Labarai




GABATARWAR MASU FASSARA


Godiya ta tabbata ga Allah. Tsira da aminci su daxa tabbata akan


shugaban talikai.


Faxakarwa dangane da iyakoki da dokokin Ubangiji Mahalicci na


daga cikin abin da musulmi ke da buqatarsa a ko wane lokaci, to, balle


kuma a wannan zamani namu da yake cike da abubuwan xaukar hankali


masu kawar da mutum daga godaben Shari’a.


To, sai dai ba kowa ne yake amfanuwa da wannan faxakarwar ba


sai wanda imani ya ratsa birnin zuciyarsa. Kamar yadda Allah ya ce;


Ma’ana:


“Ka faxakar domin, faxakarwa tana amfanin Muminai”.


Suratuz Dhariayt: 55


Wannan littafi na Sheikh Muhammad Saleh Al Munajjid yana da


matuqar muhimmanci ta wannan fuskar. Shi ya sa muka ga dacewar


mayar da shi zuwa harshen Hausa.


Roqon da muke ga Allah maxaukakin Sarki yasa mu cikin farko


waxanda ke aiki da wannan faxakarwa. Ya bamu ladar wannan aikin, ya


sanya shi cikin sikelin ayyukan alherinmu. Ya yafe mana duk wani


kuskure ko tuntuven harshe ko varin baki idan auku a cikin aikinmu.


Masu Fassara:


Muhammad Mansur Ibrahim


Da Aliyu Rufa’i Gusau


5


GABATARWAR MAWALLAFI


Godiya ta tabbata ga Allah, Abin yabo, Abin nufi da buqata.


Wanda muke neman gafararsa, muke kuma fatar Ya yi mana katangar


dutse, a tsakanin mu da sharrin zukatanmu da miyagun ayyukanmu.


Tabbas! Duk wanda Allah ya shiryar babu mai vatar da shi. Babu kuma


mai iya shiryar da wanda Allah bai nufa da shiriya ba. Na Shaida, ba abin


bauta wa da gaskiya Sai Allah, Shi kaxai, ba shi da abokin tarayya. Ina


kuma shedar da cewa Muhammadu bawansa ne kuma manzonsa.


Bayan haka:


Tabbataccen abu ne cewa, Allah Subhanahu Wa Ta’ala Ya


wajabta wasu abubuwa a kan mu, waxanda yin biris da su ba ya halasta.


Ya kuma haramta mana wasu abubuwan, waxanda su ma, yi masu kallon


hadarin kaji ba daidai ne ba. Allah a cikin ikonsa ya shimfixa mana wasu


dokoki ya shata wasu iyakoki da ba ya son a tsallake su.


A qoqarin fitowa da matsayin waxannan abubuwa biyu ne da


kuma abin da ke tsakanin su, Manzon Allah Sallallahu Alaihi


Wasallama ya ce:


“Duk abin da Allah Ya halasta a cikin littafinsa shi ne halas.


Babu kuma wani abu da ke haram, sai abin da Ya haramta. Duk kuma


abin da bai ce komai a kansa ba to garavasa ne. Ku karvi wannan


rangwame na Allah da hannu biyu biyu. Don har abada Allah ba Ya


mantuwa”. Daga nan kuma, sai ya karanta wannan aya:


Ma’ana:


Kuma Ubangijinka bai kasance mai yin mantuwa ba


(19:64).


6


Da wannan bayani na Manzon Allah Sallallahu Alaihi


Wasallama ne, ta bayyana cewa, duk abubuwan da Allah Subhanahu Wa


Ta’ala Ya yi wa bayinsa iyaka da su, su ne haram. Kuma yin biris da su


zaluntar kai ne. Allah Subhanahu Wa Ta’ala na cewa:


 :l edcba` m


Ma’ana:


Kuma wanda ya qetare iyakokin Allah to lalle ya zalunci


kansa (65:1).


Bayan wannan kuma sai Allah Subhanahu Wa Ta’ala Ya yi


tanadin wuta ga duk wanda ya qetare waxannan iyakoki da Ya shata. Ya


ce:


ÆÅÄÃÂÁÀ¿¾½m


 : l 


Ma’ana:


Kuma wanda ya sava wa Allah da manzonsa, ya kuma


qetara iyakokinsa, zai shigar da shi wuta, yana


madawwami a cikin ta, yana kuma da wata azaba mai


walaqantarwa (4:14).


Saboda irin qaunar da Allah Subhanahu Wa Ta’ala ke yi wa


bayinsa kuma, sai ya wajabta masu nisantar waxannan abubuwa ta


hanyar haramta masu su. Don kada su faxa cikin wannan azaba. A kan


haka, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama Ya ce:


“Duk abin da na hane ku da shi, ku nisance shi. Abin da kuma


duk na umurce ku da shi, ku aikata shi gwargwadon ikonku”. (Muslim:


130) .


7


Amma tattare da wannan irin gatanci, sai ka taras da waxanda


suka saba da biyar soye-soyen zukatansu, saboda raunin imani da


qarancin ilmi da suke da su, suna qorafe-qorafe. Da zarar an ce masu abu


kaza da kaza haramun ne a musulunci, sai su fara gunguni suna cewa:


“Kome dai haramun! Haramun!! Haramun!!! Wai wane irin addini ne


wannan da kullum yake qoqarin gasa mana aya a hannu? Kai kun dai ishe


mu. Ku ba ku da wata magana sai ta haram! Ai kamata ya yi addinin


musulunci ya zama kadaura babbar inwa, mayalwanciya, wurin hutawa,


ba aljannar masa ba. Kuma shin ko kun manta da cewa Allah Mai rahama


ne, kuma Mai jinqai?”


Irin waxannan mutane yana da kyau su sani cewa, Allah


Subhanahu Wa Ta’ala Sarki ne mai cikakken iko. Wanda ke gudanar da


mulkinsa yadda Ya so, kuma babu wanda ya isa ya tayar da wani hukunci


da Ya yi. Domin Ilminsa da hikimarsa sun kai matuqa. Yana halasta abin


da Ya ga damar halastawa, Ya kuma haramta abin da Ya ga dama. Kuma


mu, yana xaya daga cikin abubuwan da ke tabbatar da kasancewarmu


bayinsa na gari, mu yarda da duk wata doka da zai shata muna; mu miqa


wuya gare ta. Domin babu wata doka da zai yi face tana tsattsage da ilimi


da hikima da adalcinsa. Ba abu ne na sakarci da sharholiya ba. Kamar


yadda Allah Yake cewa:


Ma’ana:


Kuma kalmar Ubangijinka ta cika, tana mai gaskiya da


adalci. Babu mai musanyawa ga kalmominsa, kuma shi,


Mai ji ne, Masani (6:115).


8


Wani abun kuma shi ne: Allah Subhanahu Wa Ta’ala a cikin


wannan ilimi da hikima nasa, bai tsaya kawai ga halasta mana wasu


abubuwa da haramta mana wasu ba. Sai da ya bayyana mana qa’idar da


Yake bi a cikin yin haka. Dubi inda Yake cewa:


Ma’ana:


Kuma Yana halatta masu abubuwa masu tsarki


(waxanda suka shafi, Aqida da ibada da Mu’amala da


Ababen ci, da saurasu). Yana kuma haramta masu


qazantattun abubuwa. (7:157).


Ashe kenan Allah Subhanahu Wa Ta’ala Ya halatta mana wasu


abubuwa ne saboda kasancewarsu masu tsarki. Ya kuma haramta mana


wasu ne, saboda qazantar da suke da ita. Kuma irin wannan iko, na ware


wani abu a ce halas ne, ko a ware wani a ce haram ne, Allah Subhanahu


Wa Ta’ala ne kawai ke da shi. Kuma ko shakka babu, duk wanda ya naxa


wa kansa irin wannan rawani, ko ya naxa wa wani, ya tabbata kafiri.


