Labarai

1


Jerin Littafan Shi’a Na 1


Aqidar


‘Yan Shi’a


dangane da


Alqur’ani


Umar Labxo


2


بسم الله الرحمن الرحيم


Gabatarwar


Jerin Littafan Shi’a


Aikina na yaqar bidi’ar Shi’a ya fara a garin Sakkwato, a wajejen


shekarar 1993, bayan na kwashe kimanin shekaru biyar ina koyar da fannin


Alfiraqul Islamiyya (Qungiyoyin Bidi’a a Musulunci) a Jami’ar Usmanu


Xanfodiyo.


Wannan aiki ya lafa bayan da na shiga gwagwarmayar kafa Shari’a a


jihohin Sakkwato da Kebbi a qarshen shekarar 1999. Daga baya kuma aikin


ya tsaya cik a lokacin da na tafi qasar Uganda domin koyarwa a Jami’ar


Musulunci ta Uganda (IUIU) dake garin Mbale a Uganda.


Bayan komowa Nijeriya a farkon shekarar 2003, na sabunta nashaxina


na yaqar Shi’a a Sakkwato, inda na fitar da littafin Vacin Tafarkin ‘Yan


Shi’a Da Aqidojinsu a qarshen shekarar 2004.


Ayyukana na rubuce-rubuce da lakcoci sun ci gaba a tsawon zamana


na shekaru huxu a Katsina, yayin da na fitar da littafin Larabci mai suna


Bayanu Fasadi Aqa’idis Shi’a. Da na koma Kaduna a qarshen shekarar


2009, na ci gaba da nashaxina, inda na buga littafai biyu: Dangantaka da


Auratayya Tsakanin Ahalul Baiti da Sahabbai da Wa Ya Kahse Hussaini?


A duk tsawon wannan lokaci, na kasance ina mai amanna da


muhimmancin karatu da rubutu a cikin ko wace al’umma. Wannan ya sa


koda yake ina wa’azi da lakcoci, amma ban fiye damuwa da yaxa su ta


hanyar kasakasai ba. Wani lokaci ma na kan hana a xauki karatuna a rikoda,


saboda ba na son mutane su dogara da sauraro maimakon karatu. A koda


3


yaushe, na fi qarfafa guiwar mutane da su karanta littafai, maimakon su


saurari kasset da radiyo.


A lokacin da na komo gida Kano, kuma na mai da hankali zuwa


qauyuka da yankunan karkara (saboda ganin makircin Shi’a na shiga


qauyuka), yaqinina da muhimmancin karatu da rubutu ya qaru. To sai dai na


fuskanci wata matsala guda: Yawancin mazauna qauyuka da yankunan


karkara suna tsoron littafi idan yana da girma, wani lokaci kuma ya kan yi


musu tsada. Qoqarin warware wannan matsala shi ya kawo tunanin rubuta


Jerin Littafan Shi’a.


A haqiqa ba mazauna qauyuka ne kawai suke tsoron karatu, ko suke


qin sa ba. Yawancin al’ummarmu suna da qiwar karatu da qyamarsa; sun fi


son su saurari radiyo ko rikoda. Sai dai abu ne da yake tabbas cewa, ba wata


al’umma da za ta ci gaba matuqar ba ta karatu.


Yawancin malaman zamani sun biye wa Malam Bahaushe, suna ganin


tunda mutanenmu ba sa son karatu, to sai a bar su da abinda suke so: kasset


da rikoda. Amma ni ban yarda da wannan ra’ayi ba. Ina ganin ba dai-dai ba


ne a biye wa mara lafiya da ya qi karvar magani don yana zaton maganin


yana da xaci. Maimakon haka, kamata ya yi a riqa ba shi kaxan-kaxan, yana


kurva sannu a hankali, har ya saba, kuma ya warke! Warakar al’umma na


cikin karatu.


