Labarai

FALALAR GOMAN FARKO NA


 ZUL-HIJJA


 Hausa





 FALALAR GOMAN FARKO NA


ZUL-HIJJA





FALALAR GOMAN FARKO NA ZULHIJJA


GABATARWA


Godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai,


tsira da aminci su tabbata ga wanda aka aiko shi


rahama ga talikai, da alayensa da sahabbansa da


wanda ya bi sunnarsa, ya kuma yi koyi da


shiriyarsa har zuwa ranar sakamako. Bayan


haka:


Wannan wani taƙaitaccen saƙo ne, wanda ya


ƙunshi mafi muhimmancin abinda musulmi yake


buƙata a falalar goman farko na Zul-Hijja, mun


tattarashi dan masu ziyartar Harami biyu masu


daraja; domin su kasance cikin sani da fahimta


akan al'amuran addininsu, muna roƙon Allah


Mai karamci da Ya anfanar da shi, Ya sanya shi


mai kyau, kuma saboda Allah ne kaɗai; lallai Shi


ne Mafi alherin wanda ake roƙo, kuma Mafi


karamcin wanda ake fata.


Kwamitin ilimi na Kungiyar hidimtawa


Musulunci da yaruka daban daban.


FALALAR GOMAN ZUL-HIJJAH


Kwanaki goman Zul-Hijjah, falalarsu babba ce,


Allah - Maɗaukakin sarki - Ya bayyanashi a cikin


LittafinSa, kuma ManzonSa Muhammad - tsira da


amincin Allah su tabbata a gare shi - ya


bayyanashi a cikin Sunnarsa, su ne kwanakan da


2


Allah - Maɗaukakin sarki - Ya rantse da su a cikin


LittafinSa da faɗinSa:





 {Inã rantsuwa da alfijiri(1) Da darũruwa


gõma(2) } [al-Fajr: 1-2].


﴿


 Su ne goman Zul-Hijjah kamar yadda Ibn Abbas,


da Ibn Zubair, da Mujahid, da Ibn Kathir, da Ibn


al-Qayyim, da wasu daga cikin salaf da khalaf


suka faɗa1 .


Su ne kwanakan da aiki a cikinsu yafi alheri fiye


da jihadi domin Allah - Maɗaukakin sarki -;


saboda hadisin Ibn Abbas - Allah Ya yarda da su -, ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su


tabbata a gare shi - ya ce: "Babu wasu


kwanakan da aiki na ƙwarai a cikinsu ya fi


soyuwa a wurin Allah sama da waɗannan


kwanakin goma", Suka ce: Ya Ma’aikin Allah,


har jihadi domin ɗaukaka addinin Allah? Sai


Manzon Allah - tsira da amincin Allah su


tabbata a gare shi - ya ce: "Har Jihadi domin


ɗaukaka addinin Allah, sai dai mutumin da ya


fita da kansa da dukiyarsa, kuma bai dawo da


.


komai ba"2


 1Tafsirin Ibnu Kathir (4/106), da Zad al-Ma'ad (1/56).


2Bukhari ne ya ruwaito shi, da Tirmizi kuma lafazin nasa ne.


3


FALALAR AYYUKA A CIKIN KWANUKA


GOMA NA ZUL-HIJJA:


1- Aikin Hajji da Umara, suna daga mafifitan


ayyuka a cikin wannan goman; saboda faɗin


Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare


shi -: «Wanda duk ya ziyarci wannan ɗaki, bai


yi kwarkwasa ba, kuma baiyi fasiƙanci ba; zai


dawo kamar ranar da mahaifiyarsa ta


haifeshi». A cikin wani lafazin na Muslim:


«Wanda duk ya ziyarci wannan ɗakin, bai yi


kwarkwasa ba, kuma bai fasiƙanci ba; zai


dawo kamar ranar da mahaifiyarsa ta


haifeshi»1


 . Saboda faɗinsa: (Duk wanda ya zo


wannan ɗãki) yana ɗauke da ma'anar aikin Hajji


da Umara kuma godiya ta tabbata ga Allah.


