Labarai

ALAKA TSAKANIN AHLUL - BAITI


DA SAHABBAI


Gabatarwar mai fassara:


A ranar 29 ga watan Ramadan na wannan shekarar ne


ta 1423B.H. na hadu da wani dattijo a cikin babban


masallacin Makka mai alfarma, kuma sauraron karatu ne


ya hada mu da shi. Wannan dattijon dai daga baya na


fahimci cewa, shi ma malami ne kuma alKali a wata


babbar kotun shari`a ta garin Kadif a Kasar Saudiyyah.


Saduwarmu da wannan malami ke da wuya sai na


fahimci irin kishin da ya ke da shi game da yada addinin


musulunci da gusar da yana daga aKidunsa. Nan take dai


wannan bawan Allah ya fito da wani dan littafi Karami ya


ba ni kyautarsa. A lokacin da na koma masaukina na samu


natsuwa na karanta wannan littafi, sai na taras littafi ne mai


matuKar amfani wanda ya tara ilmi mai yawa da hujjoji


Kwarara masu kare martabar sahabban manzon Allah


(S.A.W) daga abin da ake jingina ma su, na Kiyayya da


gaba a tsakaninsu da Ahlul Baiti – iyalan gidan Manzon


Allah (Allah Ya jiKansu baki daya). Ga shi kuma littafin


4


ya Kunshi labarai masu dadi a kan zamantakewa da huldar


da ke a tsakaninsu.


A lokacin da na sake nazari akan wannan littafin sai


na gane ashe wanda ya ba ni littafin nan dai shi ne


mawallafinsa. Don haka na yanke shawarar zan nemi


izninsa akan fassara wannan littafi zuwa harshenmu na


Hausa domin amfanin jama`armu. Alhamdu Lillahi, a


kashegari na samu izni daga wurinsa. Allah Ya saka ma sa


da mafi kyawon alherinsa, Ya ba mu aljanna firdausi akan


wannan aiki mai amfani.


A nan zan so in sanar da mai karatu cewa, na yi sauye


-sauye da dama a cikin wannan littafi amma ban canza ma


sa ma`ana ba, sai na kusanto shi sosai zuwa ga dan uwana


malam bahaushe, ta yadda mai karatu ba zai rinKa jin wani


harshe ne ma a ke fassara ma shi ba. Saboda haka na Kara


ma littafin nau`oin ado na magana irin ta Hausa don Kara


nashadantar da mai karatu ta yadda ba zai Kosa ko ya


gajiya daga karatun ba.


Kamar haka ne dai kuma na Kara inganta littafin ta


hanyar koma ma littafan da mawallafin ya yi nazarinsu a


wajen rubuta shi, sawa`un littafan Ahlus Sunna ko na


Shi`ah, har ma na sanya lambar sifili da shafukan da aka


nazarta – ga in da bai sanya ba - domin mai buKatar ya


5


koma ga resu. Haka kuma ban yi rowa ba game da duk


wani Karin haske ko sharhi wanda zai gamsar da mai


karatu, amma kuma wannan sai na sanya shi a Kasan


littafin, kuma da Karamin rubutu.


Fatar da ni keyi daga mai karatu ya yi mani tukuici da


addu`a ta alheri, ni da mawallafinsa idan har littafin ya


kasance mai amfani a ga reshi. Idan kuwa hakan ba ta samu


ba, to, uzurinmu dai shi ne, mun so mu yi nasiha ne ga


jama`ar musulmi, kuma muna fatar ba za mu rasa ladar


wannan kyakkyawar niyyar ba.


Yanzu dai sai in ce, dan uwa a yi karatu lafiya.


Muhammad Mansur Ibrahim


Sakkwato


28 ga Zul Ki`dah 1423B.H.


6


Gabatarwar Mawallafi:


Babu shakka cewa, Manzon Allah shi ne fiyayyen


talikkai. Wannan abu ne da duniya duka ta sani, Kuma


wata ni`imar Allah ce da Ya hada Musulmai akan sanin


haka. A nan ba mu kulawa da maganganun wasu `yan


tsiraru da su ke fifita sashen Imamai1 ko Waliyyai akan


Manzon Allah ta fuskar ilmi ko wani abu. Irin wadannan


kalamai za ka iske wadanda suka yarda da masu fadarsu


ma tawilanta su su ke yi ko kuma su raunana su.


Babu wanda yake shakka game da matsayin da Allah


Ya ba ManzonSa na kasancewarsa ma`abocin ceto mafi


girma, ga kuma tafkin da Allah Ya ba shi na Alkausar da


sauran darajojinsa na duniya da lahira.


Haka kuma babu shakka cewa, wadannan albarkoki


da alherori na Manzon Allah sun shafi iyalansa da


makusantansa wadanda suka gaskata shi kuma suka


taimake shi.


Saboda haka zamu ga darajojin iyalan gidan Manzon


Allah suna da yawa, kuma sun zo a cikin AlKur`ani da


Hadissai da dama, kuma sun hada da duk iyalansa na


lokacinsa da kuma zuri`ar da suka haifa har ranar


1 Al majlisi a cikin Bihar al Anwar ya Kulla babi da ya sa ma sa


suna: "Babi a kan cewa, Imamai sun fi Annabawa ilmi" (2/82).


Duba kuma: Usul al Kafi na Kulini (1/227). – Daga mai littafi.


7


AlKiyama. Sa`annan kuma duk wasu nassoshi da suke


bayyana falalar Sahabbai, to iyalan Manzon Allah na


cikinsu.


A cikin littafinmu na farko mun yi bayanin darajjojin


wadannan Sahabbai. A cikin wannan dan littafi kuwa zamu


bayyana kyakkyawar alaKar da ke tsakanin Ahlul Baiti da


Sahabbai. Bai kamata mu gajiya da Magana a kan


abokantaka da manzon Allah da irin falalarta ba, da


lizimtar da ke tsakanin wannan manzo mai albarka wanda


albarkar zama da shi su ka samu martabar zama sahabbai.


Darajojinsu kuma sun banbanta ne a aljanna daidai


gwargwadon ayyukansu da jihadinsu tare da shugaban


manzanni.


Haka ma a nan duniya sahabbai sun kasu kashi uku:


Muhajirai da Ansarai da na bayansu kuma duk Allah Ya yi


mu su alKawalin shiga aljanna. Kamar yadda Madaukakin


Sarkin Ya fda in da Ya ce:


Ma'ana:


Wanda ya ciyar a gabanin cin nasara, kuma ya yi


yaKi a daga cikinku, bay a zama daidai (da wanda


8


bai yi haka ba). Wadancan ne mafifita girman


daraja bisa ga wadanda suka ciyar daga baya


kuma su ka yi yaKi. Kuma dukansu Allah Ya yi


mu su wa'adi da (sakamako) mai kyau, kuma


Allah Masani ne ga abin da ku ke aikatawa.


Suratul Hadid, Aya ta 10.


Haka ne. Dukkansu su na da falalarsu da darajarsu.


Kuma tilas ne a kanmu mu gane girma sahibantar manzon


Allah (S.A.W), mu gane cewa, wani matsayi ce mai zaman


kansa. Sahabbai magabata wadanda su ka fara rungumar


musulunci su na da daraja mafi daukaka. Wadanda kuma


Allah Ya hada ma su biyu: tsakanin sahibtaka da zumunta


– Ahlul Baiti kenan- su na da darja biyu kenan. Kuma


darajojinsu na daidai da aikin ko wanensu. Allah Ya yi


tsira ga resu da yarda baki daya.


Ya kai dan uwana mai karatu!


Yana da kyau ka sani cewa, tare da abin da Allah Ya


Kaddara a tsakanin wadannan zababbun mutane – wadanda


suka abokanci fiyayyen talikkai – na fitina da sabani wanda


har ya kai zuwa ga yaKar junansu, bai hana su Kauna da


rahama ga junansu ba. Wannan kuwa yana nuni zuwa ga


cewa da yawan ruwayoyi da Kissoshin da ake yadawa a


kansu ba gaskiya ba ne, duk kuwa da ya ke wasu marasa


9


hankula da nazari da kuma wasu masu ra`ayoya na son


zuciya sun yi anfani da wadannan ruwayoyi domin cim ma


gurinsu na fadada sabani da rikice-rikice a cikin wannan


al`umma.


