Labarai




NI MUSULMI NE


IMANI DA ALLAH


Ni Musulmi ne…….


∙Na yi imani da Allah shi kaxai, ba shi


da abokin tarayya, babu wani ubangiji


bayan shi, bai haifa ba, ba a haife shi


ba, sam ba shi da kwatankwaci.


∙Mahaliccin sammai da qassai, kuma


mamallakinsu, masanin abin da ya


vuya da abin da yake a bayyane, rayayyen


da ba ya mutuwa, tsayayyen da


ba ya barci.


∙Yana da sunaye kyawawa da sifofi


maxaukaka, a cikinsu akwai sunaye


casa'in da tara, wanda ya kiyaye su ya


٦


-6-


NI MUSULMI NE


kuma roqi Allah da su ya shiga


aljanna.


∙A cikinsu akwai sifofin kaxaita Allah,


shi mai girma da xaukaka shi ne "alwaahidu"


al-ahadu" "al-fardu' (ma'ana


shi xaya ne tilo), shi ne ake nufi da


buqata, mamallakin kowa da komai


kuma mai mulki.


∙Da sifofin xaukaka; ka ga shi ne mai


yawan hikima, qwararre, mai shiryatarwa,


kuma shi ne gaskiya, na farko


da na qarshe, na bayyane da na voye,


wanda zai gaje komai kuma wanzajje,


mawadaci kuma mai tsarki, mahalarci


makusanci, mai hukunci mai adalci,


-7-


٧


NI MUSULMI NE


hasken sammai da qassai, ma'abocin


xaukaka da karamci.


∙Da sifofin girma; shi ne mabuwayi mai


xaukaka da girma, mai sa a yi dole,


mai tsananin qarfi, wanda ya rinjayi


kowa, mai iko kuma mai qaddarawa,


mai taimako maxaukakin da babu


irinsa.


∙Da sifofin iko; shi ne masani mai ji


mai gani, rayayye.


٨


-8-


NI MUSULMI NE


mai riqewa mai shimfixawa, mai


dankwafarwa mai xaukakawa, mai


buwayarwa mai qasqantarwa, mai


bayarwa mai hanawa, mai amfanarwa


mai cutarwa, mai rayarwa mai


matarwa, mai qaddamarwa mai


jinkirtarwa.


∙Da sifofin da suke nuna halittunsa; shi


mahalicci ne mai yin abu ba da misali


ba, mai surantawa mai samar da


komai, gwani wajen qirqirar halitta ba


tare da ya ga ta wani ba, mai dawo da


abu mai tashin komai, mai tattara


komai mai yawan baiwa da yawan


buxi, mai yawan azurtawa mai wadatarwa,


wanda ya san qididdigar komai,


shi ne wanda ya mamaye komai, mai


-9-


٩


NI MUSULMI NE


kiyayewa mai lura da komai, mahaliccin


sammai da qassai.


∙Da sifofin rahama; shi ne mai rahama


mai jin qai, mai tausayi mai baiwa, mai


son bayi mai kyautatawa, mai kuma


yawan gafara da afuwa mai amsar


tuba, mai aminci da bayar da kariya


da tsaro, mai tausayi, wanda ake gode


masa, mai karamci da ni'imtarwa, mai


baiwa mai taimako, mai amsar addu'a


mai yalwa mai haquri mai shiryatarwa,


mai yawan haquri mai yawan


tausasawa, majivincin al'amurra, mai


ceto mai taimako, mai karvar tuba.


∙Ya yi wa xan adam ni'imomin da ba


su da iyaka, babu wata ni'ima da bawa


yake ciki face daga Allah shi kaxai


take, shi ne wanda ya halicce shi ya


kuma raya shi, ya kuma sanya masa ji


١٠


-10-


NI MUSULMI NE


da gani, ya karrama shi ya kuma kyautata


masa.


∙Saboda haka ne ya zama wajibi akan


bawa ya kaxaita Allah shi kaxai wajen


bauta –wadda ita ce aikata abin da aka


bayar da umurni da nesantar abin da


aka hana-, domin babu wani da ya


cancanci ibada sai Allah.


∙Haka ma lallai Allah ya san dukkan


halayen da bawa yake ciki, shin na


xa'a ne ko na savo, dole ne bawa ya


cika zuci-yarsa da ganin kwarjinin


Allah mai tsarki da xaukaka, da ganin


girmansa da sonsa, ya kuma ji kunyar


sava masa, ya nesanci haka saboda


Allah yana ganinsa, ya kuma san abin


da yake yi na savo.


∙Ya yi farin ciki da kyawawan ayyukan


-11-


١١


NI MUSULMI NE


da zasu kusanta shi da yardar mahaliccinsa


mai girma da xaukaka, ya kuma


ci gaba da aikata su har ya sami


matsayin "al-ihsan"; saboda imani yana


qaruwa da qaruwar xa'a, yana kuma


raguwa da aikata savo.


∙Ka da ya miqa ragamarsa ga sha'awa


ko son zuciya ko bidi'a, ya miqa ragamarsa


ne kawai ga Allah shi kaxai,


yana mai bin umurnin Annabi (sallallahu


alaihi wa sallam), ka da manufarsa


ta aiki ta zamo neman karikitan


duniya, a maimakon haka ya nemi


ladan Allah ne kawai da su.


∙Haka ma lallai Allah mai rahama ne


ga mutum sama da rahamar da uwa


take yi wa xanta, kuma rahamarsa ta


yalwaci dukkan komai, don haka


wajibi ne a kan bawa ya roqe shi, ya


١٢


-12-


NI MUSULMI NE


kuma qasqantar da kansa a gabansa


wajen neman buqatunsa na duniya da


na lahira, ka da ya roqi kowa.


∙Saboda babu wata fa'ida a roqon wani


ba Allah ba, babu wanda ke mallakan


cikakken iko ban da Allah, babu wanda


yake jin abin da ke faruwa a sirri da


wajen ganawa in ba Allah ba, babu


wanda ke mallakar qaddara wani abu


in ba Allah ba, don haka babu mai


ikon amsa addu'arsa in ba Allah ba.