Kafirci kuwa, laifi ne da babu kamar sa. Kamar yadda Allah Subhanahu


Wa Ta’ala ke cewa.


Ma’ana:


Ko suna da waxansu abokan tarayya (da Allah) waxanda


ke shar’anta masu, abin da Allah bai yi izini da shi ba


game da addini? (42:21).


Ba wannan kawai ba. Babu ma wanda Shari’a ta yarda ya tsoma


baki, a cikin yin sharhi a kan kasancewar wani abu halas ne ko haram,


9


face mutumin da ya naqalci asirin Alqura’ani da Sunnah. Saboda nauyin


wannan al’amari ne ma, Allah Subhanahu Wa Ta’ala Ya yi kashedi da


kakkausar murya, a kan masu wanke baki su tsoma, a zancen halas da


haram, alhali iliminsu bai taka kara ya karya ba. Saurari wannan aya


kuma ka kalle ta da idon basira:


Ma’ana:


Kuma kada ku ce, wannan halas ne, wannan haram ne


akan abin da harsunanku suke siffantawa na qarya.


Domin ku qirqira qarya ga Allah. Lalle waxanda ke


qirqira qarya ga Allah ba su rabauta. (16:116).


Kuma Saboda girman wannan mas’ala ne, da kariya ga


alfarmarta, tare da tsare mutuncin musulmi, Allah Subhanahu Wa Ta’ala


Ya qididdige abubuwan da aka daddale haramcin su cikin Alqur’ani,


Sunnah kuma ta tunfaye su. Ga abin da Subhanahu Wa Ta’ala Ya ce:


Ma’ana:


Ka ce “ku zo in karanta abubuwan da Ubangijinku Ya


haramta a kan ku: (Wajibi ne) kada ku yi Shirkan kome


10


da shi, kuma ku kyautata wa mahaifa, kuma kada ku


kashe xiyanku saboda talauci, Mu ne muke arzuta ku, da


su, kuma kada ku kusanci abubuwan alfasha; abin da ya


bayyana daga gare ta da abin da ya voyu, kada ku kashe


rai wadda Allah Ya haramta, face da haqqi. Wannan ne


(Allah) Ya yi muku wasiyya da shi, ko da zaku hankalta


(6:151).


Bayan wannan kuma, Sunnah ta zo da qididdigar wasu


haramtaccin abubuwa masu yawa. Kamar inda manzon Allah Sallallahu


Alaihi Wasallama ke cewa: Haqiqa Allah Ya haramta cinikin giya, da


mushe da naman alade da kuma gumaka (Abu Dawud: 3:486).


Ya kuma ce: Duk abin da Allah Ya haramta, to kuxinsa haramun ne


(Daraquxni: 3/7).


Bayan duk wannan kuma, akwai waxansu ayoyi da suka ambaci


wasu haramtattun abubuwa, a matsayinsu na qungiya; ‘yan uwa xaya uba


xaya. Kamar inda Allah Subhanahu Wa Ta’ala Ya haramta wasu nau’uka


na abinci. Ya ce:


Ma’ana:


An haramta maku mushe da jini da naman alade da abin da


aka ambaci sunan wanin Allah a gare shi (wurin yanka


shi), da maqararriyar (dabba) da jefaffiya da wacce ta


gangaro da sokakkiya da abin da masu dagi suka ci, - face


11


abin da kuka yanka - da abin da aka yanka don gumaka


(shi ma haramun ne). Kuma kada ku yi rabo da kibau na


caca. Wancan fasiqanci ne.. (5:3).


Haka kuma a wata ayar, Allah Subhanahu Wa Ta’ala Ya ambaci


qungiyar wasu mata, da aka haramta wa musulmi aurensu. Inda Ya ce:


Ma’ana:


An haramta maku (auren) uwayen ku (mata) da ‘ya’yanku,


da ‘yan uwanku, da goggonninku, da innoninku, da


‘ya’yan xan uwa, da ‘ya’yan ‘yar uwa, da uwayenku


waxanda suka shayar da ku mama, da ‘yan uwanku mata


na shan mama, da uwayen matanku, da agololinku


waxanda suke cikin xakunanku, daga matanku waxanda


kuka yi baiko da su. Idan har baku riga kuka yi baiko da su


12


ba to, ba laifi akan ku (ko auri ‘ya’yan nasu). Da matan


‘ya’yanku na tsatsonku (su ma basu halatta gare ku), da


kuma ku haxa ‘yan uwa mata biyu (a lokaci xaya), sai dai


abinda ya gabata (wannan Allah Ya yafe shi). Da matan da


suke da igiyar aure (basu halatta ku aure su a wannan


lokaci) sai fa in damanku ta mallake su (kuka kamo su a


wurin jihadi da kafirai). Wannan hukuncin Allah ne gare


ku. Kuma an halatta maku duk abinda ke bayan waxannan


(da aka lisafta) ku neme (su) da dukiyoyinku kuna masu


tsari da aure, ba masu zina ba. (4:23-24).


Haka nan kuma a wata ayar Allah Subhanahu Wa Ta’ala Ya


ambaci irin nau’in cinikin da yake haramta ga musulmi. Ya ce:


Ma’ana:


Kuma Allah Ya halatta lafiyayyen ciniki. Ya kuma


haramta Riba (2:275).


Wannan kenan. Amma kuma wani abin farin ciki, da ya kamata


kowane musulmi ya yi godiya ga Allah Subhanahu Wa Ta’ala akai shi


ne, kasancewar Buwayayyen Sarkin, Saboda tsananin rahamar da Yake


da ita ga bayinsa, Ya halasta masu wasu abubuwa masu xinbin yawa, da


yawun alqalami ba zasu iya qididigewa ba.


Saboda haka ne ma, maxaukakin Sarkin bai yi bayaninsu dalladalla


ba. Amma Ya yi bayanin haramtattun abubuwa saboda zaman su


‘yan kaxan. Domin kuma su zama rubuce raxam a kan allon zukatanmu,


har mu yi nesa- nesa da su koda yaushe. Ga abin da Yake cewa:


13


Ma’ana:


Kuma haqiqa (Allah) Ya rarrabe maku daki-daki, abin da


Ya haramta a kan ku, sai fa abin da aka buqatar da ku


zuwa gare shi bisa lalura (6:119).


Amma a taqaice, duk abin da Allah Subhanahu Wa Ta’ala Ya


halasta, to Ya yarda wa musulmi shi. Matuqar dai abu ne mai tsarki da


nagarta a dai-dai lokacin. A kan sifofin waxannan abubuwa ne Yake


cewa:


Ma’ana:


Ya ku mutane! Ku ci daga abin da yake a cikin qasa, yana


a matsayin halas, mai tsarki (2:168).


Kuma ko shakka babu, yanke hukuncin da Allah Subhanahu Wa


Ta’ala Ya yi na kasancewar komai halas a taqaice, matuqar ba a sami


wani dalili da ke haramta shi ba. Yin haka wata rahama ce da jinqayi Ya


yi wa bayinsa. Kuma wajibi ne mu miqa wuya ga haka, mu kuma gode


masa.


Haka kuma yin bayanin haramtattun abubuwa da Allah


Subhanahu Wa Ta’ala Ya yi dalla-dalla, shi ma wata rahama ce, da wani


jinqayi. Don hakan na matuqar taimaka wa musulmi ga zama faxake, a


kan dokokin shari’a. Musamman irin waxanda imaninsu da kaifin


basirarsu ba su shige cikin cokali ba, a fagen addini musulunci.