Kira


Zuwa ga wadanda su ka damu da yin bincike da


rubutu a kan tarihin wannan al'umma, da masu kira zuwa


ga hadin kan musulmi.


Zuwa ga masu Magana a kan ci gaban wannan


zamani da hadarin da al'ummar musulmi ta ke fuskanta


wanda ya wajabta mu hada kanmu don tunkarar


matsalolinmu.


Zuwa ga duk wani mai kishin ci gaban wannan


al'umma ni ke cewa, me ya sa mu ke tsokano matsaloli na


tarihin al'umma da ya gabata alhalin kuwa yin haka ya na


iya haifar da gaba da Kiyayya a tsakaninmu ? Me ya sa mu


ke yin haka ba tare da yin nazari da bincike ba ? Don me ne


ne ? Don neman jama'a ? Ko don kwaikwayon wasu ? Ko


don neman wani abin duniya ?.


Sai ka tarar da wasu marubuta da masu bincike suna


kashe lokaci mai yawan gaske wajen tsokaci game da wasu


mas`aloli na tarihi wadanda aka gina su akan ruwayoyi


masu rauni, ko aka rubuta su bisa ga son zuciya. A daidai


10


lokacin da suke ganin sun yi KoKari akan wannan bincike


in da za ka tambaye su me ne ne fa`idar abin da suka gano


kuma da me ne ne zai Karashi wannan al`umma ? ba zaka


samu wata amsa ba face dai wannan bincike nasu zai Kara


fadada baraka da rarraba da jin takaicin juna a cikin


wannan al`umma. To, a bisa wane harsashe na ilmi su ka yi


wannan bincike ?.


Mun fada a littafin da ya gabata akan sahabbai cewa,


aikin Manzon Allah ne wanda Allah Ya dora masa ya yi


tarbiyyar wadanda Allah Ya girmama su da samun


musulunta a hannunsa da abokantakarsa – wato Sahabbai –


kamar yadda Allah buwayayyen Sarki Yake cewa:


Ma`ana:


(Allah) Shi ne Wanda Ya aika a cikin jahilai wani


Manzo daga gare su, yana karanta ayoyinSa a


kansu, kuma yana tsarkake su, kuma yana sanar


da su littafin (AlKur`ani) da hikima (Sunna), ko


da yake sun kasance daga gabaninsa lalle suna a


cikin bata bayyananne.


Suratul Jum`ah, Aya ta 2.


11


Wadannan su ne wadanda manzon rahama da shiriya


ya tsayu a kan tarbiyyarsu da karantar da su. Mun yi


magana a kan lizimtar da ke tsakanin jagora (shi ne annabi


(S.A.W) da rundunarsa). Manzon Allah shi ne abin


koyinsu, kuma shi ne maKwaucin da su ka yi rayuwa da


maKwautaka tare da shi. Manzon Allah (S.A.W) shi ne


shugaban da suka kasance KarKashinsa. Su ne


talakawansa, kuma su ne sahabbansa. Wannan bayanin ya


gabata a littafi na farko.1


1 Sahabbai su ne almajiran Manzon Allah wadanda aka ce ya


tsarkake su. Idan mun kira shi Liman, to su ne Mamunsa, Idan


kuma mun ce kwamanda, to su ne sojojinsa. Idan ya kasance


shugaba, har wa yau su ne talakawansa. Idan kuma an umarci


Manzo da ya karbi zakka to daga wurinsu ne zai karba. Idan kuma


an ce ya bayar da ita, su din ne zai bai wa. Haka ma idan an umurce


shi da ya kyautata ma maKwauta, to su ne maKwautan nasa. Don


haka, ba zai yiwu a raba daya biyu ba. Idan har mutun ya yi suka ga


wadannan almajirai to, yana zargi ne da tuhuma ga malaminsu. Mu


kam dai Ahlul Sunnah mun yi amanna cewa, Manzon Allah


(S.A.W) ya yi aikin da aka dora ma sa na yi masu tarbiyya


kyakkyawa wadda a sakamakonta ne suka siffaitu da kyawawan


dabi`un da suka hada da Kaunar junansu da jin tausayi a tsakaninsu


har suka zamo al`umma mafi alheri wadda aka fitar ma mutane.


(Duba AlKur`ani, Suratu Ali Imrana, Aya ta 110). Siffofin


wadannan Sahabbai kyawawa suna da tarin yawa. Kuma duk wanda


yake karanta AlKur`ani ya san da haka.


12


Ya dan uwa mai karatu!


Babu shakka a wurinka cewa manzon nan (S.A.W) ya yi


kyakkyawar tsayuwa a kana bin da Allah Madaukakin Sarki Ya


umurce shi na isar da manzanci da tarbiyyar sabbai da


karantar da su da sauransu. Kuma sakamakon wannan


tarbiyya ce su ka sami kyawawan dabi'un da a ka sansu da


su, kai har ma Allah Ya kira su


Ma'ana:


"mafi alherin al'ummar da a ka fitar saboda mutane".


Suratu Ali Imran, Aya ta 110.


Lura da cewa :"a ka fitar". Wa ya fitar ? Wa ya ba su


wannan matsayi ?. Wannan ayar dai dai ta ke da wata ayar


in da Allah Ya ke cewa:\


Ma'ana:


Kuma kamar haka ne Mu ka sanyan ku al'umma


matsakaiciya domin ku kasance masu bayar da


shaida a kan mutane. Kuma Manzo ya kasance


mai shaida a kanku.


Suratul BaKara, Aya ta 143.


13


Ayoyin da Allah Ya saukar a kan yabonsu su na da tarin


yawa. Ga kuma wasu sun gabata ba sai mun maimaita ba.


Wannan littafi:


A cikin wannan dan littafi zan yi magana akan siffa


daya ce kacal daga cikin siffofin da AlKur`ani ya bayyana


Sahabban Manzon Allah da su. Wannan siffar kuwa ita ce


Rahama wato tausai a tsakaninsu. Zan taKaita magana


akan wannan siffa saboda dalillai kamar haka:


1- Saboda muhimmancin wannan siffa da girman


ma`anonin da ta tara, kasancewarta daya daga cikin


siffofin Allah da siffofin ManzonSa.


2- Allah (S.W.T) ne da kanSa Ya zabi wannan siffa a


wajen yabo ga wadannan bayi naSa, Yana mai kore


zace – zace da Karyace-Karyacen maruwaita. Ka


duba yadda Allah Ya sifaita su da wannan siffa a


cikin Suratu Muhammad in da buwayayyen Sarkin


Ya ke cewa:


14


Ma`ana:


Muhammadu manzon Allah ne. Kuma wadannan


da ke tare da shi masu tsanani ne a kan kafirai,


masu rahama ne a tsakaninsu, ka na ganinsu suna


masu ruku'i masu sujada, suna neman falala daga


Ubangijinsu, da yardarSa. Alamarsu tana a cikin


fuskokinsu, daga kufan sujuda.


Suratul Fathi, Aya ta 29.


3- Dalili na uku kuwa – ya kai dan uwana mai karatu –


shi ne, la`akari da yawan gurbatattun ruwayoyi masu nuna


cewa, akwai adawa da gaba a tsakanin Sahabbai har ma


mutum ya kan zaci ana magana akan wasu dabbobin daji


ne ba wasu mutanen kirki da Annabin rahama yayi ma su


tarbiyya ba, wannan kuwa ya kan haifar da mummunar


adawa da Kyama a cikin zukatan masu karatu akan


magabatan nan nasu na kirki. Alhali kuwa Allah Mahalicci


Ya neme mu ne da mu so wadannan bayin naSa, mu yi ma


su addu`a, mu kuma nisanci Kyama da tsanuwa akansu,


kamar in da Allah Ya ke cewa:


15


Ma`ana:


Kuma wadanda suka zo daga bayansu (bayan


Muhajiruna da Ansar da aka ambata a ayoyin da


su ka gabata) suna cewa, `Ya Ubangijinmu ! Ka


yi gafara a gare mu, kuma ga `yan `uwanmu


wadanda suka riga mu yin imani, kada Ka sanya


wani Kulli a cikin zukatanmu ga wadanda suka


yi imani. Ya Ubangijinmu ! Lalle Kai ne Mai


tausayi, Mai jinKai.


