cibiyar Markazus Sahabah


dake Sakkwato. Laburaren a buxe take ga kowa da kowa.


Tare da gaisuwar xan uwanku a Musulunci


Dr. Umar Labxo


1 Gidan talabijin na Aljazeera (ta Larabci) ya watsa labarin ranar 21 ga watan Fabrairu, 2013.


2 Duba jaridar Dailay Trust, Juma’a 31 ga watan Mayu, 2013, shafi na 1 da na 5.


3 Domin ganin hoton ‘yan Shi’ar Nijeriya dauke da tutocin Hizbullah, duba jaridar Dailay Trust, fitowar Talata 22


ga watan Mayu, 2012, shafi na 3.



Tulisan Terbaru

Keutamaan Puasa Enam ...

Keutamaan Puasa Enam Hari Syawal Shawal