Ba wannan kawai ba. Irin waxannan mutane, nada alamar buqatar


a danqa masu jadawalin duk abubuwan da Allah Subhanahu Wa Ta’ala


14


Ya halasta dalla-dalla, kafin su gamsu da cewa addinin musulunci ba


kurkuku ne ba.


Wato suna so ne aya ta sauka, tana cewa: Naman Raquma da na


shanu da Tumaki da zomaye da Gada da Awaki da kaji da Xanragguwa


da Agwagwar Ruwa da Zabbi, duk, halas ne, in an yanka su da sunan


Allah. Haka kuma naman kaji da fari duk halas ne. Wata kuma ta ce:


Ababen marmari da Furanni da Ganyaye, da duk wasu ire iren masu


ciyawa halas ne. Kuma Ruwa da Madara da Zuma da Mayuka, duk halas


ne. Wata kuma ta ce: “Gishiri da Yaji da Maggi da Kori” halas ne.


Sannan kuma a samu wani nassin na aya ko hadisi da zai ce:


Amfani da katako da qarfe, ko Yashi da Duwatsu da Robobi da Gilasai


da Qarau, su ma halas ne. Wani nassin kuma misali ya ce: Amfani da


ababen hawa don yin tafiye tafiye cikin su har da Motoci da Jiragen qasa


da na sama da jiragen Ruwa, su ma sun halasta.


Wannan na dasa aya kuma sai wani Nassin ya xauka: Amfani da


Na’urorin sanyaya xaki da firijin, da Injinonin wanki da masu bushe


kaya, da injinonin niqe Hatsi su koma Gari, da Na kwava fulawa, da Na


niqe nama ko Ababen marmari, da Na’urorin binciken lafiyar mutum, da


na qere qere, da Na Lissafi, da Na Hangen Nesa, da Na Tatso Ruwa da


Mayuka da ma’adanai daga qasa da Na Tace Ruwa, da Na Xab’i da Masu


qwaqwalwa, da Makamantansu. Duk amfani da waxannan abubuwa halas


ne.


Wani Nassin kuma ya ce: Sanya Suturar da aka saqa da auduga


ko ulu ko kittani ko roba ko gashin Raqumi ko fata, halas ne.


Haka kuma suna da buqatar wani Nassin ya gaya masu a fayyace,


cewa Aure, Saye da Sayarwa, Xaukar Nauyin Wani, Yajejeniyar


15


Cinikayya a Rubuce, rubuta Risit, Haya, Sana’oin Hannu kamar Saqa,


qira, Jima, kanikanci da kiwo duk su ma halas ne,


Kai!!! Ko shakka babu idan aka ce haka za a bi duk abubuwan da


ke halas tiryan- tiryan ana lissafi sai wani zamani ya qare ba a ci rabi ba.


Ma’ana:


Me ke faruwa ga waxannan mutane da ko kusa ga fahimtar


magana ba su yi ba (sai in an yi ta dalla- dalla)? (4:78).


Wannan kenan. Mu koma ga cewar da suke ta yi, musulunci


addini ne mai sauqi da rangwame. Wannan magana ko shakka babu


gaskiya ce. Amma kuma a kaikaice mun fahimci suna son karkata akalar


maganar ne a matsayinta na gaskiya, su xaure wa qarya gindi da ita.


Domin su, a tunaninsu musulunci ba zai karva sunan addini mai


sauqi ba, sai ya tafi daidai da soye-soyen zukatansu. Alhali kuwa a


haqiqa, sauqin da addini ke da shi na samuwa ne ga mutum a lokacin da


ya bi abin duk da shari’a ta zo da shi sau da qafa. Akwai banbanci


matuqa tsakanin sauqin da ke cikin addinin musulunci, da irin wanda


waxannan mutane ke qoqarin tabbatarwa a cikinsa. Su a wurin su aikata


miyagun xabi’u da halaye, a lave bayan wasu hujjoji na qarya shi ne


sauqi. Ko alama. Ba haka abin yake ba. Sauqin da musulunci ya zo da


shi, ya shafi xaga wa musulmi qafa ne a cikin waxansu abubuwa na halas


don gudun su niqe shi. Kamar damar da aka ba shi ta haxa wata sallah da


wata, ko taqaita wata, ko ajiye azumi a cikin halin tafiya, ko shafa a kan


safa, na tsawon kwana xaya da yini ga mazaunin gida, da tsawon kwana


uku da wuninsu ga matafiyi, ko wanda ke fargaban tava ruwa a kan wata


lalura ya yi taimama, ko halatta kallon maccen da ba muharrama ba ga


16


mai neman ta aure, ko zaven xaya daga cikin: ‘Yantar da Bawa ko Ciyar


da Miskini ko Tufatar da shi ga wanda ya karya wani alwashi a matsayin


kaffara, ko cin naman mushe idan wuri ya qure, da dai sauran rangwamerangwamen


da shari’a ta zo da su masu kama da waxannan.


Babban abin da ya kamata kowane musulmi, har da irin


waxannan mutane, ya fahimta shi ne Allah Subhanahu Wa Ta’ala Ya


shata wasu iyakoki da dokoki ne, ta hanyar haramta waxansu abubuwa a


musulunci don Ya jaraba bayinsa. Kuma cin wannan jarrabawa ne, zai


banbanta su da ‘yan wuta waxanda suka qare rayuwarsu cikin biyar


qyaleqyalin duniya da son zuciya. Abubuwan da, da su ne Allah


Subhanahu Wa Ta’ala Ya yi wa gidan wuta qawanya. Ya kuma yi wa


gidan aljanna zoba da abubuwa masu nauyi da sosa zuciya waxanda


haquri da su ke sa a samu isa tudun mun tsira. Ka ga kenan ta wannan


hanya ce kawai Allah Subhanahu Wa Ta’ala zai ware bayinsa masu


biyayya daga kangararru, ba don bai san su ba.


Sanin haka ne ya sa masu ingantaccen imani ke kallon irin


waxannan jarabawoyi a matsayin wata hanya ta samun lada da yardar


Allah. A haka sai ka taras saboda jin daxi, har tuman gada suke yi idan


suna wata xa’a ga Allah, komai nauyinta. A yayin da su kuma munafukai


ke kallon jarabawoyin a matsayin wata takurawa da musgunawa. A


sakamakon haka sai al’amarin ya niqace su, su kasa cin jarrabawar bale


su sami ladarta da yardar Allah.


Ka ga kenan, wannan bayani da ya gabata na tabbatar mana da


cewa, duk wanda ya yi xa’a ga Allah Subhanahu Wa Ta’ala ta hanyar


nisantar abubuwan da ya haramta, saboda shi kawai, to Allah zai maye


masa gurbinsu da abin da ya fi wancan da ya nisanta zama Alheri. Bayan


daular zaqin da zata cika zuciyarsa.


17


Don in faxakar da musulmi a kan wasu abubuwa da Allah


Subhanahu Wa Ta’ala Ya haramta kuma Alqur’ani da Sunna suka


tabbatar amma mutane suka yi biris da su, na rubuta wannan taqaitaccen


littafi, ta hanyar fitowa da matsayin shari’a a kan abubuwan. Musamman


saboda kasancewar ‘yan uwa musulmi na aikata da yawa daga cikin su.


A qarshe, ina roqon Allah Subhanahu Wa Ta’ala Ya yi mana


jagora, mazanmu da mata. Ya kuma taimake mu a kan aikata abin da Ya


umurce mu da aikatawa tare da nisantar abin da ya haramta. Ya kuma


shiga tsakanin mu da miyagun ayyukanmu. Tabbas Allah shi ne mafi


taimakon masu taimako ga shiriya. Shi ne kuma mafi jinqayin masu


jinqayi.