∙Saboda haka bai halatta ga musulmi


ya roqi qabari ba, ko ya roqi na cikin


qabarin, ko wane ne aka rufe a cikin


qabarin kuwa, saboda ba ya jinsa, ta


ma yaya


zai amsa masa ko ya amfane shi?


Lallai Allah shi kaxai shi ne mai amfa-


13-


١٣


NI MUSULMI NE


narwa, mai kuma cutarwa, saboda


haka bai halatta musulmi ya gina masallaci


akan qabari ba, domin Annabi


(sallallahu alaihi wa sallam) ya hana


yin haka.


∙Saboda haka wajibi ne akan bawa ya


yi duba zuwa ga rauninsa da kuma


qarfin Allah mabuwayin sarki, ya


kuma sake duba talaucinsa da wadatar


Allah maxaukakin sarki, ya kuma


duba jahilcinsa da sanin Allah maxaukakin


sarki, ya kuma yin duba zuwa ga


qasqancinsa da girman Allah maxaukakin


sarki.


∙Ya kuma san cewa lallai girma da


buwaya suna ga Allah ne da manzonsa


da muminai.


∙Domin haka ya wajaba ya zama cikin


١٤


-14-


NI MUSULMI NE


waxannan muminan, waxanda ba sa


dogara da kowa sai Allah, ba sa neman


taimakon kowa sai Allah, ba sa neman


tsari daga kowa sai Allah, ba sa neman


ceton kowa sai Allah, ba sa tsoron


kowa sai Allah, ba sa fatan komai daga


wurin kowa sai Allah, ba sa roqon


kowa sai Allah, ba sa yanka saboda


kowa sai Allah, ba sa bakance saboda


kowa sai Allah, ba sa ranstuwa da


kowa sai Allah, ba sa xaura layu da


tsumburkai, ba sa gasgata bokaye da


masu tsubbu da taurari da matsafa, ba


kuma sa zuwa wajensu.


∙Su ba sa shu'umanci, suna kuma takatsantsan


da kura-kuren harsunansu


kan ka da su ja su zuwa wuta. Ba sa


cewa: "Abin da Allah ya so da abin da


wane ya so" ko "ba domin Allah da kai


-15-


١٥


NI MUSULMI NE


ba" ko "na dogara da Allah da kai",


a'a su ne masu cewa: "Na dogara ga


Allah shi kaxai" ko " abin da Alah ya


so sannan wane ya so"; saboda waxancan


kalmomi suna daidaita tsakanin


Allah da bayinsa, suna kuma cikin


qaramin shirka.


∙Kamar yadda ya wajaba mu yi imani


da Allah, haka ma ya wajaba mu


kafirce wa xagutai.


∙Babban xagutu shi ne shaixan, da


kuma duk wanda aka bauta masa ba


Allah ba da yardarsa.


∙A cikin waxanan xagutan akwai


wanda duk ya sanya wata doka da ta


haramta abin da Allah ya halatta, ko


ta halatta abin da Allah ya haramta.


∙Haka ma xagutu ne duk wanda ya yi


١٦


-16-


NI MUSULMI NE


kira zuwa ga aikata haka, ko ya


umurci mutane da shi, ko ya yi hukunci


da shi, saboda ya qetare iyakar


halitta na ya ji ya kuma bi.


∙Allah shi kaxai shi ne ya halicci


mutane, ya kuma san mene ne zai


gyara su, don haka babu wani wanda


ya isa ya sanya masu doka in ba shi ba.


-17-


١٧


NI MUSULMI NE


(2) IMANI DA MALA'IKU


∙Na yi imani da mala'ikun da Allah ya


halicce su daga haske, ya kuma sanya


musu fukafukai, wasu bibbiyu wasu


uku-uku wasu kuma hurhuxu. Su


kuma ba sa cin abinci, ba sa shan ruwa,


ba sa barci, ba sa kuma auratayya, ya


umurce su da wasu ayyuka suna kuma


aikatawa.


∙Mala'iku dawwama suke yi cikin aikin


xa'a ba sa gajiya, ba sa kuma savon


Allah, suna jin tsoron ubangijinsu da


yake sama da su, a cikinsu akwai


wanda yake sujada tun ranar da Allah


ya halicci sammai da qassai har zuwa


ranar alqiyama, idan kuma ya xaga


kansa sai ya ce: mun ambaci tsarkinka


ya Allah, ba mu bauta maka da bautar


١٨


-18-


NI MUSULMI NE


da ta dace da kai ba.


∙Su bayin Allah ne, ba kuma mata ba


ne, ba kuma mataimakansa ba ne,


suna ceton muminai da izinin Allah a


ranar alqiyama.


∙A cikinsu akwai masu kiyayewa: su ne


waxanda suke bai wa bayi kariya ga


barin abubuwan qi.


∙A cikinsu akwai masu girma kuma


marubuta: su ne waxanda suke rubuta


ayyukan bayi na alhairi da na sharri


(masu kyau da munana)


∙A cikinsu kuma akwai masu tasbihi:


su ne waxanda suke tasbihi dare da


rana ba sa gajiya har zuwa ranar


alqiyama.


∙A cikinsu akwai masu shawagi: su ne


-19-


١٩


NI MUSULMI NE


waxanda suke halartar majalisun


zikiri da na karatun Alqur'ani da


majalisu na ilimi.


∙A cikinsu akwai waxanda suke xaukan


al'arshin mai rahama: su takwas ne, su


manyan halittu ne daga cikin halittun


Allah, tsuntsu zai iya tashi daga gefen


kunnen xaya daga cikinsu ya yi tafiyar


shekaru xari biyar kafin ya isa zuwa


wuyarsa.


∙A cikinsu akwai mala'ikan mutuwa:


shi ne mai amsar rayukan bayi da


izinin Allah, yana da mataimaka.


∙A cikinsu akwai Israfilu: wanda zai


busa qaho dukkan halittu su mutu


kafin tashin alqiyama, sannan ya sake


٢٠


-20-


NI MUSULMI NE


busawa nan take ka gansu a tsaye suna


duban juna suna sauraro.


∙A cikinsu akwai Mika'ilu: shi ne wanda


aka wakkala masa ruwan sama.