Suratul Hashri Aya ta 10.


4- Sanin dukkan wani mai bincike ne cewa, ana buKatar


a tace ruwayoyi ta hanyar nazari game da


maruwaitansu da kuma duba gundarin abin da suka


Kunsa. To amma kuma sai ya kasance ire-iren


wadannan ruwayoyi ana ta yada su ba tare da la`akari


da wadanda suka ruwaito su din ba tare da


kasancewar galibinsu daga cikin shahararrun


maKaryata ne. Ga kuma uwa uba zamowar wadannan


ruwayoyin sun zo da akasin abinda AlKur`ani kansa


ya ke tabbatarwa na tsarkin zukatan wadannan bayin


allah da Kaunatar juna da ke a tsakaninsu. Idan ma


har ka binciki littafan da aka samo wadannan


16


ruwayoyi a cikinsu sai ka taras irin littafan nan ne da


aka wallafa su domin shaKatawa da bayar da


labarurruka na ban mamaki da makamantansu, ba wai


littafai ne na ilimi wadannan Malamai magadan


Annabawa su ka rubuta ba.


Ya kai dan uwana mai karatu ! Ina fatar kada ka yi


gaggawar yanke hukunci da yin suka da zargi don kawai


abin da ya ke a cikin tunaninka na labaran tarihi, ka dakata


har sai ka ji irin hujjojin da ni ke sonn in fada ma ka,


domin hujjoji ne wadanda ba a saba da su ba, duk da


bayyanarsu da kusancinsu da kuma Karfinsu. Haka kuma


ina son in ba ka shawarar ka sake komawa a karo na biyu


zuwa ga ayoyin da muka ambata ma ka a sama, ka yi ma su


karatun mai basira domin ka gane maganar da ni ke fada


ma ka. Musamman ma dai ka sake nazarin wadannan


ayoyin guda biyu:


Aya ta farko:


Ma`ana:


Muhammadu manzon Allah ne. Kuma


wadannan da ke tare da shi masu tsanani ne a kan


kafirai, masu rahama ne a tsakaninsu, ka na ganin


suna masu ruku'i masu sujada, suna neman falala


daga Ubangijinsu, da yardarSa. Alamarsu tana a


cikin fuskokinsu, daga kufan sujuda.


Suratul Fathi, Aya ta 29.


Aya ta biyu:


Ma`ana:


Kuma wadanda suka zo daga bayansu (bayan


Muhajiruna da Ansar da aka ambata a ayoyin da


su ka gabata) suna cewa, `Ya Ubangijinmu ! Ka


yi gafara a gare mu, kuma ga `yan `uwanmu


wadanda suka iga mu yin imani, kada Ka sanya


wani Kulli a cikin zukatanmu ga wadanda suka


yi imani. Ya Ubangijinmu ! Lalle Kai ne Mai


tausayi, Mai jinKai.


18


Suratul Hashri Aya ta 10.


Karanta wadannan ayoyi, ka sake nazarinsu. Allah Ya


yi ma ka jagora. Amin.


19


BINCIKE NA DAYA: AKAN SUNAYEN SAHABBAI


Abin da mu ka sani ne cewa, sunan mutum shi ne


adireshinsa wanda ya ke nuna ko shi wane ne ko kuma


wane iri ne. Da sunan mutum ka ke gane addininsa da irin


hankalinsa. Misali ai ba mu taba ganin wani bayahude ya


sanya sunan Muhammadu ba. Ko ka taba ganin Musulmi


da sunan Lata ko Uzza?.


Saboda haka Suna yana da muhimmancin gaske.


Kuma da sunan mutum ne iyayensa da danginsa da sauran


jama`a su ke kiransa. Da shi ne kuma mutum ya ke


banbanta da wanda ba shi ba. Don haka ne ma addinin


Musulunci ya yi umurni ga uba da ya kyautata zaben suna


ga `ya`yansa. Kai har ma Annabin Rahama (S.A.W) ya


canza ma wasu sahabbai maza da mata sunayensu saboda


rashin dacewarsu, domin iyayensu ba su zaba ma su sunaye


na gari ba. Bugu da Kari babban birnin da Manzon Allah


ya yi hijira zuwa ga reshi sai da ya canza ma sa suna daga


Yasriba sunan da akwai ma`anar zunubi a cikinsa zuwa


Daiba mai ma`anar daddadan birni.


Kamar haka ne kuma Manzo (S.A.W) ya yi nuni


zuwa ga kyawawan sunaye kuma dadadansu har ma ya fadi


wadanne sunaye ne mafifita a Musulunci wato Abdullahi


da Abdur Rahman. Kuma ya yi nuni ga wasu sunaye da ba


20


su dace ba kamar "Sarkin sarakuna" da makamantansu.


Wannan ya sa malamai sun yawaita bincike a kan mas'alar


sunaye, kuma sun wallafa littafai da dama a kan haka.


To, a nan zan yi tambaya ga reka ya kai mai karatu :


Da me ka ke kiran `ya`yanka? Shin da irin sunayen da ka


ke so kuma ka ke Kaunar ma`abotansu? Ko kuma da


sunayen maKiyanka wadanda ka ke adawa da su kuma ka


ke Kyamar su?!. Idan ka amsa wannan tambaya to, me za


ka ce idan ka san cewa, Sahabban nan da ka ke jin a tarihi a


na cewa, su na adawa da gaba sunayen junansu su ke


sanyawa?. Ina fatar kada ka yi gaggawa har sai ka yi


nazarin misalan da ni ke son kawo ma ka. Idan ka duba su


sai ka yi amfani da hankalinka da basirar da Allah Ya ba


ka, na tabbata za ka hango abin da na hanga a cikin yardar


Allah.


Ga wasu `yan misalai a gurguje:


1- Sayyiduna Ali dan Abu Talib (R.A) yana da `ya`ya


ukku wadanda ya sanya ma su sunayen Abubakar da


Umar da Usman kuma dukkansu sun yi shahada a


Karbala` tare da dan uwansu al- Hussain (Allah ya


jiKansu baki daya).1


1 Al`amarin da ya faru a Karbala` yana da ban takaici a cikin


tarihin wannan al`umma. Amma kuma Allah Ya riga Ya rubuta


faruwarsa, ya kuma faru din a bisa ga yadda Allah Ya Kaddara shi.


21


2- Al Hassan dan Ali dan Abu dalib shi ma yana da


`ya`ya masu sunaye kamar haka: Abubakar da Umar


da Talha su ma kuma suna daga cikin wadanda


sha`anin Karbala` ya rutsa da su (Allah Ya jiKansu).


3- Al Hussaini dan Ali dan Abu dalib (wanda aka kashe


a bisa zalunci da Keta a Karbala`) shi ma yana da da


mai sunan Sayyiduna Umar.


4- Ali dan Hussaini dan Ali dan Abu dalib (Wanda aka


fi sani Zainul Abidin) yana da `ya mace wadda ya


sanya ma ta sunan A`ishah, yana kuma da da namiji


mai suna Umar.


Ya kai dan uwa mai karatu ! ko akwai buKatar in ci


gaba da jera irin wadannan sunaye? Ko hankalinka zai


yarda cewa, wadannan bayin Allah suna adawa da junansu


Wajibinmu a yanzu shi ne, mu kwatanta adalci a game da jingina


laifin kisan Husaini da `yan uwansa da wasu daga cikin iyalinsa.


Dalili kuwa shi ne, ruwayoyi sun sha banban da juna akan wannan


lamari. Kuma babu shakka cewa, Yazidu dan Mu`awiyah bai yi


umurni da a kashe su ba, bai kuma yi farin ciki akan kisan su ba.