18


BABI NA XAYA


SHIRKA


Shirka ita ce abu mafi girma daga cikin abubuwan da Allah


Subhanahu Wa Ta’ala Ya haramta. Kuma haxarin da ke cikinta ya shafe


na saura. Kamar yadda Abubakar Raliyallahu Anhu ya riwaito a wani


hadisi cewa: “Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce wa


Sahabbai wata rana: “kuna so in ba ku labarin zunubin da ba wanda da ya


kai shi girma? Muka ce, qwarai muna so ya Manzon Allah! Sai ya ce, shi


ne haxa Allah da wani abu a cikin bauta. (Bukhari: 2511).


Saboda girman wannan zunubi ne na Shirka, Allah Subhanahu


Wa Ta’ala Ya sha alwashin ba ya gafarta wa duk wanda ya yi ta.


Matuqar har ya mutu bai tuba ba. Savanin sauran zunubai da komai


yawansu Yake shirye da ya gafarta wa wanda ya aikata su, qyaftawa da


bisimillah.


Don tabbatar da wannan magana ne, Buwuyayyen Sarkin ke


cewa:


Ma’ana:


Haqiqa, Allah bai gafarta wa duk wanda ya haxa shi da wani


a cikin bauta. Amma Yana gafarta abin da bai kai wannan


ba, ga wanda Ya so (4:48).


Daga cikin nauo’an Shirka, da suka yawaita matuqa a qasashen


musulunci a yau, akwai:


19


Bautar Qaburbura


Bautar qaburbura ita ce qudurce cewa, wani waliyyi daga cikin


waliyyan da suka riga mu gidan gaskiya, na iya biyan wata buqatar


mutum ko cetonsa daga wani haxari. Saboda haka sai a riqa kiran


sunayensu don neman taimako ko agaji.


To, a idon shari’ah da aqidar musulunci ingantatta yin haka bauta


wa irin waxannan bayin Allah ne. Alhali kuwa Allah Subhanahu Wa


Ta’ala Ya ce:


Ma’ana:


Kuma Ubangijika Ya hukunta kada ku bauta wa kowa sai


shi kaxai (17:23).


Irin wannan bauta ba ta tsaya ga waliyyai da qaburburansu ba.


Har wasu Annabawa da Salihan mutane, da suka riga mu gidan gaskiya,


wasu mutane kan nufa da wasu buqatu, da suka haxa da neman agaji,


buqatar haifuwa, gyaran aure da makamantansu. Su ma sukan yi haka ne


ta hanyar kiran sunayensu a irin waxannan lokuta. Alhali kuwa ba za su


iya amfanin su da komai ba. Ga shi kuma Allah Subhanahu Wa Ta’ala


Ya ce:


Ma’ana:


Ko wane ne yake karva wa mai buqata idan ya kira shi,


kuma ya sanya ku mamayan qasa? Shin akwai wani abin


bauta wa tare da Allah? Kaxan ne kuke faxaka (27:62).


20


Saboda tsananin kama jikin waxansu mutane da irin wannan


Shirka ta yi, abin har ya fi qarfin qudurtawa a zuci. Wasu ma har


ambaton sunayen wasu shehunai da waliyyai suke yi idan za su zauna ko


za su tashi tsaye, ko idan suka yi tuntuve ko suka haxu da wata annoba.


Sai ka ji suna cewa: “Ya Muhammadu” ko “Ya Aliyyu’’ ko “Ya


Husaini”. A yayin da kuma wani zai ce: “Ya Badawi’’ ko “Ya jelani” ko


“Ya shazali” ko “Ya Rufai”. Wasu ma har al-Aidarus ko Sayyidah


Zainab suke kira. Alhali kuwa gaba xayansu su ma ta kansu suke yi,


kuma bayin Allah ne kamar kowa. Kamar yadda Allah Subhanahu Wa


Ta’ala Ya ce:


Ma’ana:


Tabbas, waxanda ku ke kira ba Allah ba bayin Allah ne


kamar ku. To, ku kira su su karva maku in gaskiya ne kuke


yi (7:194).


Wasu ma har tattaki sukan yi zuwa wurin kusheyin waxannan


bayi su dinga yin xawafi gare su kamar yadda ake yi ga xakin ka’abah,


har ma su shafi kusurwoyinsu. Wasu kuma sukan har ma sunbanci


kusheyin, su kuma kai hannayensu gare su, su shafi fuskokinsu da qurar


kamar masu taimama. A yayin da wasu ko, da zarar sun tunkaro


makwantan ba abin da za su yi sai ruku’i ko su yi tsaye qyam a gabansu


suna masu tsananin ladabi da vari kamar su narke. A inda za su roqi


buqatunsu kamar neman waraka daga wata rashin lafiya, ko albarka ga


wani yaro, ko tsira daga wata matsala. A wasu lokutan ma zaka ji wasu


21


daga cikinsu na magana da mamatan suna cewa: “Ya shugabana! ga ni na


niqo gari daga uwa duniya ina fatar buqatuna sun gama biya. Alhali kuwa


da za su share shekarun Abarshi suna kiran su ba za su karva masu ba.


Allah Subhanahu Wa Ta’ala na cewa:


Ma’ana:


Kuma wane ne mafi vata daga wanda ke kiran wanin


Allah wanda ba zai karva masa ba, har Ranar qiyama,


alhali su (waxanda ake kiran) shagaltattu ne daga kiran


su (46:5).


Kuma Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Duk


wanda ke nufin wani da wata buqata banda Allah, makomarsa ita ce wuta


(Buhari: 8/176).


Duk bayan waxannan kiraye-kiraye kuma, qarshe sai ka ga wasu


daga cikin waxannan mutane sun karkata gefen kusheyin sun aske kansu.


Wasu kuma sun shagala da karatun xan littafinsu mai suna: “al-


Mashahid” wanda littafi ne da aka tsara yadda ziyarar qaburburran


Waliyai da Annabawa zata kasance, da karance- karancen da wasu


mutane suka ga ya dace ayi. Kamar dai Littafin “Manasik al- Hajji”


wanda gamagarin Alhazzai ke amfani da shi. Qarewa da qarau ma, wasu


daga cikin irin waxannan mutane sun yi imani da cewa a hannun


waxannan matattu linzamen harkokin duniya suke. A sakamakon haka,


suna iya amfanar da wanda suke so, su kuma cutar da wanda bai masu


daidai ba. Tarqashi! Allah mai halitta!!.


Allah Subhanahu Wa Ta’ala dai cewa Ya yi


22


Ma’ana:


Kuma idan Allah Ya shafe ka da wata cuta, to babu mai


yaye ta face shi, kuma idan Yana nufin ka da alheri, to


babu mai iya hana falalarsa sauka. Yana bayar da alherinSa


ga wanda Ya so, kuma Shi ne Mai yawan gafara, Mai


Yawan jinqai (10:107).


Haka kuma duqa ma wani wanda ba Allah ba, Shirka ne. Kamar


irin duqawar da irin waxannan mutane ke yi ko ajiye fitilu da kyandirora


ga waxannan qaburbura. Bayan wannan nau’in Shirka sai kuma:


Yanka Don Wanin Allah


Xaya daga cikin yanke – yanken da mushrikai kan yi tun zamanin


Jahiliyyar Larabawa, wanda kuma ya zama wata al’ada da ta watsu a


cikin duniya shi ne yanka wata dabba don aljannu su sha jini.


Mushrikan Larabawa kan yi wannan al’ada ne, kamar idan xayan


su ya gina ko ya sayi gida, ko ya haqa wata rijiya. Sai a sami wata dabba


a yanka a bai wa aljannun da ake da imanin suna cikin gidan ko rijiyar


jini a matsayin cin hanci, don su bar abin. Wanda idan ba haka aka yi ba,


a tunaninsu, mai gidan ko rijiyar zai haxu da wata cuta.