Wanda yabo da aminci suka tabbata a gareshi ya


ce: «Umra zuwa Umra kaffara ce ga abinda ke


tsakaninsu, kuma kuɓutaccen Hajji ba shi da


wani sakamako sai Aljanna»2 .


2- Na biyu: Azimin kwanaki tara, ko abin da ya


sawwaƙƙa daga cikinsu; saboda faɗin Annabi -


tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -.


«Babu wasu kwanaki da aiki na ƙwarai a


cikinsu ya fi soyuwa a wurin Allah sama da


1Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi.


2Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi.


4


waɗannan kwanaki goman». Kuma azumi yana


daga cikin mafi girman ayyukan alheri, Manzon


Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare


shi - ya kwaɗaitar zuwa gare shi, kuma ya


kwaɗaitar, daga hakan akwai faɗinsa - tsira da


amincin Allah su tabbata a gare shi -: «Babu wani


bawa da zai yi azumin yini ɗaya a tafarkin Allah


sai Allah Ya nisantar da fuskarsa daga wuta


(tsawon) shekara saba'in». 1


3- Ana shar'anta yin layya a ranar babbar sallah


da kuma kwanakin Tashriƙ, haƙiƙa ya tabbata


cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata


a gare shi -: «Ya yi layya da raguna biyu masu farar


fuska da baƙi-baƙi masu ƙaho, ya yanka su da


hannunsa, ya ambaci Allah ya yi kabbara, kuma ya


ɗora ƙafarsa akan fatun wuyayensu». 2


Daga A'isha - Allah Ya yarda da ita - ta ce:


Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata


a gareshi - ya ce: «Babu wani aiki da ɗan Adam


zai yi a ranar babbar sallah da yafi soyuwa ga Allah


fiye da zubar da jini, kuma za'a kawo shi ranar


alƙiyama da ƙahonninsa da gashinsa da ƙafafunsa,


kuma lallai jinin yana faɗuwa a wajen Allah a wani


1Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi.


2Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi.


5


da shi»1


 wuri kafin ya faɗi a ƙasa, don haka ku daɗaɗa rai


.


Kuma idan goma ga watan Zul-Hijjah ya shiga;


wanda yake son yin layya ya dakatar da cirar


wani abu daga gashinsa da fatar jikinsa; saboda


hadisin Ummu Salamah - Allah Ya yarda da ita -


daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a


gare shi - cewa shi ya ce: «Idan kun ga jinjirin


watan Zul-Hijja kuma ɗayanku yana son ya yi


layya; to ya kame daga (cirar) gashinsa da


faratansa». Kuma a cikin wani Lafazin: «Kada ya


cire wani abu daga gashinsa ko faratansa har sai


.


ya yi layya»2


 4- Kabbara, da Hailala, da ambaton Allah a cikin


waɗannan kwanaki goman da kwanukan


Tashriƙ; saboda hadisin Abdullahi Ibnu Umar


Allah Ya yarda da su- daga Annabi -tsira da


amincin Allah su tabbata a gare shi- ya ce: «Babu


wasu kwanaki da suka fi girma a wurin Allah


kuma mafi soyuwa a gare shi daga aiki a


cikinsu kamar waɗannan kwanaki goman, don


haka ku yawaita: Hailala, da Kabbara, da


Hamdala a cikinsu»3 .


1Tirmizi ne ya rawaito shi.


2Muslim ne ya rawaito shi.


3Ahmad ne ya ruwaito shi.


6


Kabbara kashi biyu ne kamar haka:


Sashe na farko: Kabbara kai tsaye, wadda ba ta


ƙayyadu da bayan salloli; sai dai ana shar'anta ta


a kowane lokaci.


Ana fara kabbara kai tsaye a idin layya daga


farkon goman Zul-Hijja zuwa ƙarshen ranar


kwanukan Tashriƙ: A dukkanin lokuta, a dare, da


rana, da hanya, da kasuwanni, da masallatai, da


gidaje, da kuma a duk wurin da ya halatta a


ambaci Allah - Maɗaukakin sarki -.