Abin da ya yi umurni da shi shi ne a hana su isa IraKi in da `yan


shi`a su ka yi alKawalin nada Husaini a matsayin shugaba na biyu


bayan kuwa ga tsayayyen shugaba wanda ke gudanar da mulki,


wato Yazidu. To, a fagen nan fa na tare su daga isa birnin IraKi


Allah Ya hukunta al`amarinSa in da wasu tsiraru su ka kai farmaki


akan su bayan duk tattaunawar da aka yi ba ta ci nasara ba. Yazidu


kuma ya nuna damuwa ainun akan wannan abin da ya auku, ya


kuma yi rantsuwa cewar bai yi umurni da haka ba, kuma ba haka ya


ke nufi ba. Amma ina abin yi bayan mai aukuwa ta riga ta auku?.


Allah Ya kare mu daga fitina.


22


ne amma kuma su ka sanya ma `ya`yansu sunayen abokan


adawarsu domin wata manufa ta siyasa ko wani abu?. Ka ci


gaba da bincike kuma a cikin tarihin zuri`oin Ahlul Baiti


kamar gidan Abbas dan Abdul Muddalib da zuri`ar Ja`afar


dan Abu dalib kuma Kanen Sayyiduna Ali da zuri`ar


Muslim dan AKilu dan Abu dalib da sauran Ahlul Baiti za


ka yi mamakin gaske idan har kana cikin masu zaton akwai


adawa a tsakaninsu da sauran Sahabbai musamman ma


Khalifofin Manzon Allah guda ukku na farko(Allah Ya


yarda da su).


Mene ne matsayin `yan shi`a akan wannan lamari?


To, daga cikin shi`awa akwai wadanda suka musanta


wannan magana cewa, Sayyiduna Ali da `ya`yansa sun


sanya sunayen manyan khalifofin Manzon Allah (S.A.W)


guda ukku da Nana A`ishah diyar SiddiKu da


makamantansu daga cikin makusantan Manzon Allah


(S.A.W) domin wannan ya ci karo da abin da su ka ba da


gaskiya gare shi na haifuwar adawa da gaba a tsakaninsu.


Sai dai kuma malaman Shi`a kansu sun mayar da martani


akan wannan magana kasancewarta a rubuce a cikin


manyan littafansu, al`amarin da wasu daga cikinsu ke


ganin dasisa ce ta Ahlus Sunna. Idan ko su ka bude ma


kansu wannan Kofa to, mu kuma za mu tuhumce su da


23


rashin aminta da littafansu wadanda suka bayyana sunayen


nan da mu ka ambata musamman ma dai wadanda suka yi


shahada a Karbala` kamar Abubakar dan Ali dan Abu dalib


da Abubakar dan Hassan dan Ali. Wasu ruwayoyin ma sun


bayyana Umar dan Ali da Umar dan Hassan a matsayin


manyan barade wadanda suka nuna zarunta mai yawa a


filin daga ranar Karbala`. To, da yaya Ahlus Sunna su ka


miKa hannuwansu a cikin wadannan littafai naku su ka


soka wadannan bayanai? Ashe kenan ku ma ba ku aminta


ba da littafanku. Don haka sai ku bar su domin ku koma ga


gaskiya. Allah Ya sa mu dace.


To, daga cikin malaman Shi`a wadanda suka nuna


amincewa da gaskiyar wadannan ruwayoyi akwai masu


ra`ayin cewa, Sayyiduna Ali ya sanya wa `ya`yansa


wadannan sunaye ne domin taKiyyah ma`ana wai yana son


ya nuna wa wadannan khalifofi cewa yana tare da su alhali


a haKiKanin gaskiya shi maKiyinsu ne. Wannan maganar


kuwa ita kanta suka ce babba ga matsayin Sayyiduna Ali


da irin jaruntakar da aka san shi da ita, ace jin tsoronsa da


rauninsa sun sanya shi har yana daukar matakai na kada


aga laifinsa!. Wannan suka ce babba wadda muke nisantar


da darajar Sayyiduna Ali daga irinta.


TUSHEN BAYANI:


24


Duba wadannan sunayen da ma wasu ba su ba a cikin


littafan Shi`a din kan su kamar:


1- Kashful Gummah (2/334)


2- Al fusulul Muhimmah shafi na 283


3- A`lamul Wara na Tabarsi shafi na 203


4- Al Irshad na Mufid shafi na 186


5- Al Tarikh na Ya`Kubi shafi (2/213) da sauran su.


Sakamakon Bincike:


Wannan al`amari ya tabbata haka shi ke, shahararrun


magabata daga cikin Ahlul Baiti su na farin cikin sanya ma


`ya`yansu sunayen Abubakar da Umar da A`ishah da Talha


da makamantansu domin Kaunatayyar da ke tsakaninsu da


sanin matsayinsu da darajarsu wadanda su ka ribata a


sakamakon kusancinsu da Manzon Allah (amincin Allah ya


tabbata gare shi). Gaskatar wannan magana kuwa yana nan


a cikin AlKur`ani a cikin ayoyin da suka gabata da kuma


Karshen Suratu Muhammad in da Ya ke cewa:


Ma`ana:


Muhammadu manzon Allah ne. Kuma


wadannan da ke tare da shi masu tsanani ne a kan


25


kafirai, masu rahama ne a tsakaninsu, ka na ganin


suna masu ruku'i masu sujada, suna neman falala


daga Ubangijinsu, da yardarSa. Alamarsu tana a


cikin fuskokinsu, daga kufan sujuda.


Suratul Fathi, Aya ta 29.


Sake karanta wannan aya ka Kara tunani a kan


rahamar da Allah Ya ce akwai a tsakaninsu.


26


BINCIKE NA BIYU : GAME DA AURATAYYA


A TSAKANINSU:


Dangantaka a tsakanin `yan adam iri biyu ce:


dangantakar jini da ta auratayya. Allah Ta`ala Yana cewa:


Ma`ana:


Kuma (Allah) Shi ne wandaYa halitta mutum


daga ruwa, sai ya sanya shi zumunci da sarakkuta,


kuma Ubangijinka Ya kasance Mai iko ne.


Suratul FurKan Aya ta 54


Sanin kowa ne cewa, aure alama ce ta yarda. Misali


mutum ba zai dauki `yarsa ya bayar ga wanda ya ke


shawaraki ne ba ko mutumin banza ballantana ma a ce


maKiyinsa wanda ma shi ne ya kashe uwar yarinyar ko dan


uwanta.


Matsayin Larabawa game da Sarakkuta:


Sarakkuta tana da wani matsayi na musamman a


wajen Larabawa domin kuwa ba su aurar da `ya`yansu


mata sai ga wanda ya yi daidai da irin matsayin ubannensu


ta fuskar dangantaka domin kada ta wulaKanta. Kishin da


balarabe ya ke da shi akan `ya`yansa mata da jin sauna


akan su gamu da wulaKanci shi ne ya haifar ma su da


27


mugunyar dabi`ar nan ta turbude `ya mace da ranta da


lafiyarta, al`adar da addinin Musulunci ya rosa ta, ya mayar


da Larabawa bisa ga dabi`u managarta. A bisa gaskiya ma


an yi ta samun yaKe-yaKe a tsakanin Larabawa wadanda


musabbabinsu shi ne kishi akan `ya mace.


Matsayin musulunci game da Sarakkuta:


Haka ma a addinin Musulunci za mu samu cewa, an


yi umurni da mutum ya zabi mace ta gari, haka shi ma


uban diya ya nema ma ta miji na gari. Malaman FiKhu sun


tsawaita bincike akan mas`alar Kafa`ah wato irin namijin


da ya cancanta waliyyin mace ya amince da daura ma sa


aure da ita. An yi maganganu daban-daban akan sana`ar


mutum da dangantakarsa da makamantansu. Amma abin


da babu sabani a kansa shi ne, wajabcin la`akari da addini


ga duk wanda za`a ba shi auren mace musulma.


A game da kishi akan `ya`ya mata kuwa, Annabi


(S.A.W) ya ce, duk wanda aka kashe shi a wajen kariyar


irlinsa (Matarsa ko `yarsa) to, wannan mutum ya yi


shahada. A dalilin keta mutuncin `ya mace guda ne Annabi


(S.A.W) ya ba da sanarwar yaKi da yahudawan KainuKa`a


a lokacin da wani daga cikinsu ya kware ma ta zane a


kasuwa. Annabi (S.A.W) ya yi haka ne kuwa bayan ya


Kulla alKawalin zaman lafiya da su, amma sai ya dauki


28


wannan keta mutuncin `ya macce musulma da daya daga


cikinsu ya yi a matsayin kwance alKawali daga bangaren


yahudawan tare da abin da ya biyo bayan wannan na


kashewar da wani musulmi ya yi wa wancan bayahuden


dan ta'adda da kuma kashewar da shi ma yahudu su ka yi


ma sa.