Irin wannan Shirka ta haxa nau’in haramiya biyu: Na farko,


Sadaukar da wani abu da sunan bauta ga wanin Allah. Na biyu kuma,


yanka abin da za a yi ba da sunan Allah ba.


23


Da zuwan addinin Musulunci sai wannan al’ada ta haramta.


Allah Subhanahu Wa Ta’ala Ya musanya wa musulmi ita da bauta masa


inda Ya ce:


Ma’ana:


Saboda haka, ka yi sallah ga Ubangijika, ka kuma yi


yanka (don Shi) (108:2).


Bayan wannan kuma sai Manzon Allah Sallallahu Alaihi


Wasallama ya qara daddale wannan haramci tare da qara fitowa da shi


fili, ya ce: “Allah Ya la’anci duk wanda ya yanka wani abu don wanin


Allah (Muslim: 1978).


Nau’in Shirka na gaba kuma shi ne:


Halsta Abin Da Allah Ya Haramta


Haka nan kuma yin imani da cewa akwai wani mahaluki a bayan


qasa, wanda ke da lasisin halasta wani abu da Allah Subhanahu Wa


Ta’ala Ya haramta, Shirka ne.


Irin wannan Shirka ta haxa har da kai qara a kotunan da ba na


musulunci ba. Musamman idan haka ta kasance tare da yin imani da


cewa yin haka halas ne. Kuma an tafi can ne bisa zavin kai; babu wanda


ya tilasta hakan.


Allah Subhanahu Wa Ta’ala Ya ambaci irin wannan Shirka a


cikin Alqur’ani, a matsayin Babbar Shirka, in da Ya ce:


24


Ma’ana:


Sun riqi malamansu (Yahudawa) da ruhubanawansu


(Nasara) Ubannangiji, baicin Allah (Saboda Suna yi


masu xa’a a cikin abubuwan da suka halasta masu ko


haramta masu, bisa ra’ayin kansu; ba umunin Allah ba)


(9:31).


A lokacin da Adiyyu xan Hatimu ya ji Manzon Allah Sallallahu


Alaihi Wasallama ya karanta wannan aya sai ya ce: Ya Manzon Allah!


Ai ba bauta masu suke yi ba. “Sai Manzon Allah Sallallahu Alaihi


Wasallama ya karva masa da cewa: “Na ji. Amma ai suna halasta masu


abubuwan da Allah Ya haramta, su kuma haramta masu abubuwan da Ya


halasta, su kuma amince da haka ko? To, ai wannan ita ce bautar da suke


yi masu. (Baihaqi: 10/116).


Bayan wannan ma, irin wannan tavargaza, na daga cikin siffofin


mushrikai, kamar yadda Allah Subhanahu Wa Ta’ala Ya bayyana a wata


aya da ke cewa:


!, :567 lzyxwvum


Ma’ana:


Ba su haramta abin da Allah da Manzonsa ya haramta,


kuma ba su bin addinin gaskiya (9:29).


A wata ayar kuma Ya ce:


Ma’ana:


25


Ka ce, “Shin, kun ga abin da Allah Ya saukar saboda ku


na arziki, sai kuka halalta wasu kuka haramta wasu?”.


“Ka ce, “Shin, Allah ne Ya yi maku izini, ko Allan ne


kuke wa qazafi? (10:59).


Nau’in Shirka na gaba kuma shi ne:


Sihiri, Bayar Da Sa’a Da Faxin Gaibi


Sihiri wani na’ui ne na kafirci, kuma Shirka ne. Yana kuma daga


cikin zunubai guda bakwai da ke durmuyar da mutun a cikin wuta. Kuma


babu wani amfani da ake samu a cikinsa. Hasali ma ba abin da yake


haifarwa ga wanda aka yi wa shi illa hasara da ci baya.


Allah Subhanahu Wa Ta’ala Ya gaya mana matsayin masu


koyon sa. Ya ce:


Ma’ana:


Kuma suna neman ilimin abin da yake cutar da su, kuma


ba ya amfaninsu (2:102).


A wata ayar kuma Ya ce:


, :89 lzyxwvum


Ma’ana:


Kuma masihirci ba ya cin nasara a duk inda ya je (20:69).


A wata ayar kuma Allah Subhanahu Wa Ta’ala Ya tabbatar da cewa duk


wanda ke sihiri da tsafi kafiri ne. Ya ce:


26


Ma’ana:


Kuma sulaimanu bai yi kafirci ba, kuma shaixanun su ne


suka yi kafirci, (Saboda) suna karantar da mutane sihiri


da abin da aka saukar da shi a kan mala’iku biyu a


Babila; Haruta da Maruta. Kuma babu wanda suka sanar


sai sun ce: “Mu fa fitina ne, saboda haka kada ka kafirta”.


(2:102).


Bayan wannan kuma hukuncin mai sihiri a duniya shi ne kisa,


kuma duk abin da ya samu daga wannan sana’a tasa qazantatta, shi ma


haram ne.


Amma kuma duk da irin wannan mugun matsayi na mai sihiri,


sai ka taras da wasu musulmi, saboda kantar jahilci da tsatsarsa, da raunin


imani da ke tattare da su, suna ziyarar masu wannan mugunyar sana’a


don neman su taimake su, su xauki fansa a kan wani ko kuma don su


karya wani makaru da wani ya yi masu. Alhali kuwa kamata ya yi su


fuskanci Allah Subhanahu Wa Ta’ala su nemi taimakonsa a kan


waxannan al’amurra da makamantansu. Ta hanyar karanta wasu surori na


Alqur’ani kamar Falaqi da Nasi.


Haka su ma masu bayar da sa’a, ta hanyar bayar da labarin abin


da zai faru. Su ma kafirai ne. Domin suna raya cewa sun san gaibi. Alhali


kuwa babu wanda ya san gaibi sai Allah.


27


Mafi yawan masu irin wannan sana’a sukan yi amfani ne da


qarancin ilimi da wayewar wasu mutane, su karve masu kuxaxe. Sai ka


ga suna ‘yan zane –zane ga qasa, suna jefa xiyan wuri suna karanta wasu


surkulle. Wasu kuma a qasashen Turai suna wasa da kofunan Gahawa da


wasu ‘yan kwalayen qarau da madubbai, da makamantansu. Amma kuma


a mafi yawan lokuta, sau xaya ne sukan yi nasara daga cikin sihiri xari


da suke yi, sauran xari ba xayan kuma, sun sha kunya a cikinsu. Duk da


haka, irin waxancan jahilan mutane sai su mayar da hankali a kan sihirin


nan guda da qaddara ta riga fata a cikin sa, su manta da Tasa’in da tarar.


Take Sai ka ga suna ta yin tururuwa a garaken masihirtan, suna


neman su gaya masu ko akwai sa’a a cikin wani aure ko kasuwanci da


suke shirin qullawa. Ko su taimaka masu su gane wani abu nasu da ya


vata da wasu abubuwa masu kama da wannan.


A qa’idar shari’ar musulunci kuwa gaskata mai sihiri kafirci ne.


Kamar yadda Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Duk


wanda ya je wurin wani boka ko mai sihiri, ya kuma gaskata shi, to, ya


kafirce wa abin da aka saukar ga Muhammadu Sallallahu Alaihi


Wasallama (Ahmad: 2/429).