Sashe na biyu: Kabbara abar ƙayyadewa: Ita ce


wadda ake ƙayyadeta da bayan salloli a idin


layya musamman, da lokacinsa, kuma sifarta


kamar haka:


Na farko: Kabbara abar ƙayyadewa tana


farawane bayan sallar Asuba ranar Arfa, kuma


tana ƙarewa bayan sallar La'asar a rana ta uku na


kwanukan Tashriƙ. Wannan ga wanda ba


mahajjaci ba, amma mahajjaci kabbara abar


ƙayyadewa a haƙƙinsa tana farawa ne daga


Azahar ranar layya.


Na biyu: Siffar Kabbara: “Allahu Akbar, Allahu


Akbar, La'ilaha illallahu, Allahu Akbar Allahu


Akbar walillahil hamd” (Allah ne Mafi girma,


Allah ne Mafi girma, babu abin bautawa da


7


gaskiya sai Allah, Allah ne Mafi girma, Allah ne


Mafi girma, godiya ta tabbata ga Allah)1 .


5- Kula da yin sallar idi ga wanda ba mahajjaci


ba, da zuwa da wuri, da sauraron huɗuba; domin


tana daga cikin mafi girman alamomin


Musulunci; kuma saboda girman al'amarinta ne


aka umarci mata su fita zuwa gare ta har ma da


budurwai da masu haila; daga Ummu Aɗiyya -


Allah Ya yarda da ita - ta ce: «Mun kasance ana


umartar mu da mu fito ranar idi, harma mu


fito da budurwan da suke cikin budurcinsu,


har da masu haila ma mu fito da su sai su zama


a bayan mutane, sai suyi kabbara tare da


kabbarar masu sallah suyi addu`ah da addu`ar


su, suna masu fatan samun albarkar wannan


yini da kuma tsarkinsa». Kuma a cikin wani


Lafazin: «Ya umarci mata masu haila da su


nisaci wuraren sallar musulmai»2 .


6- Yawaita ayyuka na gari, daga cikin nafilfili na


ibada: Kamar sallah da sadaka, da karãtun Al


ƙur'ani mai girma, da umarni da kyakkyawa da


hani daga mummuna, da kyautatawa maƙwabta,


da sãda zumunci da sauran ayyuka na gari,


saboda faɗin Manzon Allah - tsira da amincin


1Ka duba: "al-Mughni na Ibni Qudama" (3/290), da "al-Sharhin al


Kabir tare da al-Muqni' da al-Insaf" (5/380).


2Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi.


8


Allah su tabbata a gareshi -: «Babu wasu


kwanaki da aiki na ƙwarai a cikinsu ya fi


soyuwa a wurin Allah sama da waɗannan


kwanakin goma". Suka ce: Ya Manzon Allah,


har jihadi domin ɗaukaka addinin Allah? Sai


Manzon Allah - tsira da amincin Allah su


tabbata a gare shi - ya ce: «Har jihadi domin


ɗaukaka addinin Allah, sai dai mutumin da ya


fita da kansa da dukiyarsa, kuma bai dawo da


komai ba». 1


Allah ne abin roƙo Ya amfane mu da abin da


muka sani, kuma Ya sanar da mu abin da zai


amfane mu, lallai cewa Shi Mai yawan kyauta ne


kuma Mai girma ne, tsira da amincin Allah su


tabbata ga Annabinmu Muhammad da iyalansa


da amincin Allah mai yawa.


 1Bukhari ne ya rawaito shi, da Tirmizi.


9


 


 


Teburin bayani


 


Falalar goman farko na Zul-Hijja .................................... 2


Gabatarwa .................................................................................. 2


Falalar goman Zul-Hijjah .................................................... 2


Falalar ayyuka a cikin kwanuka goma na zul-hijja: ... 4



 



Posts na kwanan nan

FALALAR GOMAN FARKO N ...

FALALAR GOMAN FARKO NA ZUL-HIJJA

SIFFAR SALLAR ANNABI ...

SIFFAR SALLAR ANNABI – TSIRA DA AMINCIJ ALLAH

FAHIMTAR ADDINI (SHIN ...

FAHIMTAR ADDINI (SHINE) TSARI DAGA FITINTINU 2

FAHIMTAR ADDINI (SHIN ...

FAHIMTAR ADDINI (SHINE) TSARI DAGA FITINTINU 1