∙A cikinsu akwai Ridwan: shi ne mai


tsaron aljanna, yana da mataimaka


waxanda duka suke kai-komo wajen


jin daxi da walwalar muminai a


aljanna.


∙A cikinsu akwai Maliku: shi ne mai


tsaron wuta, yana da mataimaka –


shugabanninsu su goma sha tara neakwai


gudumomin qarfe tare da su,


suna yi ma kafirai azaba da su ne a


cikin wuta,- Allah ya kiyaye mu-.


-21-


٢١


NI MUSULMI NE


∙Babban mala'iku shi ne Jibrilu:


wanda aka wakkala masa wahayi zuwa


ga annbawa da manzanni.


∙Tabbas Annabi (sallallahu alaihi wa


sallam) ya ganshi a sifarsa da Allah ya


halicce shi, ya toshe sasanni saboda


girmansa, yana fukakai xari shida, shi


ne wanda ya kifar da alqaryar Annabi


Luxu da gefen fuffukensa, ya xaga ta


sama ya juya ta ya kuma kifar da ita,


ya sanya samanta ya koma qasa (juyin


waina).


∙Akwai kuma adadi masu yawa


waxanda ba waxannan ba, -babu


wanda ya san iyakan rundunar


ubangijinka in ba shi ba.


٢٢


-22-


NI MUSULMI NE


[ المدثر: ٣١ ] ﴾ μ´ ³ ² ± ° ¯﴿


∙ Mala'iku suna son muminai waxanda


Allah yake sonsu, suna masu addu'a,


suna kuma neman masu gafara.


∙Mala'iku duk da qarfinsu suna zuwa


yaqi tare da muminai.


-23-


٢٣


NI MUSULMI NE


(3) IMANI DA


LITATTAFAI


∙Na yi imani da litattafan Allah


waxanda ya saukar zuwa ga manzanninsa,


kuma lallai duka –a asalin


yadda aka saukar da su- maganar


Allah ne da ya yi masu wahayi domin


su isar da shari'arsa da addininsa,


manyan waxannan litattafai su ne:


∙Alqur'ani mai girma da aka saukar


wa manzonmu Muhammadu (sallallahu


alaihi wa sallam).


∙Injila da aka saukar wa Annabi Isah


(alaihis-salam).


∙At-taura da aka saukar wa Annabi


Musa (alaihis-salam).


∙Zabura da aka saukar wa Annabi


٢٤


-24-


NI MUSULMI NE


Dauda (alaihis-salam).


∙Da kuma shafukan da aka saukar wa


Annabi Ibrahim (alaihis-salam)


∙A cikinsu akwai waxanda aka caccanja


su kafin saukar da Alqur'ani.


∙Kuma lallai Alqur'ani mai girma ya


mamaye dukkan waxannan litattafan,


shi ne alqali akan dokokinsu da


hukunce-hukuncensu, wanda kuma


daga saukansa ya share duk wani


hukunci na su da ya sava masa.


∙Kuma lallai Allah ba zai karvi aiki da


komai ba a ranar alqiyama sai aiki da


Alqur'ani, ba zai karvi aiki da litattafan


da suka gabata ba bayan saukar


Alqur'ani ga Annabi Muhammadu


(sallallahu alaihi wa sallam).


∙Tabbas Alqur'ani magana ne na Allah


-25-


٢٥


NI MUSULMI NE


mai gajiyarwa, yana da tsarki, varna


ba ta zuwa masa ta ko'ina, duk wanda


ya yi magana da shi ya yi gaskiya, duk


wanda ya yi hukunci da shi ya yi


adalci, duk wanda ya yi aiki da shi to


kuwa lallai an shiryatar da shi zuwa ga


kyakkyawar hanya, duk wanda ya yi


riqo da shi ya sami babban rabo kuma


ya tsira, wanda kuma ya juya masa


baya ya tsinci kansa cikin halakakku.


∙Ma'abota Alqur'ani su ne jama'ar


Allah kevavvun Allah, fiyayyen


mutane shi ne wanda ya koyi karanta


Alqur'ani da aiki da shi ya kuma koyar


da shi, domin zai zo ranar alqiyama ya


yi ceto ga waxanda suka karanta shi


suka kuma kiyaye shi sannan suka yi


aiki da shi, yana mai neman aljanna ga


iyalansa.


٢٦


-26-


NI MUSULMI NE


∙Alqur'ani yana tsarkake zukata ga


barin abin da ke gurvata su na


abubuwa masu rikitarwa da


sha'awaice-sha'awaice, yana kuma


kusanta su zuwa ga mahaliccinsu mai


girma da xaukaka, yana kuma


kwaxaitar da su zuwa ga yin aikin da


zasu sami rabo da dawwamammiyar


ni'ima.


∙Cikin ladubban karanta Alqur'ani


akwai:


 Tsarki da alola.


 Fuskantar alqibla.


 Zama cikin ladabi da natsuwa.


 Rashin gaggawa wajen karanta


shi.


 Tsoron Allah da qasqantar da


-27-


٢٧


NI MUSULMI NE


kai.


 Bayyanar da baqin ciki akan


zunubai da wuce gona da iri.


 Kuka saboda tsoron Allah da


ganin girman maganarsa.


 Rashin xaga murya wajen


karanta shi saboda ka da ya


daburta masu sallah.


 Lura da tadabburi wajen karanta


shi.


 Halarto da zuciya.


 Tunani cikin ayoyin Allah.


 Kuma mu tabbatar da cewa


tsayar da hukunce-hukuncen


wannan littafin tsakanin mutane


shi ne babban dalilin samun


xaukaka da nasara akan abokan


٢٨


-28-


NI MUSULMI NE


gaba a bayan qasa.


Ya xan uwa musulmi ka yi gaggawa


zuwa ga ubangijinka, ka riqe wannan


littafi gam, ka yi fatar ka da wani ya


riga ka zuwa wajen Allah, Allah yana


farin ciki da komowarka zuwa gare shi


fiye da farin cikin da iyalai suke yi


idan wanda ba ya nan a cikinsu ya


komo.


-29-


٢٩


NI MUSULMI NE


(4) IMANI DA


MANZANNI.