Idan kuwa har zuwa wurinsu kawai mutun ya yi, ba don ya yi


imani da abin da suke yi ba, ba kuma don ya yi amanna cewa sun san


gaibi ba. A’a ya dai tafi ne don tantancewa da ganarwa idonsa, ko don


wani abu mai kama da wannan, to bai zama kafiri ba. Amma dai ya yi


babbar hasara. Don Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce:


Duk wanda ya je wurin wani mai sihiri ya kuma tambaye shi wani abu to,


ba za a karvi Sallarsa ba har kwana arba’in (Muslim: 4/1751). Amma duk


da haka wajibi ne ya ci gaba da Sallar, yana kuma neman gafarar Allah a


kan laifin.


28


Bayan wannan na’ui na Shirka sai kuma:


Imani Da Taurari


Zaidu xan khalidu al-juhani ya riwaito cewa: “Wata rana a


Hudabiyya, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ba mu sallar


safe, bayan an xauke ruwan sama, da aka kwana ana yi. Da ya qare sallar


ya juyo ya fuskance mu. Sai ya ce: ko kun ji abin da Unbangijinku ke


faxa? Muka ce: Allah da Manzonsa kaxai ke da sani. Daga nan sai ya ce:


“Allah Ya ce ne: Wayewar garin nan wani bawa nawa ya yi imani da ni,


wani kuma ya kafirce mani. Duk wanda ya ce: “Ruwan nan Allah ne Ya


shayar da mu a cikin ikonsa da rahamarsa”. To shi ne wanda ya yi imani


da ni, ya kafirce ma taurari. Shi kuwa wanda ya kafirce mani ya kuma yi


imani da taurari shi ne wanda ya ce: “Tauraruwa kaza da kaza ne suka


shayar da mu wannan ruwa (Buhari: 2/333).


Haka kuma duk wanda ya karanta jadawalin abubuwan da za su


faru na gaibi wanda ake kirdado dabra da kaiwa da komowar taurari, a


cikin wata jarida ko mujalla, ya kuma yi imani da abin to, babu shakka


shi ma mushriki ne. Savanin wanda karantawa kawai ya yi don nishaxi.


Shi mai laifi ne kawai. Dalili kuwa shi ne, ba abu ne yardadde a shari’a


ba, mutum ya nemi samun wani nishaxi ta hanyar karanta wasu abubuwa


da suka qunshi Shirka. Domin shexan na iya amfani da wannan dama ya


tuqa masa tuwon tulu, a wayi gari ya faxa cikin mushrikai.


Abu na gaba kuma a layin nau’o’an Shirka shi ne:


Imani da Tasirin wani Abu


Wani nau’i na Shirka kuma shi ne imani da cewa, wani abu na da


wani tasiri na amfani zuwa ga mutum. Alhali Allah Mahalicci bai tanadi


haka ba.


29


Wasu mutane sun yi imani da cewa, abubuwa irin su: Karho,


Laya, Guru da Dagumma na da wani amfani da zasu iya yi masu.


Wannan kuwa wata tsohuwar al’ada ce da suka gada tun kaka da


kakanni. Wasu kuwa yanzu ne da rana tsaka bokaye da malamansu na


tsibbu ke xora su a kan wannan aqida. A sakamakon haka sai ka tarar da


su rataye da waxannan abubuwa ga wuyansu ko sun xaura ga


kunkuransu, ko sanye ga kunnuwansu ko ga damatsansu ko na’ya’yansu.


Imanin da suka yi shi ne abubuwan na taimakonsu ga kuranye masu


hatsarin mayu da masu kandun baka.


Wasu kuma zaka ga rataya irin waxannan abubuwa suke yiga


motocinsu ko a bangayen gidajensu. Wasu kuma wasu zobba zaka gani


ga yatsunsu, waxanda aka saka wa wasu duwatsu na musamman


waxanda suka yi imani cewa, suna ba su kariya ne daga wasu matsaloli.


Alhali kuwa a haqiqanin gaskiya, waxannan abubuwa na kawai nisantar


da waxanda suka yi imani da su ne, daga kasancewa masu imani da


Allah Subhanahu Wa Ta’ala, masu dogara gare shi. A qarshe kuma ba


abin da za su qaru da shi, illa rauni da hasara da tavewa. Domin yin


hakan neman waraka ne ta hanyoyi haramtacci.


Eh! Ko shakka babu hanyoyi ne haramtacci. Domin a cikinsu


akwai Shirka, wadda ke tabbata ta hanyar neman agaji daga shexanu ko


wasu aljannu. Ko ka taras a cikin su da surkulle, na wasu zane-zane da


rubuce- rubuce. A wasu lokuta kuma zaka ga an rubuta wasu ayoyin na


Alqur’ani, an sassaqa su da wasu kalmomi na Shirka. Wani lokaci ma


akan yi waxannan rubuce-rubuce da zane- zane ne, da qazamtattun


abubuwa kamar jinin haila da makamantan sa.


Ko shakka babu, xaura irin waxannan abubuwa da amfani da su a


jikin mutum ta ko wace hanya haramun ne. Saboda Manzon Allah


30


Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Duk wanda ya xaura laya ya yi


Shirka (Ahmad: 4/156).


Qarin bayani game da wannan hadisi shi ne: Idan wanda ya xaura


layar ga misali ya qudurce cewa, tana da wani tasiri na kai tsaye, a cikin


samar da wani amfani ko wata cuta wadda Allah bai nufa ba, to, ya


aikata babbar Shirka. A yayin da wanda kuma ya xaura layar yana mai


qudurce cewa, tana zama sanadi ne kawai na amfanin ko cutar amma


tantagaryar aikin na hannun Allah. To, irin wannan ya aikata qaramar


Shirka.


Wani nau’i na Shirka kuma shi ne:


RIYA


Yana daga cikin qa’idojin da shari’a ta gindaya, ga ko wane


kyakkyawan aiki, kafin ya zama karvavve a wurin Allah, dole ne ya


kasance an yi shi ba don a nuna wa duniya ba. Kuma dole ne ya kasance


daidai da yadda sunnah ta tanada a yi shi.


A kan haka, duk wanda ya aikata wani aiki na ibada kamar Sallah


don ya nuna wa mutane cewa yana sallah, to ya yi Shirka. Kuma Allah ba


zai karvi aikinsa ba.


Allah Subhanahu Wa Ta’ala ne cewa a kan haka:


Ma’ana:


Haqiqa, munafukai suna yaudarar Allah (a zatonsu) alhali


kuwa Shi ke yaudarar su ga haqiqani. Kuma idan sun tashi


zuwa sallah, sai su tashi a raggwance. Suna nuna wa mutane


31


(wai suna sallah!), kuma ba su ambatar Allah sai kaxan


(4:142).


A idon shariar musulunci duk wanda ya yi wani aiki na ibada don


labari ya kai ga kunnuwan mutane, ya faxa tarkon Shirka, kuma


sakamakonsa shi ne Allah zai taqaita ladar aikin nasa a kan haka. Kamar


yadda xan Abbas Raliyallahu Anhu ya riwaito a wani hadisi cewa,


Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: Duk wanda ya aikata


wani abu don mutane su ji ko su gani Allah zai sa su jin kuma su gani


(Shi ke nan. Ba lada). (Muslim: 4/2289) .


Haka kuma yau da mutum zai yi irin wannan aiki na ibada amma


bai yi shi don mutane su gani ko so ji ba kawai. A’a har ma don Allah Ya


ji kuma Ya gani, To, shi ma irin wannan bai tsira ba. Kenan ya yi aikin


don Allah da mutane. Aikin nasa kuwa ya zama ba karvavve ba a wurin


Allah. Kamar yadda wani hadisi qudusi yake cewa, Allah Subhanahu Wa


Ta’ala Ya ce: “Na wadaci kaina, ta yadda ba na buqatar yin tarayya da


kowa a cikin komai. Saboda haka duk wanda ya aikata wani aiki, ya ce


ya yi shi don mutane da kuma Ni, to na bar wa wanda ya haxa Ni da shi


aikin. Ni ba na so (Muslim: 2485).