Haka ma idan mu ka yi la`akari da wasu hukuncehukunce


na Shari`a kamar shardanta waliyyin macce ga


daura aure da wajabta shedu da haramta zina da sanya


haddi ga wanda ya yi ta, duka wadannan su na nuna yadda


kariyar mutuncin macce ya ke da matsayi a Musulunci.


A dalilin sarakkuta ma Shari`a ta kan haramta ma


mutum auren wasu mata na har abada ko ta hana shi auren


wata matuKar yana aure da wata.


Ya kai dan uwana mai karatu ! duk abin da ya gabata


shinfida ce mai nuna maka cewa, auratayyar da ta gudana a


tsakanin Sahabbai da Ahlul Baiti babbar alama ce ta


amincewa da junansu da Kauna a tsakaninsu. Bari dai anan


ma mu ba ka wasu `yan misali. Ko ka san:


1- Sayyiduna Ali dan Abu dalib ya aurar da Ummu


kulsum Kanwar Hassan da Hussaini ga Khalifa Umar


dan Khaddab? Ita ce kuma ta Haifa ma sa Zaidu dan


Umar da RuKayyah diyar Umar. Ko kana mamakin


29


wannan ? Me ya sa Umar ba zai auri diyar Fatima ba


alhalin kuwa shi kansa baban Fatima (S.A.W) ya auri


`yarsa, ita ce Hafsah Uwar muminnai ? Ko ka na


ganin tsoro ne ya sa sayyiduna Ali ya aurar da 'yarsa


–jikanyar manzon Allah (S.A.W)- ga surukin


manzon Allah –sayyiduna Umar ? Ina jaruntakar ta


sa? A wurin azzalumi ya kai ta ? Ina tsoron Allansa


da kishin addininsa ? Ko ko dai ka yarda cewa, Ali ya


aurar da 'yarsa ne ga Umar da ya aminta da shi da


kuma addininsa ? domin ba komai a tsakaninsu ban


da Karairayin 'yan shi'ah ?.1


2- Muhammadu dan Abubakar SiddiKu ya haifi da


AlKasim wanda shi kuma ya ba da auren `yarsa


Ummu farwah ga Muhammad dan Ali dan Hussain


dan Ali dan Abu dalib (Wato dai jikanyar Abubakar


SiddiKu ce aka hada ta aure da jikan sayyiduna Ali


kuma jikan Manzon Allah (S.A.W). Ummu farwa


kuwa ita ce ta haifi Ja`afar al SadiK wanda `yan


Shi`ah suke dogara kacokan ga ruwayoyinsa. An


ruwaito shi Ja`afar al SadiK yana cewa, Sayyiduna


Abubakar ya haife ni sau biyu. Me ya sa haka?


1 Bayan rasuwar sayyiduna Umar (R.A) Abdullahi dan Ja'afar dan


Abu dalib shi ne ya aure ta.


30


Domin daman can ita mahaifiyarsa Ummu farwa


uwarta ita ce Asma`u diyar Abdul Rahman dan


Abubakar SiddiK.


3- Zaidu dan Harisah – wanda shi kadai ne sunansa ya


zo cikin alKur'ani- maula ne, ba baKuraishe ba.


Amma saboda darajar musulunci da sahibtakar


manzon Allah (S.A.W) shi ne ya auri Zainab diyar


Jahsh – 'yar uwar Nana Khadijah (R.A) – wadda


bayan sun rabu da ita Allah Ya daura ma manzonSa


aure da ita kamar yadda ya zo a cikin suratul ahzab.


4- Usamah dan zaidu dan Harisah – wanda babansa ya


gabata- manzon Allah ne ya aurar da Fatima diyar


Kais – BaKuraisha – a ga reshi.


5- Salim – maulan abu Huzaifa – abu Huzaifa ya aurar


ma sa da diyar dan uwansa, ita ce, Hindu diyar al


Walid dan Utbah. Gidansu kuwa ya na cikin mafi


girman gidajen Kuraishawa.


Auratayya a tsakanin dangin manzon Allah (Kuraishawa)


da zuri'arsa a daya bangaren da kuma sauran sahabbai a


bangare na biyu ta na da yawa Kwarai da gaske. Wadannan


misalai ne kawai.1


1 Daga cikin auratayyar da ya kamata mu sani a tsakaninsu akwai


auren da Sayyiduna Ali dan Abu dalib ya yi da matar Khalifa


Abubakar SiddiKu a bayan rasuwarsa. Wannan matar ita ce


31


Matsayin Malaman Shi`a akan auren Ummu kulsum da


sayyiduna Umar:


A game da aurar da Ummu kulsum `yar Sayyiduna


Ali zuwa ga Khalifa Umar kuwa wasu daga Malaman Shi`a


kamar al Mufid sun ce, wai da Karfi ne Sayyiduna Umar ya


dauke ta daga gidansu. Haka dai shi ma Kulini ya fada a


cikin Furu`ul Kafi (6/115) A yayin da al Majlisi a cikin


Asma`u Bintu Umais wadda daman can matar Ja`afar ce Kanen


Sayyiduna Ali kafin ya samu shahada a yaKin Mu'uta wanda


manzon Allah ya tura shi. Bayan rasuwarshi sai ta auri Abubakar.


Asma`u kuma ita ce ta haifi Muhammadu dan Ja`afar, sa`annan da


ta auri Abubakar shi ma ta haifa ma sa Muhammadu. A wata rana


wadannan `ya`yan nata sun yi jayayyar daraja a gaban mijinta


Sayyiduna Ali, sai ya ce ma ta, ki raba ma su gardama mana! Ita


kuma sai tace, to, kai dan Ja`afar Babanka ba irinsa a cikin matasa.


Kai kuma dan Abubakar Babanka ba irinsa a cikin dattijai. A cikin


raha da nashadi irin na mata da miji sai Ali ya ce ma ta, to wa ya


rage kenan? Yana nufin shi a wane matsayi ta ajiye shi?.


To, a yanzu dan Uwa ko ka lura da yadda sarakkuta ta ke a


tsakanin Ahlul Baiti kansu da sauran Sahabbai? Ko ka shaKi


Kanshin wata adawa tana gudana a tsakaninsu? Ko ko dai ka lura


al`amarin nasu yadda Allah Ya fade shi ne a ayoyin da malam ya


kawo ma ka su a baya?


Ko ka na iya lura tare da ni cewa, wanda ya ke suka ga


surukanka kai din ne ya ke suka a gare ka? Manzon Allah (S.A.W)


da kansa ne ya auri `yar gidan Abubakar (Nana A`ishah), sa`annan


ya auri `yar gidan Umar (Nana Hafsah), sa`annan ya aurar da `yarsa


RuKayyah ga Usman, da Allah Ya yi ma ta cikawa sai ya sake ba


shi wata `yar ta sa Ummu Kulsum, ita ma a lokacin da ta cika


Annabi (S.A.W) yace ma sa, a yanzu ba ni da wata `ya da na Kara


ba ka ita. To, saboda Allah idan `yan Shi`a su ka ce, wadannan


mutanen, Abubakar da Umar da Usman duk ba mutanen kirki ba ne


to, wa su ke nufin ba ya da kirki?!.


32


Mir'atul UKul (2/45) ya ke ganin wannan kuskure ne. Abin


da dai ya faru ga cewarsa, shi ne, Sayyiduna Ali ya bayar


da aurenta ne akan tilas bisa ga taKiyyah wato saboda jin


tsoro ke nan !!. To, amma kuma Safiyyuddin al TaKtaKi ya


tabbatar da wannan aure a cikin littafinsa wanda ya saw a


sunan al Tusi (shafi na 58). Shi ma al Raja'i ya cirato daga


Abul Hassan al Umar (Jikan Umar dan Ali dan Husaini)


wanda ya ce Abbas ne dan Abdul Muttalib ya bayar da ita


aure ga Sayyiduna Umar bisa ga yarda da amincewar


babanta. Amma kuma shi ne ya ruwaito cewa, wai wata


aljana ce ta ke fitowa da kamannun ita Ummu Kulsum a


duk lokacin da mijin na ta zai sadu da ita. Ta haka ne har ta


Haifa ma sa da Zaidu!!!.