Wannan shi ne abinda na yi da qananan littafai na wannan jeri. Kuma


abin ya yi nasar har na fara rubuta na Larabci da na Turanci.


Waxan nan jerin littafai, daga na xaya zuwa na tara, sun qunshi


duk abinda mai karatu yake bukata ya sani dangane da ‘yan Shi’a da


aqidojinsu da hukunce-hukuncensu da ibadojinsu da halayensu da xabi’unsu


da tarbiyyarsu da dangantakarsu da sauran Musulmi, musamman Ahalus


Sunna. Kuma, kamar yadda mai karatu zai gani qarara, a cikin waxan nan


4


al’amura duka, ‘yan Shi’a suna yin nesa da Musulunci da duk abinda ya


qunsa na aqidoji da hukunce-hukunce da ibadoji da halaye da ladubba da


xabi’u da tarbiyya. A taqaice, ‘yan Shi’a suna yin nesa da koyarwar


Alqur’ani da Sunnar Annabi da tafarkin Sahabbai da Ahalul Baiti baki xaya.


Wani abu muhimmi da wannan jerin littafai suka yi fice da shi, shi ne


dogaro kacokan wajen bayanin aqidojin ‘yan Shi’a da hukunce-hukuncensu


da ibadojinsu da halayensu da dangantakrsu da sauran Musulmi a kan


littafan malamansu da shaihunnansu waxanda suka yarda da su, tare da


lazimtar amana wajen naqalto maganganunsu daga littafan nasu. Saboda


haka, abinda mutum zai karanta a cikin waxan nan littafai dangane da ‘yan


Shi’a kai-tsaye ne daga bakin mai ita. Duk abinda aka faxi dangane da su


daga littafansu aka xauko, ba daxi, ba ragi. Wannan kuma domin a yi adalci


ne gare su, kuma a lazimta musu hujja.


Ina roqon Allah Maxaukaki da ya shiryi mutane da waxan nan ‘yan


littafai, ya rubuta mun ladansu, ya yi sakamako da alheri ga duk wanda ya


taimaka wajen buga su, ko yaxa su, ko sada su ga makaranta ta kowace


hanya.


Kano Umar Labxo


Afrilu, 2016


5


Aqidar ‘Yan Shi’a Dangane da Alqur’ani


‘Yan Shi’a suna qudure cewa Alqur’ani mai girma wanda yake a


hannun Musulmi a yau ba cikakke ba ne; domin, a ganinsu, Sahabbai da


suka tattara Alqur’ani a zamanin Abubakar da Usman, Allah ya qara yarda a


gare su, sun sauya abubuwa da dama a cikinsa ta hanyar yin qare-qare da


rage-rage a cikin ayoyinsa. Suka ce wai wannan Alqur’ani da muke karanta


wa a yau babu abinda yake cikinsa daga abinda aka saukar ga Annabi


(SAW) sai xan kaxan.


‘Yan Shi’a suna zargin Sahabbai da sauya Littafin Allah, da canja


ayoyinsa. Suka ce wai Sahabban sun yi haka ne ta hanyar xebe ayoyi masu


yawa da aka saukar waxanda suke tona asirinsu da kuma ayoyi da suke nuna


falalar Ali binu Abi Xalib(RA) da zuri’arsa. Abinda suke nufi da tona


asirinsu, wai bayyana kafirci da munafuncin Sahabbai. Wal iyazu billahi!!


Saboda haka a wurin ‘yan Shi’a, ayoyi da yawa dake cikin Alqur’ani


ba maganar Allah ba ce, wannan ya sa suke zavar abinda ya dace da son


zukatansu a cikin Alqur’ani, saura kuwa su yi burus da shi.