Tana yiwuwa kuma, wani lokaci, mutum ya fara wani aiki, ba ya


nufin kowa da shi sai Allah. Amma kuma kafin ya qare sai shexan ya


kaxa masa tambari sai ya ji yana buqatar a gani. To, idan ya qi sauraren


wannan huxuba ta shexan Allah zai karvi aikin nasa. Amma idan ya


saurare shi har ya yi masa kari, to, mafi yawan malamai sun tafi a kan


cewa Allah Subhanahu Wa Ta’ala ba zai karvi aikin nasa ba.


Nau’i na gaba kuma daga cikin waxannan nau’o’i na Shirka shi ne;


32


CAMFI


Camfi wata tsohuwar al’ada ce ta maguzanci, da akan yi amfani da


ita don gano abin da zai faru nan gaba na alheri ko sharri, ko kuma don


yanke hukuncin dalilin faruwar wani abu da mafarinsa. Allah Subhanahu


Wa Ta’ala na cewa:


Ma’ana:


Sai idan wani abu mai kyau ya je masu, sai su ce:


“Wannan namu ne”. Kuma idan masifa ta same su sai su


ce, shu’umcin Musa ne da waxanda ke tare da shi


(7:131).


Kafin zuwan musulunci idan Balarabe ya shirya tafiya sai ya kama


wani xan tsuntsu sannan ya sake shi a sarari har tsuntsun ya yi tafiyar sa.


Idan ya fiffika ta dama, sai ya ce, akwai sa’a ga wannan tafiya. Idan


kuwa har ya fiffika ta hagu, to, shikenan, ba batun tafiya domin babu sa’a


a cikinta.


Da bayyanar musulunci, sai Manzon Allah Sallallahu Alaihi


Wasallama ya yanke wa irin wannan camfi hukunci da cewa: “Camfi


Shirka ne” (Ahmad: 1/389).


Irin wannan haramtacciyar aqida ta camfi wadda ke takin saqa da


aqidar Tauhidi ta haxa da, qudure cewa akwai waxansu lokuta ko


ranakku ko watanni da makamantan su da babu sa’a a cikinsu faufau.


Kamar yadda wasu suka camfa watan Rajab da cewa watan rashin sa’a


ne. Saboda haka ba sa yin aure a cikinsa. Wasu kuma sun camfa ranar


33


larabar qarshen ko wane wata da cewa ita ma rana ce ta rashin sa’a, da


saukar miyagun qaddarori. Wasu kuma sun camfa wasu sunaye da wasu


lambobi, kamar 13 da wasu mutane suka camfa da cewa ba sa’a a tare da


ita.


Haka kuma camfa musakai da wasu mutane suka yi da cewa suna


tare da rashin sa’a. Shi ma wannan haramun ne. Akwai mutanen da yau


da zasu nufi kasuwa su don su buxe shagunansu. Da zarar sun ci karo da


mai- ido- xaya a hanya sai su dawo gida. Wai, ba sa’a a ranar kenan. Duk


waxannan camfe-camfe haramun ne, kuma nau’i ne na Shirka. Kuma


Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce, ba shi ba mai yin su.


Kamar yadda Imrana xan Husaini ya riwaito cewa, Manzon Allah


Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Duk wanda ke amfani da tsuntsu


don neman sa’a, ko yake da wani mai yi masa haka, ko ya ke gaya masa


abin da gobe zata haifar, ko yake haka da kansa, ba ya tare da mu”. Mai


riwayar ya kuma ce: Kuma kamar na ji ya ce haka: “Ko wanda ke tsafi,


ko yake da wani mai yi masa”. (Tabarani: 18/162).


Kaffarar da wanda ya yi irin wannan aika-aika zai yi na cikin


hadisin da Abdulahi xan Ausu ya riwaito cewa, Manzon Allah Sallallahu


Alaihi Wasallama ya ce: “Duk wanda ya fasa yin wani abu saboda wani


camfi, ya yi Shirka. Sai sahabbai suka tambaye shi, mene ne kaffararsa?


Sai ya ce: kaffararsa ita ce, ya ce: Ya Allah! babu wani alheri sai


alherinka, babu kuma wani sharri sai wanda ka hukunta, kuma babu wani


Ubangiji sai kai kaxai. (Ahmad: 2/220).


To amma kuma a haqiqa, yin imani cewa, wani abu na iya zama


alheri ko sharri wani abu ne da Allah Subhanahu Wa Ta’ala Ya halitta


cikin jinin xan Adamu, kai tsaye ko kaikaice. Amma kuma babban


maganinsa shi ne dogara ga Allah. Kamar yadda xan Ma’sudu


34


Raliyallahu Anhu ya ce: “Babu wanda ba ya irin wancan hasashe daga


cikinmu a wasu lokuta. Amma da zarar mun mayar da kome ga Allah sai


mu sami sukuni (Abu Dawud: 3910).


Nau’i na qarshe daga cikin waxannan nau’o’i na Shirka shi ne:


Rantsuwa Da Wanin Allah


Allah Maxaukakin Sarki shi ke da iko da damar yin rantsuwa da


duk abin da ya ga dama daga cikin abubuwan da ya halitta. Babu wani


mutum da ke da damar yin rantsuwa da wani abu da ba Allah ba. Amma


kuma duk da haka akwai mutane da dama daga cikin musulmi da ke yin


rantsuwa da wanin Allah. Yin haka kuwa ba wa abin da aka yi rantsuwar


da shi ne matsayin Allah Subhanahu Wa Ta’ala. Wannan kuwa laifi ne


babba. Xan Umar ya riwaito cewa, Manzon Allah Sallallahu Alaihi


Wasallama ya ce: Haqiqa Allah Ya haramta maku yin rantsuwa da


ubanninku. Duk wanda rantsuwa ta kama shi daga cikinku, to ya rantse


da Allah ko ya kama bakinsa. (Bukhari: 11/530). Haka kuma xan Umar


xin ya riwaito Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama na cewa: “duk


wanda ya rantse da wanin Allah ya yi Shirka. (Ahmad: 2/125).


Haramun ne mutum ya rantse da: Xakin Ka’aba, ko Gaskiyar wani


ko tasa, ko Darajar wani ko tasa, ko suturar wane da wane, ko rayuwar


wane da wane, ko Mu’ijizojin wani Manzo, ko karamar wasu Waliyyai,


ko mutum ya rantse da Mahaifansa ko dai wani abu. Duk wanda ya aikata


haka to, ya yi Shirka. Babu abinda zai kankare masa wannan laifi sai sake


faxar kalmar shahada; ita ce: “La’ilaha Illal-lah”. Kamar yadda wani


ingantaccen hadisi ya ce: “Duk wanda ya yi rantsuwa da Lata ko Uzza, to


ya ce: “La’ilaha Illallah” (Bukhari: 11/536).


35


Bayan irin wannan rantsuwa da wanin Allah ta kai tsaye, akwai waxansu


kalamai da musulmi ke furtawa waxanda kuma ba wani abu a cikinsu sai


Shirka. Kalaman sun haxa da:


(i) Ina neman taimakon Allah da naka”


(ii) Wannan abu daga Allah ne da kuma kai


(iii) Ba ni da kowa sai Allah sai kai


(iv) Taqamata Allah a sama da kai a qasa”


(v) Ba don Allah da wane da wane ba..”


(vi) “….na jingine musulunci”


(vii) Shekara ta karya ni


(viii) Wannan mummunan lokaci ne”


(ix) Zamani xan mangwaro ne.