Har wayau dai game da wannan aure, wani Malamin


Shi`ah a wannan zamani ya ba da amsa da cewa, auren dai


dai ya ke da auren Manzon Allah (S.A.W) ga Ummu


Habiba diyar Abu Sufyan alhalin yana mushriki..1


1 Wannan magana abar haushi ce, abar dariya!. Domin kuwa shi


Manzon Allah shi ne ya aura, ba aurar ma Abu Sufyan ya yi ba.


Kuma ita Ummu Habiba musulma ce shi ya sa manzon Allah Ya


aure ta. To, a ina ku ka sami musulmi ya aurar da 'yarsa ga wanda


ku ka ce kafiri ne ?.


Malam bai yi magana game da matsayin malaman shi'ah ba a


game da auren manzon Allah (S.A.W) da wadannan tsarkakakkun


`ya`ya na Abubakar da Umar (Ina nufin Nana A`ishah da Nana


Hafsah), a kan haka na ga ya dace in yi taKaitaccen sharhi a kai.


33


Sakamakon Bincike:


Tabbas dai Sahabbai sun kasance suna sarakkuta da


junansu ba tare da wani fargaba ba. Haka kuma su kansu


Ahlul Baiti sun kasance suna bayar da auren `ya`yansu ga


sauran Sahabbai. Babu shakka kuma duk mai hankali ya


san wannan abu ne mai nuna aminci da Rahama da Kauna.


Duk tawilolan da Malaman Shi`ah su ka yi babu wanda ya


ke da wata makama ta hankali wadda ake dogara ga re ta.


Domin aure abu ne da ba shi yiwuwa sai da Kauna da


soyayya a tsakanin ma`aurata, sa`annan da fahimta da


mutuntawa a tsakanin dangogansu. Abin da muka kawo na


misalai kuwa kadan ne daga cikin abin da manazarta tarihi


za su iya tsokaci a game da shi musamman auratayya a


tsakanin dangin Banu Umayyah da na Banu Hashim za`a


iya tattara littafi akanta. Allah Ya sa mu dace. Amin.


To, a haKiKanin gaskiya malaman shi'ah ba su fitowa fili su yi suka


ga auren wadannan mata da manzon Allah (S.A.W) yayyi, amma su


kan yi suka ga su matan a cikin littafansu. Misali Ni`imatullah al


Jaza`iri a cikin littafin Al Anwar al Nu`maniyyah (1/108) ya yi suka


ga Nana A`ishah da cewa, wai tana adawa da Nana Fatima diyar


Manzon Allah (S.A.W). Haka ma Muhammad BaKir al Majlisi a


cikin littafin Mir`atul UKul (3/305) cewa ya yi ta na adawa da


Allah da ManzonSa da duk Ahlul Baiti. A yayin da shi kuma Abdul


Hussain al Najfi a littafinsa al Gadir (6/79) suka ya yi ga Nana


Hafsah yana mai cewa, wai ba ta san wankan janaba ba !


Subhanallah ! To, wane ne bai koya ma ta ba kenan?!


34


TUSHEN BAYANI:


Dubi tabbacin abin da muka fada na auratayya a


tsakanin Sahabbai da Ahlul Baiti a cikin littafan Sunna


kamar:


1- Siyar A`lam al Nubala` na Dhahabi (6/258-260).


2- Tarikh al Islam na Dhahabi (6/46-47)


Sa`annan ka duba littafan Shi`ah kamar haka:


1- Al Gadir fil kitab wal Sunnah wal Adab na Abdul


Hussain al Najfi (6/79).


2- Al Kafi na Kulini tare da sharhinsa Mir`atul UKul na


Majlisi (3/305).


3- Al Anwar al Nu`maniyyah na Ni`imatullah al Jaza`iri


(1/80).


35


BINCIKE NA UKKU AKAN YABO A TSAKANIN


SU:


Ya kai dan Uwana mai karatu ! Ko ka taba zama a


wasu cikin abokan tafiya a aikin Hajji ko neman karatu ko


tafiyar aiki ko fatauci ? Ya ya ka ji rayuwar baKunci tare


da abokan tafiya?


Ko ka taba samun kanka a cikin wani matsatsi ko


Kunci a gidan kaso ko a sarari? Ya ya ka ga rayuwa tare da


abokai a cikin wahala? Ko ka lura da irin kusanci da


Kaunatayyar da wannan zamantakewa ta ke haifarwa?


To, me za ka ce game da zamantakewar Sahabbai a


Makka lokacin da fadar kalmar La`ilaha Illallahu ya


kasance dalilin shiga wani Kunci da wahala?. Ka tuna


tarayyar Sahabbai (irin su Abubakar SiddiKu da Ali dan


Abu Dalib da Usman dan Affan da Zaidu dan Harisa) a


mabuyarsu ta Darul ArKam a lokacin da ba zai yiwu ma a


bayyana karatun lKur`ani ba. Sa`nnan ka tuna tarayyarsu a


cikin wahalhalu da azaba da Mushrikai su ka rinKa gana


ma su. Sai kuma hijirar da suka yi har sai biyu domin


kubuta da addininsu zuwa Kasar Habasha. Ka tuna yadda


su ka sami kansu a garin baKunci da kewa a lokacin da su


ka je Madina suna masu barin dukiyoyi na gidaje da


36


bisashe da Kaddarori daban daban, kai da ma iyalan wasu


daga cikinsu.


Ka tuna irin zamantakewar Muhajirai da masu


masaukinsu wato Ansar da abin da Allah Ya fada a game


da su na zabin `yan uwansu akan kawunansu ga abin da su


ke so kuma su ke da buKata zuwa ga reshi.


Ka tuna tarayyarsu a tafiye tafiyensu na Jihadi da


Hajji tare da Manzon Allah (S.A.W) a lokacin da a Kafa


ake tafiya da kuma kan raKuma, sa`adda ayari ya ke yin


kwana goma a tsakanin Makka zuwa Madina kawai. A


lokacin da ake tsoron dabbobin dawa ta yadda matafiyi ba


zai yi shishishigin tafiya nesa da ayarinsa ba don gudun


aukuwar hakan. Duba irin yadda su ke yi wa junansu


murna da san barka a lokacin da suka rinjayi Mushrikai a


yaKin Badar da Khaibar da makamantansu da lokacin da


su ke jajanta ma junansu a yayin da Allah Ya jarabce su a


Uhud da Hunain. Ashe duk wadannan ba abubuwa ne da ke


Karfafa danKon Kauna da zumunci ba? Duba yadda


Buwayayyen Sarki Ya ke cewa:


37


Kuma Ku tuna ni`imar Allah a kanku, a lokacin


da kuka kasance maKiya, sai Ya sanya soyayya a


tsakanin zukatanku, saboda haka ku ka wayi gari,


da ni`imarSa, `yan uwan juna.


Suratu Ali Imran Aya ta 103.


Haka shi ke. Ni`imar Allah ce a kansu da Ya fitar da


su daga shirka wadda ta sanya su Kiyayya da gaba da yaKar


junansu, Ya mayar da su ga tafarkin Musulunci suna


Kaunar junansu da tausayin junansu.


Ya kai dan uwana mai karatu ! me zai hana ka yarda


da abin da Allah Ya fada:


Ma'ana:


Sai (Allah) Ya sanya soyayya a tsakanin zukatanku,


saboda haka kuka wayi gari, da ni`imarSa, `yan


uwan juna.


Suratu Ali Imran Aya ta 103.