∙Na yi imani da manzannin Allah, lallai


Allah ya zavi manzanni daga cikin


mutane, ya yi masu wahayin


shari'arsa, ya kuma umurce su da su


isar zuwa ga mutane, kuma duk wanda


ya bi su zai shiga aljanna, wanda kuma


ya sava masu zai shiga wuta.


∙Sannan ya qarfafi gwiwarsu da mu'ujuzozi


waxanda suka bayyanar da


gaskiyarsu, domin su yi amfani da su


ga duk wani wanda ya qaryata su, su


kuma zama hujja ne a gare su.


∙Kuma tabbas farkon manzanni shi ne


Annabi Nuhu (alaihis-salam), cikamakonsu


kuma shi ne Annabi Muhammadu


(sallallahu alaihi wa sallam).


٣٠


-30-


NI MUSULMI NE


∙Kuma mutane ne su, suna cin abinci.


Suna sha, suna kuma auratayya, suna


rashin lafiya, suna mutuwa, kuma su


ne fiyayyun halittun Allah, an katange


su ga barin yin savo.


∙Manzannin Allah suna da yawa, a


cikinsu akwai waxanda Allah ya


ambace su a cikin Alqur'ani, waxanda


su ne: Annabi Muhammadu (sallallahu


alaihi wa sallam) da Ibrahim Khalilurrahman


da Musa Kalimul-lah da Isah


Kalmar Allah da Nuhu (alaihimussalam)


waxanda su ne "ulul-azmi"


daga cikin manzani (tsira da aminci su


tabbata a gare su). Akwai kuma


Isma'il da Ishaq da Ya'akub da


Haruna da Ayuba da Yunusa da


Sulaiman da Dauda da Yahya da


Zakariyya da Hudu da Salihu da


-31-


٣١


NI MUSULMI NE


Yusuf da Shu'aibu da Ilyasu da Luxu


da Zulkifli da Idris da sauransu masu


yawa, a cikinsu akwai waxanda Allah


ya bayar da labarinsu a cikin


Alqur'ani, akwai kuma waxanda bai


bayar da labaransu ba.


∙Farkon abin da manzanni suka yi kira


akai shi ne kaxaita Allah, kuma mafi


girman abin da suka hana shi ne haxa


Allah da wani a wajen bauta, dukkansu


sun zo da musulunci ne da kira


zuwa ga kaxaita Allah, duk kuwa da


cewa shari'o'insu da hanyoyin yin


bautarsu ga Allah mai girma da


xaukaka ya xan canja saboda canjin


zamunnansu da garuruwansu.


∙Kuma lallai manzanni sun yi bishara


da zuwan Annabi Muhammadu


(sallallahu alaihi wa sallam), sun kuma


٣٢


-32-


NI MUSULMI NE


umurci mabiyansu da su yi imani da


shi (sallallahu alaihi wa sallam) idan


an aiko shi suna nan.


∙Bambancin dake tsakanin manzo da


annabi shi ne: shi manzo an aiko shi ne


da sabuwar shari'a, an kuma umurce


shi da ya isar da ita zuwa ga mutane.


Shi kuwa annabi an aiko shi ne domin


ya tabbatar da shari'ar manzannin da


suka gabace shi.


∙Na yi imani da cewa fiyayyen


manzanni a wurin Allah shi ne Muhammadu


(sallallahu alaihi wa sallam),


shi xin xaya ne daga cikin 'ya'yan


Isma'il xan Ibrahim (alaihimas-salam),


Allah ya aiko shi zuwa ga mutane baki


xaya, da annabcinsa Allah ya cika


annabta, da manzancinsa ne kuma


Allah ya cika saqwanni.


-33-


٣٣


NI MUSULMI NE


∙Ya qarfafe shi da mu'ujuzozi, ya


kuma fifita shi akan dukkan manzanninsa


kamar yadda ya fifita saqonsa


akan dukkan saqwanni, ya kuma


xaukaka shari'arsa akan dukka


shari'o'i, littafinsa ma –Alqur'ani- ya


fifita shi akan dukkan litattafai, al'ummarsa


ma –musulmai- ya fifita su akan


saura al'ummatai.


∙Ubangijinsa ya ba shi abin da bai


baiwa wani annabi kafinsa ba, a cikin


abubuwan da ya ba shi akwai:


1) Alwasilat: ita ce babban matsayi


a cikin aljanna, Allah ya tanadi


wannan matsayi ne domin


Annabi (sallallahu alaihi wa


sallam)


2) Alkausar: wani kogi ne a cikin


٣٤


-34-


NI MUSULMI NE


aljanna, yana gudana ne ta


qarqashin al'arshi.


3) Alhaudhu: shi ne tafkin ruwan da


babu wanda zai sha shi a ranar


alqiya sai musulmi.


ranar da mutane zasu sha matsanancin


qishin ruwa, gumi ya mamaye


jikkunansu tun daga gwiwowinsu har


zuwa cikkunansu da kafaxunsu, kowa


gwargwadon abin da ya aikata,


musulmai zasu sha wannan ruwan ne


da kofunan da Annabi (sallallahu


alaihi wa sallam) zai ba su da hannayensa


masu girma da albarka, bayan


haka ba zasu qara jin qishirwa ba har


abada.


4) Ceto: wannan shi ne matsayin da


ake cewa da shi "maqamul-


35-


٣٥


NI MUSULMI NE


mahmud" a ranar alqiyama;


lallai manzon Allah (sallallahu


alaihi wa sallam) zai yi ceto a


wurin Allah, har ya fitar da


musulmai masu laifi daga wuta,


ta yadda babu wani da yake faxin


"La'ilaha illallahu Muhammad


ur-rasulullahi" da zai yi saura a


cikinta, mai savo ba zai dawwama


cikin wuta ba, za a fitar da shi


bayan an tsarkake shi daga


savonsa.


∙Duk wanda ya yi imani da dukkan


annabawa amma bai yi imani da


Annabi Muhammadu (sallallahu alaihi


wa sallam) ba, to kuwa lallai ba zai


tava fita daga wuta ba.