Haka kuma akwai wasu sunaye da wasu musulmi ke amfani da su,


waxanda ke xauke da amon Shirka, kamar:-


(a) Abdul- Masihi (Bawan Masihu)


(b) Abdun- Nabiyi (Bawan Annabi)


(c) Abdul- Husaini (Bawan Husaini)


Duk ire-iren waxannan Sunaye da ke danganta mutum ga wani


wanda ba Allah ba, a matsayin bawansa, haramun ne. Kamar yadda yake


haramun musulmi ya furta irin waxancan kalamai da muka faxa don sun


qunshi haxa Allah da wani, ko sukar lamirin wani lokaci tun da yin haka


suka ne ga Allah Shi kansa.


Haka kuma akwai waxansu kalamai da zamani ya zo da su


waxanda ke takin saqa da Tauhidi. Su ma duk furta su da qudurce


ingancinsu a zuci haramun ne ga musulmi. Waxannan kalamai sun haxa


da kamar:


1- Gurguzun Musulunci (Islamic Socialism)


36


2- Dimuquraxiyyar Musulunci (Islamic Democracy)


3- Ra’ayin Mutane shi ne Ra’ayin Allah


4- Addini na Allah ne, qasa kuma ta kowa ce


Da sauran su.


Haka kuma haramun ne a ambaci wani munafuki ko kafiri da xaya daga


cikin waxannan laqubba.


- Alqalin Alqalai


- Sarkin Sarakuna


- Mai gida


Haka kuma yin “da-na sani” ta hanyar amfani da kalmar “Da dai..” ko


“in da ..” haramun ne. Domin kalmar na nuna cewa mutum bai gamsu da


wani abin da Allah Subhanahu Wa Ta’ala Ya riga ya hukunta ba.


Haka kuma cewa: “Allah ka gafarta mani in ka ga dama” shi ma


haramun ne.


Mai son qarin bayani da faxaxa nazari sai ya duba littafin: Mu’ujamul


Manahil Lafziyyah Na Sheikh Bakr Abu Zaidi.


37


BABI NA BIYU


Zama Da Munafukai Da Mavarnata


Wani abu kuma da Allah Subhanahu Wa Ta’ala Ya haramta kuma


mutane suka yi biris da shi, shi ne zama wuri xaya da munafukai da


mavarnata. Zaka sami mutane da dama saboda rashin qarfin imani suna


zamansu gaba gaxi tare da irin waxannan mutane marasa tarbiyyah da


tsoron Allah. Wani lokacin ma sukan zauna har tare da waxanda ke sukar


lamirin shari’ar Musulunci, suna zolayar addini da masu kishinsa.


Ko shakka babu irin wannan xabi’a haramun ce. Kuma abu ne da


ke rosa imanin mai yinsa. Allah Subhanahu Wa Ta’ala Ya ce;


Ma’ana:


Kuma idan ka ga waxanda suke kutsawa a cikin ayoyinmu,


to, ka kau- da- kai daga gare su, sai sun shiga cikin wani


labari ba shi ba. Kuma in ma dai shexan ya mantar da kai, to


kada ka zauna a bayan tanawa tare da mutane azzalumai


(6:68).


Wannan aya ta tabbatar mana da haramcin zama tare da waxannan


mutane, koda kuwa makusanta ne na qud-da qud. Sawa’un kun haxa


zumuntar jini ko hulxar arziki. Sai fa idan za ka zauna ne a wurinsu don


ka yi masu gargaxi ko ka qalubalance su game da abinda suke yi don su


daina. Idan ba haka ba, to haramun ne mutum ya zauna da su. Allah


Subhanahu Wa Ta’ala na cewa:


38


Ma’ana:


Suna rantsuwa gare ku (Su Munafukai) don ku yarda da su.


To, ko kun yarda da su haqiqa Allah ba shi yarda da mutane


fasiqai. (8:96).


Ke nan duk wanda ya zauna tare da waxannan mutane zama na


yarda da amincewa, to ya zama xaya da su.


Rashin Natsuwa A Cikin


Sallah


Wani abun kuma da shari’a ta haramta shi ne yin sallah ba cikin


cikakkar ratsuwa ba. Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce:


“Babu Babban Varawo irin wanda ke satar wani abu daga cikin sallarsa.


Sai sahabbai suka ce: “Ya Manzon Allah, ya za a yi mutum ya saci wani


abu daga cikin sallah”? Sai ya ce: “Idan ya qi yin ruku’i da sujuda cikin


natsuwa” (Ahmad: 5/310).


Rashin cikakkar natsuwa a cikin ruku’i da sujuda da tsayuwa


bayan ruku’i da zama tsakanin sajaddai biyu, abu ne da ya zama ruwan


dare a tsakanin musulmi yau. Babu wani masallaci da zaka leqa sai ka


tarar da irin wannan matsala birjik. Alhali kuwa natsuwa babban rukuni


ce a cikin sallah, wanda sai ya samu ne take zama karvavviya a wurin


Allah. Wannan mas’ala babba ce matuqa. Domin kuwa Manzon Rahama


Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Sallar mutum ba zata zama


39


karvavviya ba har sai gadon bayansa ya zama shimfixe a lokacin da yake


ruku’i da sujada (Abu Dwuda: 1/533).


Ko shakka babu, rashin cikakkiyar natsuwa a sallah ba abu ne mai kyau


ba. Kuma duk wanda ke haka ya cancanci gargaxi da faxakarwa da


alwashin horo na musamman.


Abu Abdillahil Ash’ari ya riwaito cewa: Wata rana Manzon Allah


Sallallahu Alaihi Wasallama ya ba wa shabbansa wata sallah. Da aka


qare kuma ya zauna wurin tare da wasu daga cikinsu. Suna nan zaune a


haka, sai ga wani mutum ya shigo ya kabbarta sallah, yana ta qoton


kurciya. Kafin xan wani lokaci ya sallace.


Sai Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Kun ga


yadda mutumin nan ya yi sallah ko? To, duk wanda ya mutu yana irin


wannan sallah bai mutu a kan addinin Muhammadu ba. Kuma sallarsa ba


ta da banbanci da hankaka a lokacin da take qoton jini. Mai irin wannan


sallah kuma daidai yake da mayunwacin da zai ci qwarar dabino xaya ko


biyu. Kuna ganin za su amfane shi? (Ibnu Khuzaimah 1/332).


Haka kuma Zaidu xan Wahabu ya ce: Huzaifah ya ga wani mutum


na sallah, yana ruku’insa da sujada yadda ya ga dama sai ya ce masa:


“Sallarka bata yi ba. Kuma da zaka mutu yau ka sani ba zaka mutu a kan


addinin da Allah Ya saukar wa Muhamadu Sallallahu Alaihi Wasallama


ba (Bukhari: 2/274).


Don haka, duk wanda yake da masaniya da waxannan hadisai, ya


kuma qi yin sallah cikin natsuwa, to wajibi ne ya sake ta, ya kuma nemi


gafarar Allah akan abin da ya gabata. Don ko Manzon Allah Sallallahu


Alaihi Wasallama ya ce wa mai munana sallarsa: “Je ka sake wannan


sallah, don ba ta yi ba”. Amma fa ba lalle ne sai ya maimaita gaba xayan


sallolinsa da suka gataba ba.



Posts na kwanan nan

FALALAR AZUMIN KWANA ...

FALALAR AZUMIN KWANA SHIDA SHAWAL

TAKAITACCEN BAYANI MA ...

TAKAITACCEN BAYANI MAI ANFANI GA SABON SHIGA MUSULUNC

ZIKIRAI WADANDA AKE Y ...

ZIKIRAI WADANDA AKE YIN SU DA SAFE DA KUMA YAMMA

BIDI’AR ‘YAN SHI’A A ...

BIDI’AR ‘YAN SHI’A A RANAR ASHURA