Ya kai dan uwa ! me zai hana ka kyautata zato ga


wadannan bayi na Allah wadanda Ubangijinsu Ya ke mu su


sheda, Ya ke tunatar da su da falalar da Ya yi a kansu, Ya


na cewa, sun wayi gari su na 'yan uwa, zukatansu na hade,


38


Kauna ta ke a tsakaninsu. Duba yadda Ya ce ma AnnabinSa


a kansu:


Ma`ana:


Kuma idan (Mushrikai) sun yi nufin su yaudare ka,


to, lalle ma`ishinka Shi ne Allah. Shi ne Wanda Ya


Karfafa ka da taimakonSa, kuma (Ya Karfafa ka) da


Mummunai. Kuma Ya sanya soyayya a tsakanin


zukatansu. Da ka ciyar da abin da ya ke a bayan


Kasa, gaba daya, da ba ka sanya soyayya a tsakanin


zukatansu ba, kuma Allah Ya sanya soyayya a


tsakaninsu. Lalle Shi ne Mabuwayi, Mai hikima. Ya


kai annabi! Allah ya ishe ka da kuma wadanda su ka


bi ka daga Muminai.


Suratul Anfal Aya ta 62-64.


Sai ka sake karanta wannan ayar ka gani wace irin


falala ce Allah Ya yi akan ManzonSa ta hanyar Karfafa shi


da Sahabbai, Kuma ya ya Allah Ya sanya Kauna a


tsakaninsu, aikin da duk dukiyar duniyar nan idan an yi


amfani da ita kwalliya ba za ta biya kudin sabulu ba. Har


yanzu dai kana nan kana gaskata gurbatattun ruwayoyin


39


Shi`ah masu nuna Sahabbai a matsayin masu adawa da


gaba?! Ya Allah Ka ba mu basira.


Bari kuma in ba ka wani labari wanda ya fito daga


daya daga cikin littafan da su ne madogarar shi`ah, ina


nufin littafin Kashful Gumma na Arbulli wanda aka buga


shi a Iran (2/78):


An karbo labari daga Imam Ali dan Hussaini


(Zainul Abidin) yace, wasu mutane sun zo daga IraKi


wurin Imam (yana nufin Ja`afar al SadiK) sai suka rinKa


aukawa a cikin mutuncin Abubakar da Umar da Usman


(R.A). To, a lokacin da suka Kare kalamansu sai Imam


yace da su: Ku ba ni labari su wane ne ku? Shin ku ne


Muhajirai na farko da Allah Ya ce:


Ma'ana:


(Ku yi mamaki) ga matalauta masu hijira


wadanda aka fitar daga gidajensu da dukiyoyinsu,


suna neman falala daga Allah da kuma yarda,


kuma suna taimakon Allah da manzonSa!


Wadannan su ne masu gaskiya.


Suratul Hashri, Aya ta 8.


Sai su ka ce, A`a. Ya ce: to, ku ne:


Ma'ana:


Da wadanda suka zaunar da gidajensu (ga


musulunci) kuma (suka zabi) imani, a gabanin


zuwansu, suna son wanda ya yi hijira zuwa gare


su, kuma ba su tunanin wata buKata a cikin


Kirazansu daga abin da aka bai wa muhajirai,


kuma suna fifita wadansu a kan kawunansu, kuma


ko da suna da wata larura. Kuma wanda aka


kiyaye shi daga rowar ransa to, wadannan su ne


marabauta.


Suratul Hashri, Aya ta 9.


Sai su ka ce, A`a. Ya ce: To, ga shi ku kun sheda ba


ku cikin wadannan biyun. Ni kuma na shaida ba ku


cikin na ukkun su ne:


Ma'ana:


Kuma wadanda suka zo bayansu, suna cewa, "Ya


Ubangijinmu! Ka yi gafara a gare mu, kuma ga


'yan uwanmu, wadanda suka riga mu yin imani,


41


kada Ka sanya wani Kulli a cikin zukatanmu ga


wadanda suka yi imani. Ya Ubangijinmu! Lalle


Kai ne Mai tausayi, Mai jinKai.


Suratul Hashri, Aya ta 10.


Sa`annan ya ce da su: Ku fita ku bani wuri. Allah


Yayi mu ku kaza da kaza (ma`ana yayi addu`a maras


kyau akansu).


Ko da yake na sani duk irin wadannan ruwayoyi da su


ka zo daga Ahlul Baiti `yan shi'ah su kan dauke su a


matsayin taKiyya, amma mai hankali yana iya gane cewa,


wannan bawan Allah gaskiya ce ya fada, don haka ba


dalilin tuhumarsa da munafucci akan ya fadi gaskiya. Allah


Ya sa mu dace.


Ga abin da shi kansa sayyiduna Ali ya ke cewa akan


sahabbai:


Lalle, naga sahabban Annabi Muhammadu


(S.A.W) kuma ban taba ganin wanda ya yi kama


da su ba daga cikinku, domin su idan ka gan su da


safe sai ka raina kamarsu alhalin kuwa sun kwana


su na sallah. Su na da alamomi a goshinsu da


kumatunsu (Alamun sallah da kukan tsoron


Allah). Idan dayansu ya tuna alKiyama sai ka gan


42


shi kamar wanda ya taka garwashi (yana zufa).


Idan kuma a ka ambaci Allah sai hawaye ya


dararo ma dayansu har ya jiKe rigarsa, ya rinKa


girgiza irin girgizar ganye idan iska ya kada duk


saboda tsoron azaba da Kaunar lada.


Kalamansa da na `ya`yansa suna da yawa akan yabon


sahabban Annabi (S.A.W). Jikansa Zainul Abidin Ali dan


Husaini ya na da wani littafi wanda ya ke yabonsu a cikinsa


ya na kuma yi mu su addu`a. Haka ma duk wani shugaba


daga cikin mutanen kirki za ka taras ya na yawaita yabo a


gare su musamman ma khalifofi shiryayyu da iyayen


muminai (matayen manzon Allah (S.A.W).1


1 Wani abu mai muhimmanci da ba a cika mayar da hankali gare


shi ba shi ne, ayyukan da sayyiduna Ali (R.A) ya yi a KarKashin


gwamnatocin da su ka gabace shi. Sai kuma yaKoKan da ya yi tare


da su kamar yaKin ridda wanda sayyiduna Abubakar ya yi a kan


Banu Hanifa in da can ne sayyiduna Ali ya samu kuyangar da ta


Haifa ma sa shahararrren dan nan nasa Muhammad wanda a ke ce


ma sa Ibnul Hanafiyyah (a cikin bangaroran shi'ah akwai wadanda


su ke sanya shi cikin Imamai goma sha biyu). Ko ka yarda cewa,


duk cikin bai yarda da sahihancin mulkinsu ba ne ya yi ma su aiki,


kuma ya yi yaKi tare da su har ya halaltar da samun rabo a cikin


bayi ?


43


BINCIKE NA HUDU : MATSAYIN AHLUS


SUNNAH GAME DA AHLUL BAITI :


1. Su wane ne Ahlul Baiti ?


Fassarar Ahlul Baiti ita ce iyalan gida. Iyalan ko wane


gida kuwa su ne wadanda ke cikinsa. Matar mutum ta na


cikin iyalansa, haka ma `ya`yan cikinsa da ya Haifa. Malam


Shari`a su kan ce Ahlul Baiti ne ga Iyalan gidan manzon


Allah (S.AW) . To, amma har wa yau malamai sun yi


zantuttuka mabanbantan juna dangane da su wane ne iyalan


gidansa?.


Kafin mu je zuwa ga maganganun malaman sunna –


ma`abuta gaskiya- ya dace mu yi nuni zuwa ga cewa,


malaman shi`ah sun taKaita iyalan Annabi kawai akan


`yarsa Nana Fatima da mai gidanta Ali da `ya`yansu Hassan


da Husaini, sai kuma cikon imamai goma sha biyu daga


cikin zuri'ar Ali.1 Akwai kuma sabani mai yawan gaske a


tsakaninsu game da wannan mas`ala. Ka duba littafin


FiraKul Shi`ah na Nubakhti.


To, ga ra`ayoyan Ahlus sunna akan wadanda sunan


Ahlul Baiti ya Kunsa :


1 Sauran `ya`yan manzon Allah guda shida da matayensa da har


sauran zuri`ar Ali din kansa kamar Ummu kulsum diyar Fatima


wadda sayyiduna Umar ya aura duk ba su samu shiga a ciki ba


saboda son ran `yan shi`ah.