5) Kuma lallai Allah ya taimake shi,


ya kuma taimaki rundunarsa da


٣٦


-36-


NI MUSULMI NE


mabiyansa har zuwa ranar


alqiyama, ta hanyar saka tsoro da


razana a zukatan maqiyansu na


tsawon tafiyar wata, ba a kuma


bayar da haka ga wani annabi


kafinsa ba (sallallahu alaihi wa


sallam).


6) An sanya qasa a gare shi da


sauran musulmai ta zamo wajen


sujada, kuma mai tsarki, wannan


ma ba a bai wa annabawan da


suka gabace shi ba.


7) Allah ya aike shi zuwa ga mutane


da aljannu baki xaya, sa'ilin da


ya aiki kowane Annabi zuwa ga


jama'arsa kaxai.


8) Kuma lallai shi ne farkon wanda


qabarinsa zai tsage ya fito, farkon


-37-


٣٧


NI MUSULMI NE


mai ceto, kuma farkon wanda zai


qwanqwasa qofar aljanna, sai


Ridwan –mai tsaron


aljanna- ya ce: wane ne? sai ya ce:


Muhammadu ne, sai Ridwan ya ce: kai


kaxai aka umurce ni da na buve wa, ka


da kuma in buxe wa wani kafinka.


A cikin mu'ujuzozinsa (sallallahu


alaihi wa sallam) akwai:


 Tsagewar wata.


 Ya mayar wa Qatadatu idonsa da


aka cire masa a ranar Uhdu,


wannan idon kuma ya zamo ya fi


lafiya akan xayan.


 Ya mayar da maqyangyamar


Ibnul-Hakam lokacin da aka


karya ta a ranar Badar.


٣٨


-38-


NI MUSULMI NE


 Ya nemi bishiya da ta yi shaida,


kuma ta shaida da "shahadataini"


har sau uku a gaban wani


kafiri, ya kuma musulunta.


 Kukan kututturen bishiya wanda


manzon Allah (sallallahu alaihi


wa sallam) yake huxuba a kansa


lokacin da ya bar shi, bai kuma yi


shiru ba sai da (sallallahu alaihi


wa sallam)ya xaura hannayensa a


kanshi.


 Haka ma yawaitar abinci a


hannunsa (sallallahu alaihi wa


sallam) har mutane sama da


tamanin suka ci gwargwadon


tafuka biyu na abinci suka kuma


qoshi.


 Haka ma yawaitan ruwa a ranar


-39-


٣٩


NI MUSULMI NE


Hudaibiyya, lokacin da ruwa ya


qare wa runduna ba su da sama


da kimanin kofi xaya, sai Annabi


(sallallahu alaihi wa sallam) ya


sanya hannunsa, nan take sai


ruwa ya ci gaba da vuvvugowa


daga yatsunsa masu albarka


(sallallahu alaihi wa sallam),


mutane suka sha suka kuma yi


alola, kuma adadinsu ya kai


kimanin mutum dubu xaya da


xari huxu.


 Haka ma an yi tafiya da shi zuwa


"Masjidu- al-aqsa", sannan an yi


"Mi'iraji" da shi zuwa maxaukakan


sammai har zuwa magaryar


tuqewa.


 A cikin mu'ujuzozinsa (sallallahu


alaihi wa sallam) akwai labarai


٤٠


-40-


NI MUSULMI NE


na al'ummatan da suka gabata da


na annabawansu,


tabbas shi "ummiyyi' ne, ba ya karatu


balle rubutu. Haka ma bayar da


labarin abin da zai faru nan gaba na


buxe Parisa da Rum, da kuma kekketa


mulkin Kisra da ya keta saqon manzon


Allah (sallallahu alaihi wa sallam), da


ma wasunsu na mu'ujuzozi masu


yawa.


 Mafi girman mu'ujuzarsa shi ne


Alqur'ani mai girma, shi ne kuma


dawwamammen mu'ujiza har zuwa


ranar sakamako.


 Sannan Allah ya xaukaka ambatonsa


(sallallahu alaihi wa sallam)


ta yadda mai girma da xaukaka


ya gwama sunansa da sunansa, ya


-41-


٤١


NI MUSULMI NE


kuma sa kalmar shahada


"La'ilaha illallahu Muhammad


ur-rasulullah" ta zamo farkon


abin da bawa zai shiga musulunci


da ita, kuma qarshen abin da ya


kamata bawa ya bar duniya da


ita, duk wanda maganarsa ta


qarshe ta zama "La'ilaha


illallahu" to kuwa ya shiga aljanna.


 Game da Annabinmu (sallallahu


alaihi wa sallam) ya zama


wajibinmu ne ka da mu gabatar


da maganar kowa a cikin halittu


akan maganarsa, ko ra'ayin


kowane mai bi akan umurninsa,


idan wasu mutane sun riga ka yin


hijira zuwa gare shi (sallallahu


alaihi wa sallam), to kai ma ka yi


hijira zuwa ga sunnarsa a cikin


٤٢


-42-


NI MUSULMI NE


dukkan al'amurranka, ka da ka


bi kowa in ba shi ba.


Mu haxa kai gaba xaya akan


umurninsa, mu yi masa biyayya


.[ ﴿! " # $ % &' ﴾ [النساء: ٨٠


(sallallahu alaihi wa sallam), saboda


duk wanda ya yi wa manzo biyayya to


kuwa lallai ya bi Allah.


 Ka da mu kira shi ba da manzon


Allah (sallallahu alaihi wa sallam)


ba, ka da mu ce da shi


"Muhammadu" kawai.


 Mu ladabtu da ladubbansa, mu yi


koyi da shi a dukkan halayensa


(sallallahu alaihi wa sallam) a


wurin barcinsa ne ko warin cin


abincinsa da tafiyarsa da sallarsa


da azuminsa da sadakarsa da


-43-


٤٣


NI MUSULMI NE


jahadinsa (sallallahu alaihi wa


sallam).


 Mu so shi fiye da yadda muke son


kanmu da 'ya'yanmu da iyayenmu


da ma mutane baki xaya.


∙Kuma dole ne mu so duk wanda yake


son manzon Allah (sallallahu alaihi wa


sallam), yake kuma koyi da shi. Mu


kuma qi mai qin manzon Allah


(sallallahu alaihi wa sallam), yake


kuma qin lizimtar shari'arsa.


∙Ya zama wajibi akan musulmi ya so


muminai, ya kuma taimake su, ya yi


kama da su, ya kuma damu da


al'amurransu, ya taimake su wajen


aikin alhairi, ya riqe su a matsayin


abokai.


∙Wajibi ne a gare shi ya qi kafirai da


٤٤


-44-


NI MUSULMI NE


kafircinsu, ka da ya yi masu biyayya,


ka da ya haxa kai da su wajen cin


mutuncin musulmai, ka da ya taimake


su akan varnarsu, ka da ya yi tarayya


da su a bukukuwansu, kuma haramun


ne ya zalunce su, dole ne ya yi masu


adalci.


∙Wajibi ne mu so iyayen muminai,


matan Annabi (sallallahu alaihi wa


sallam), mu kuma so sahabbansa


(sallallahu alaihi wa sallam); saboda su


ne fiyayyun mutane bayan annabawa.


∙Haka ma ya wajaba mu rayar da


sunnarsa (sallallahu alaihi wa sallam),


mu kuma bayyanar da shari'arsa, mu


kuma isar da kiransa zuwa ga mutane


baki xaya, sannan mu yi haquri akan


abin da zamu gamu da shi na cutarwa


game da hakan, hakan dole ne.


-45-


٤٥


NI MUSULMI NE


∙Saboda lallai sunnar Allah za ta ci


gaba da gudana akan halittunsa,


saboda babu wani annabi daga cikin


annabawa ko waliyyi da ya yi kira


zuwa gaskiya face an qi shi kuma an


cutar da shi.


∙ya kai musulmi, ka faxaka, ka da ka


yarda cutarwar da kafirai suke maka


ta kawar da kai ga barin addininka,


domin an cutar da manzon Allah


(sallallahu alaihi wa sallam) lokacin da


yake cikin sahabbansa marasa yawa,


an kuma cutar da sahabbansa sun yi


haquri.


∙Ka da wai danganta ka da rashin


hankali da rashin tunani da ci baya su


sa himmarka ta yi rauni, ko su ce: an


٤٦


-46-


NI MUSULMI NE


yi maka wankin qwaqwalwa. Kyakkyawar


koyi da manzon Allah ya wajaba


a gare ka, domin dai tabbas wasu sun


ce da shi: mawaqi wasu kuma sun ce:


mahaukaci.


∙Ka da ka damu idan an ce maka: mai


tsattsaurar ra'ayi ko vatacce. Wannan


shi ne halin kafirai tare da muminai:


.[ المطففين: ٣٢ ] ﴾Ü Û Ú Ù Ø ×﴿


(idan sun gansu sai su ce: lallai


waxannan tabbas vatattu ne) [32,


mutaffifina]


∙Shin bai ishe ka ba idan aka ce


mutane sun kasu kashi biyu kai ka


zamanto a cikin kashin da Annabi


(sallallahu alaihi wa sallam) yake?!


-47-


٤٧


NI MUSULMI NE


o n m l k j i h< ﴿∙


.[ الفرقان: ٢٧ ] ﴾ q p


Ka qyale su har zuwa ranar da


azzalumi zai ciji yatsarsa yana mai


cewa: kaico na, ina ma na bi hanya


tare da manzon Allah.


∙Ka da ka ruxe idan sun ce maka xan


ta'adda, ko asharari, wannan qarerayi


ne na azzalumai a kan muminai duniya


da lahira, domin lokacin da mika'ilu


suka kora su akan fuskokinsu zuwa


jahannama, suka yi ta duba cikin suka


ce:


.[ ﴿! " # $ % & ' ) ( *﴾ [ ص: ٦٢


mene ne ya sa ba mu ganin mutanen


da muka qirga su cikin ashararai?


٤٨


-48-


NI MUSULMI NE


∙A nan ne muminai zasu kira su


(waxanda suka kira su da ashararai)


daga babban matsayi a cikin Firdausi,


su ce:


.[ ﴿& ' ) ( * + ,﴾ [الأعراف: ٤٤


(Lallai kan mu mun sami abin da


ubangijinmu ya yi mana alqawari


gaskiya ne) [44, al-a'arafi]


-49-


٤٩


NI MUSULMI NE


(5) IMANI DA RANAR


LAHIRA


∙Na yi imani da ranar lahira, ita ce


ranar da duniya za ta qare (gidan


aiki), ranar lahira kuma ta fara (gidan


sakamako), masu biyayya a saka masu


da aljanna, masu savo kuma a saka


masu da wuta.


∙A ranar alqiyama ne ake sanya


mizani, a kuma baiwa kowane bawa


littafinsa, duk wanda ya amshi


littafinsa da hannun damansa to kuwa


lallai yana tare da Annabi (sallallahu


alaihi wa sallam) a aljanna, wanda


kuma duk ya amshi littafinsa da


hannun hagunsa to kuwa lallai yana


tare da Fir'auna (Allah ya la'ace shi) a


cikin wuta.


٥٠


-50-


NI MUSULMI NE


∙Ana kafa siraxi, duk wanda ya qetare


shi ya shiga aljanna, wanda kuma


tsininsa ya fizgo shi saboda mugun


aikinsa zai faxa wuta.


∙Ranar alqiyama tana da alamu


manya da qanana.


∙A cikin qananan alamun akwai:


tozarta amana da yawan kashe-kashe,


ka ga fasiqai sun xauki jan ragamar


al'umma da qarfi, sannan wawaye su


riqa magana akan al'amurran


al'umma masu muhimmanci.


∙A cikin manyan alamun akwai:


bayyanar Mahdi da tsayuwan Halifanci


na gaskiya akan tsari irin na


Annabi kafin tashin alqiyama da


fitowar Dujal.


∙Da saukowar Annabi Isah (alaihis-


51-


٥١


NI MUSULMI NE


salam) domin ya jagoranci musulmai


ya kuma yaqi kafirai,


ya kuma karya kuros, ya kashe alade,


ba zai yarda da komai ba sai


musulunci.


∙Babu wani gida -a birni ko a qauyeda


zai saura face Allah ya shigar da


wanan addinin ko dai girman mai


girma ko da qasqancin qasqantacce.