44


Ra`ayi na daya:


Su ne wadanda Annabi (S.A.W) ya hana su cin sadaka


daga cikin danginsa. Wadannan sun hada da duk zuri`ar


Banu Hashim da Banul Muddalib.


Ra`ayi na biyu:


Su ne `ya`yansa da matansa da kuma zuri`arsa.


Wannan shi ne zancen da Malam Ibnul Arabi ya zaba, kuma


ya kafa hujjoji a kansa.


Ra`ayi na uku:


Su ne dukkan mabiyansa tun daga sahabbai har zuwa


ranar tashin alKiyama. Wannan shi ne zancen da Malam


Nawawi ya Karfafa. Haka ma mawallafin littafin al Insaf.


Wasu kuma da su ka zabi wannan zance cewa su ka yi ana


nufin da Ahlul Baiti ma su taKawa daga cikin muminai.


Amma zance mafi rinjaye (ta wajen hujja) shi ne zance na


farko.


45


2.Matsayin Ahlul Sunna a game da Ahlul Baiti :


Idan ka dauki ko wane littafi daga cikin littafan Ahlul


Sunna wadanda su ke koyar da aKida, to, za ka tarar akwai


wannan mas`ala a ciki saboda muhimmancinta.


Ba zan tsawaita ma mai karatu bayani ba, amma zan


taKaita ne a kan maganar shaihun malamin nan (Ahmad


dan Abdul Halim wanda a ka fi sani da) Ibnu taimiyyah.1


Ga maganar ta sa kamar haka:


3. Me ne ne haKKoKan Ahlul Baiti a kan musulmi ?


Iyalan gidan manzon Allah (S.A.W) su na da matsayi


mai girma wanda ya wajabta ma su haKKoKa a kan


musulmi kamar haka:


HaKKe na daya: Jibintarsu da Kaunarsu. Kamar yadda


dan uwana mai karatu ya sani cewa, son musulmai duka


wajibi ne. Kuma "Muminai maza da mata majibintan juna


ne". To, amma kuma su Ahlul Baiti sun kebanta da wani


matsayi saboda kusancinsu ga Manzon Allah (S.A.W)


1 Maganar wannan malami a nan ta na da muhimmanci Kwarai da


gasket saboda dalillai guda uku:


1- Domin taKaicewarta


2- Domin gamewar ma`anarta


3- Domin malamin ya na cikin wadanda `yan shi`ah su ke ganin


kamar ya fi kowa adawa da su, saboda littafinsa da ya wallafa


Minhajul Sunnatin Nabawiyyah wanda ya ragargaza aKidunsu


a cikinsa da hujjoji mabayyana.


46


kamar yadda mu ka fahimta daga maganar Ibnu taimiyyah


wadda ta gabata. Allah Mabuwayin Sarki Y ace:


Ma`ana:


Ka ce ba ni roKonku wata lada a kansa (kiran da ni


ke yi mu ku) sai dai Kauna a dangina.


Suratul Shura, aya ta 23.


Wannan shi ne ma`anar hadisin da ya gabata wanda ya


ce, "Ba za su yi imani ba har sai sun so ku domin Allah da


kuma kusancina". Domin manzon Allah ya hada zumunta


da dukkan rassan Kuraishawa. Kuma a nan a na nufin


soyayya da jibinta sama da wadda ta tabbata ga sauran


musulmi.


HaKKe na biyu: Yin salati a gare su. Iyalan gidan manzon


Allah (S.A.W) su na shiga a cikin salatin da Allah


Madaukakin Sarki Ya yi umurni a yi wa manzon naSa in da


ya ke cewa:


47


Ma`ana:


Lalle Allah da mala`ikunSa Su na salati ga


annabi. Ya ku wadanda su ka yi imani ! ku yi


salati a gare shi, kuma ku yi sallama domin


amintarwa a gare shi.


Suratul Ahzab, Aya ta 56


Dalilin shigar Ahlul Baiti a cikin wannan salati kuwa


shi ne hadisin da Muslim ya ruwaito a cikin ingantaccen


littafinsa daga Abu Mas`ud al-Ansari (Allah Ya Kara ma sa


yarda) wanda ya ke cewa : Manzon Allah (S.A.W) ya same


ni a wurin zaman Sa`adu dan Ubadah, sai Bishru dan Sa`ad


y ace ma sa : Ya manzon Allah ! Allah Ya umurce mu da


mu yi ma ka salati, to, yaya za mu yi ma ka salatin? Sai


annabi ya yi kawaici har sai da mu ka yi fatar bai tambaya


ba. Sa`annan sai manzon Allah (S.A.W) y ace : "Ku ce : Ya


Allah ! Ka yi tsira ga Muhammadu da iyalan Muhammadu


kamar yadda ka yi tsira ga Ibrahim da iyalan Ibrahim.


Kuma ka yi albarka ga Muhammadu da iyalan Muhammadu


kamar yadda ka yi albarka ga Ibrahim da iyalan Ibrahim a


cikin talikkai. Lalle Kai mai godiya ne, Mai girma". Ya ce :


Sannan ku yi sallama kamar yadda ku ka sani.


(Sahihu Muslim, Hadisi na 405).


48


Daga cikin dalillan da ke bayyana wannan haKKin na


Ahlul Baiti kuma akwai hadisin Abu Humaidin al Sa`idi


wanda Buhari da Muslim su ka ruwaito. Hujjoji dai a kan


wannan batun su na da yawa.


Malam dan Kayyimu ya ce :


Wannan haKKi ne na su ban da sauran al`umma,


ba tare da sabani akan haka ba a tsakanin


Malamai.


(Jala`ul Afham Fil Salati ala khairil anam )


HaKKe na uku: Bayar da humusi gare su kamar yadda


Allah Ya ce:


Ma`ana:


Kuma ku sani, abin sani kawai, abin da ku


ka samu na ganima daga wani abu, to, Allah Ya


na da humusinsa kuma don manzo, kuma saboda


masu zumunta da marayu da miskinai da dan


hanya…


Hadissai kuma a maganar humusi su na da yawa.


Kuma rabon ya kebanci danginsa ne su kadai. Kuma ya


tabbata a gare su bayan rasuwar Manzon Allah (S.A.W).


49


Wannan shi ne zancen jumhurin malammai, kuma shi ne


ingantacce.


(Al Mugni 9/288)


Fa`ida:


HaKKoKan Ahlul Baiti su na da dama. Amma dai


wadannan su ne mafi muhimmanci. Kuma duk wanda


nasabarsa daga manzon Allah (S.A.W) ta tabbata, kuma ya


kasance musulmi, to, wadannan haKKoKan sun tabbata a


gare shi. Amma kuma dole ne a kula da kyawon aiki, domin


nasaba ita kadai ba ta wadatarwa. Manzon Allah (S.A.W)


ya kasance ya na tsoratarwa dangane da dogara a kanta. Ga


kuma abin day a aikata a makka – a cikin labarin day a


shahara- in da manzon Allah (S.A.W) ya tara danginsa ya


ce ma su:


Ya ku jama'ar Kuraishawa ! ku sayi kawunanku


daga wuta, domin ni ba ni wadatar da ku da komai


daga Allah. Ya Abbas dan Abdul Muddalib ! ba


ni wadatar da kai da komai daga Allah. Ya


Safiyyah gwaggon manzon Allah ! ba ni wadatar


da ke da komai daga Allah. Ya Fatima diyar


Muhammadu (S.A.W) ki roKe ni abin da ki ke so


daga dukiyata, ba ni wadatar da ke da komai daga


Allah.



Posts na kwanan nan

SAKO DAGA MUSULMI MAI ...

SAKO DAGA MUSULMI MAI WA'AZI ZUWA GA MUTUM KIRISTOCI

FALALAR AZUMIN KWANA ...

FALALAR AZUMIN KWANA SHIDA SHAWAL

TAKAITACCEN BAYANI MA ...

TAKAITACCEN BAYANI MAI ANFANI GA SABON SHIGA MUSULUNC

ZIKIRAI WADANDA AKE Y ...

ZIKIRAI WADANDA AKE YIN SU DA SAFE DA KUMA YAMMA