∙Da fitowar Yajuju da Majuju, haka


ma fitowar dabbar da za ta yi magana


da mutane, da hudowar rana daga


mafaxarta da xauke Alqur'ani da


makamantan haka.


∙Duk wanda ya aikata wani aiki na


alhairi ko sharri ko da gwargwadon


qwayar zarra ne zai gani a ranar


alqiyama a cikin littafinsa.


٥٢


-52-


NI MUSULMI NE


∙Ku yi gaggawa zuwa ga aikata


ayyukan xa'a tun lokacin rubuta su bai


qare da mutuwar bawa ba, a kuma


lokacin da babu wanda ya sani sai


Allah.


∙Iyalinsa su yi masa wanka, su kuma


yi masa likkafani, su yi masa sallah su


binne shi, mala'iku biyu su zo masa


"Munkar" da "Nakir" su zaunar da


shi su tambaye shi: wane ne ubangijinka?


Mene ne addininka? Wane ne


annabinka?


∙Idan ya amsa da cewa: Allah shi ne


ubangijina, kuma Musulunci shi ne


addinina, Muhammadu (sallallahu


alaihi wa sallam) shi ne annabina


kuma manzona – Allah ya katartar da


shi zuwa ga haka- za a buxe masa taga


cikin qabarinsa har ya zuwa aljanna,


-53-


٥٣


NI MUSULMI NE


ya hango mazauninsa a can, da


benensa da mulkinsa, ya kama farin


ciki, a kuma yalwata masa qabarinsa


iya ganinsa.


∙Idan kuma yana cikin kafirai ne, to


ba zai iya amsawa da komai ba, amsa a


wannan lokacin ba wai wayau da


kaifin qwaqwalwa ke kawo ta ba.


Sai dai Allah yana tabbatar da


ma'abota imani a wannan lokaci;


saboda abubuwan da suka gabatar na


kyawawan ayyuka da kaxaita Allah, da


bayar da farillai da jahadi da biyayya


da umurni da aikin alhairi da hana


munanan ayyuka da sadaka da


karatun Alqur'ani da azumi a lokacin


garji da tsayuwar darare masu tsawo


da sanyi.


٥٤


-54-


NI MUSULMI NE


∙Amma idan ya zamo kafiri ne shi, to


lallai qabarinsa zai quntata har kafaxunsa


su shige cikin jikinsa, qabarin na


sa ya zamo rami ne daga cikin ramukan


wuta saboda mum-munar aikinsa.


∙Ya xan uwa musulmi, ka yi qoqari,


yanzu lokaci ne na aiki ba hisabi, gobe


kuma ranar hisabi ne babu aiki.


∙A wannan rana ce musulmai masu


biyayya -su kaxai- zasu shiga aljanna,


saboda Allah ba zai karvi komai ba a


ranar alqiyama sai musulunci.


∙A cikin aljanna akwai ni'imar da


kunne bai tava ji ba, ido bai tava gani


ba, kuma ba ta tava xarsanuwa a cikin


zuciyar wani mutum ba. Kuma


ni'imarta za ta dawwama har abada ba


yankewa, mutanen cikinta ba zasu


-55-


٥٥


NI MUSULMI NE


mutu ba, mafi girmar ni'ima ita ce


duba zuwa ga zatin Ubangijin talikai.


∙Masu savo da fajirai da kafirai zasu


shiga wuta, a cikin wuta akwai azaba


mai tsanani, wadda Allah ya tanadar


wa kafirai, manyan duwatsu kafaffu


ma ba zasu iya jurewa ba, a can ne za a


yi ta azabtar da su babu qaqqautawa.


∙A can ne mabiya xagutai zasu yi


addu'ar a ruvanya azaba


ga shugabannin da suka vatar da su,


sai Allah ya bayar da umurnin a


ruvanya azaba a gare su baki xaya.


∙Ya xan uwana musulmi ka dawwama


akan gaskiya, ka da yawan waxanda


suka sava ya ruxe ka, saboda idan har


ka bi mafi yawan waxanda suke a


bayan qasa zasu vatar da kai ga barin


٥٦


-56-


NI MUSULMI NE


hanyar Allah, kai dai ka ci gaba ta


tafiya tare da masu zuwa wajen Allah.


∙Domin dai tabbas samun wasu


jama'a masu riqo da gaskiya a cikin


al'ummar Annabi Muhammadu


(sallallahu alaihi wa sallam) abu ne


wanda ba zai gushe ba, wanda ya sava


masu ko ya bayar da su ba zai rage su


da komai ba har zuwa tashin alqiyama.


∙Shin ina dubara ta riskar waxannan


darajoji da tsira, da kuma nesantar


waxancan azabu? Ina dubara ta cin


ma waxancan magabata makusanta da


kuma nesantar waxancan masu juya


baya kuma halakakku? Lallai babu


wata hanya sai tuba ta gaskiya da za ta


gyara abin da ya wuce, da kuma aiki


na gari da zai gyara abin da ya yi


saura na rayuwa, da kuma kyakk-


57-


٥٧


NI MUSULMI NE


yawar xammara wajen tsayawa daidai


akan hanya babu karkata.


∙Ka zamo kana tare da mutane da


jikinka, ka siya ka siyar ka yi aure, ka


raya duniya da abin da Allah ya


halatta maka.


∙Ka da ka xamfara komai na duniya


da zuciyarka, ka tafi da zuciyarka


zuwa in da ya kamata ta kasance, can


qarqashin al'arshin mai rahama, ka yi


sujada da zuciyarka, sujadar da babu


xagowa har zuwa ranar tashin


alqiyama.


٥٨


-58-


NI MUSULMI NE


(6) IMANI DA QADDARA


∙Shi ne mu yi imani da cewa lallai


Allah ya san duk abin da yake a cikin


wannan duniya, haka ma duk abin da


ya kasance da wanda zai kasance a


gaba har zuwa ranar alqiyama, kai


daidai da sanin halin qwayar zarra bai


kuvuce masa ba.


Kuma lallai tabbas ya san ayyukan


bayi da arzikinsu da lokutan ajalinsu,


kuma su wane ne 'yan aljanna a


cikinsu, su kuma wane ne 'yan wuta


tun kafin ya halicce su.


∙Kuma lallai Allah ya rubuta waxannan


qaddarorin a cikin "Lauhulmahfuz"


tun kafin ya halicci sammai


da qassai da shekaru dubu hamsin,


kuma wannan "Lauhul-mahfuz" xin


-59-


٥٩


NI MUSULMI NE


babu wanda ke leqa shi, shin shi


mala'ika ne makusanci ko kuwa


annabi mursali.


∙Kai har jinjiri a cikin mahaifiyarsa


Allah zai umurci mala'iku da su


rubuta shi a matsayin namiji ko


tamace, su kuma rubuta arzikinsa da


aikinsa da ajalinsa da makomarsa


(zuwa aljanna ko wuta), su kuma


rubuta abubuwan da zasu faru da shi


na alhairi ko na sharri.


∙Sannan a daren "Lailatul-qadri"


abubuwan da aka qaddara zasu faru a


shekara su sauka daga "Lauhulmahfuz",


na ajalin mutane ne da


arzikinsu da wanda zai yi aikin hajji a


cikin wannan shekarar da dai makamantan


haka, a dai qaddara duk abin da


zai faru a cikinta a wannan daren.


٦٠


-60-


NI MUSULMI NE


∙Sannan abubuwan da aka qaddara su


faru kullum a lokutansu a kuma kan


abubuwan da aka qaddara masu haka,


Allah ya xaukaka wasu mutane, ya


kuma qasqantar da wasu.


∙Mun yi imani da cewa duk abin da


Allah ya so shi ne zai faru, abin da ya


so ya faru, abin da bai


so ba ba zai faru ba, babu wanda ya isa


ya rinjayi Allah, kuma lallai shi ne ke


juya zukata, yana shiryatar da wanda


yake so da falalarsa da rahamarsa, ya


kuma vatar da wanda ya so da


adalcinsa da hikimarsa, shi xin ya san


wanda ya cancanci shiriya kamar


yadda ya san wanda ya cancanci vata.


∙Shi Allah ba a tambayarsa akan


abubuwan da yake aikatawa, mutane


-61-


٦١


NI MUSULMI NE


ne kawai ake tambayarsu.


∙Kuma lallai mun yi imanin cewa


Allah shi ne ya halicci dukkan komai,


babu daidai da qwayar zarra a


wannan duniya face Allah shi ne ya


halicce ta, ya kuma halicci motsinta da


shirunta.


∙Kuma lallai ya halicci bayi da ayyukansu,


shi kuma ya halicci iko da qudura


ga bayi domin su zavi ayyukansu


da kansu.


∙Kuma lallai Allah maxaukakin sarki


ya umurci halittunsa su yi masa biyayya,


ya kuma yi masu alqawarin aljannarsa,


ya kuma hana su aikata savo, ya


kuma yi wa masu savo gargaxi da


wutarsa, bai wajabta masu wani aiki


ba sai abin da zasu iya, daga nan sai


٦٢


-62-


NI MUSULMI NE


suka kasu kashi biyu: Muminai da


Kafirai, su suka so haka suka kuma


zava, duk hakan Allah ne ya halitta


masu ikon yin hakan a cikinsu.


∙Kuma lallai lada da azaba suna zuwa


ne gwargwadon yadda mutum yake


wajen bin shari'a, ba wai akan sanin


da ya yi masu tun asali ba, duk wani


wanda ya yi aiki ko da gwargwadon


qwayar zarra ne na alhairi zai sami


lada, haka ma wanda ya yi wani aiki


ko da gwargwadon qwayar zarra ne na


sharri za a yi masa uquba akan haka.


∙Kuma lallai abin lura shi ne qarshen


ayyuka, kuma kowane bawa an sawwaqe


masa abin da aka


halitta dominsa na jin daxi a aljanna


ko shan wahala a cikin wuta.


-63-


٦٣


NI MUSULMI NE


∙Saboda haka ne ya zama dole bawa


ya ji tsoron mummunar makoma, ya


dage wajen roqon Allah, yana mai


nuna talaucinsa zuwa gare shi kan ya


shiryatar da shi zuwa ga hanya madaidaiciya,


ya kuma dawwama wajen


neman taimakonsa a kan yin masa


xa'a, ya kuma ci gaba da neman tsarin


kar ya sava masa; saboda bawa ba shi


da wani iko akan duka waxannan


halaye in ba da qaddarawar Allah ba.


∙Kuma tabbas muminai sun yarda da


qaddarar Allah da ikonsa na alhairi da


sharri a cikin abubuwa masu xaci da


masu daxi, kuma suna da yaqinin cewa


babu wani da ya isa ya amfane su sai


idan Allah ne ya qaddara, kamar


yadda babu wanda zai cutar da su sai


da abin da Allah ya rubuta.


٦٤


-64-


NI MUSULMI NE


∙Babu yadda za a yi bawa ya sami


garxin imani sai idan ya san cewa: duk


abin da ya same shi dama ba zai tava


kuskure masa ba, abin da kuma ya


kuskure masa ba zai tava samunsa ba.


∙A qarshe: ina gode wa Allah, ina


kuma roqonsa kan ya shigar da ni


aljanna, ni da sauran musulmai, ya


kuma kare ni ga barin wuta, ni da


sauran musulmai, amin.


ALLAH KA YI SALATI GA ANNABI


MUHAMMADU DA ALAYENSA DA


SAHABBANSA KA KUMA YI TSIRA A GARE SU.


QARSHEN ADDU'ARMU SHI NE: (GODIYA TA


TABBATA GA ALLAH UBANGIJIN TALIKAI).



Posts na kwanan nan

SAKO DAGA MUSULMI MAI ...

SAKO DAGA MUSULMI MAI WA'AZI ZUWA GA MUTUM KIRISTOCI

FALALAR AZUMIN KWANA ...

FALALAR AZUMIN KWANA SHIDA SHAWAL

TAKAITACCEN BAYANI MA ...

TAKAITACCEN BAYANI MAI ANFANI GA SABON SHIGA MUSULUNC

ZIKIRAI WADANDA AKE Y ...

ZIKIRAI WADANDA AKE YIN SU DA SAFE DA KUMA YAMMA