Wani babban malaminsu mai suna Hashim binu Sulaiman Albaharani


yana faxi a cikin wani littafi nasa da ya rubuta a kan Tafsiri, “Ka sani cewa a


haqiqanin gaskiya wacce babu kokwanto a cikinta, gwargwadon ruwayoyi


mutawatirai, wannan Alqur’ani da yake hannunmu sauye-sauye sun faru a


cikinsa bayan rasuwar Manzon Allah (SAW) kuma waxanda suka tattara shi


bayan Annabi sun xebe kalmomi da ayoyi masu yawa daga cikinsa.”1


A cikin littafin Alkafi , littafin da ya fi ko wanne inganci a wajen ‘yan


Shi’a, an yi bayanin gwargwadon abinda aka xebe daga cikin Alqur’ani.


Marubucin littafin, watau Muhammad binu Ya’aqub Alkulaini, ya ce, “An


1 Duba Alburhan fi Tafsiril Qur’an na Hashim binu Sulaiman Albaharani, bugun Almadaba’atul Ilmiyya,


Qum-Iran, 1393, shafi na 36.


6


ruwaito daga Abu Abdullahi (watau Imamin Shi’a na shida) cewa


Alqur’anin da Jibrilu ya zo da shi ga Muhammad (SAW) aya dubu goma sha


bakwai (17,000) ne.”1 Wannan yana nufin ke nan cewa Kur’anin da yake


hannunmu xan ragowa ne kawai; domin kuwa a bisa ga wannan ruwaya


waxanda suka tattara littafin a bayan rasuwar Annabi (SAW) sun xebe


kimanin sulusi biyu na littafin. Za mu tabbatar da haka idan muka lura da


cewa Alqur’anin da yake hannunmu, wanda Musulmi suka sani a yau,


ayoyinsa dubu shida da xari biyu da talatin da shida ne (6,236) kawai, kamar


yadda malaman Sunna suka tabbatar.2


Akwai ruwayoyi masu yawa a cikin littafan malaman Shi’a da suke


izna da su, waxanda suka tabbatar da wannan mugunyar aqida tasu. Wani


malaminsu mai suna Ni’imatullahi Aljaza’iri da ya qididdige ruwayoyin ya


tabbatar da cewa sun fi dubu biyu.3 Saboda haka, ita aqida ce wacce dukkan


‘yan Shi’a, ciki har da na Nijeriya, suka yarda da ita. Kuma idan ka ji suna


musun ta, to taqiyya ce kawai suke yi, watau munafunci da yaudara!!


Wani qasurgumin malamin Shi’a, mai suna Hussain binu Muhammad


Annuri Alxabarsi, ya rubuta shirgegen littafi musamman don ya tabbatar da


aqidar ‘yan Shi’a cewa Alqur’anin nan da yake a hannunmu a yau ba


cikakke ba ne, kuma akwai sauye-sauye, da qare-qare, da rage-rage, a


cikinsa. Littafin wanda ya sa wa suna Faslul Khixab fi Ithbati Tahrifi Kitabi


Rabbil Arbab, (watau Yankakkiyar Magana A Kan Tabbatar Da Sauya


Littafin Mamallakin Mamallaka), ya qunshi dubunnan ruwayoyi daga


Imaman Shi’a da malamansu waxanda suke tabbatar da cewa wai waxan


nan sauye-sauye, da qare-qare, da rage-rage Sahabbai, waxanda suka haxa


1 A duba Alkafi na Muhammad binu Ya’aqub Alkulaini, Darul Kutubil Islamiyya, Teheran-Iran, ba tarihi,


mujalladi na 2, shafi na 634.


2 Duba Tafsiru Ibnu Kathir na Isma’il binu Kathir, bugun Maktabatus Safa, Alqahira, 1423/2002,


mujalladi na 1, shafi na 7.


3 Duba Faslul Khidab na Hussain binu Muhammad Taqiyyud Din Aldabarsi, ba tarihi, shafi na 248.


7


da Abubakar da Umar da Usman, Allah ya yarda da su baki xaya, su ne suka


zartar da su. A cikin littafin har ila yau, an tabbatar da cewa malaman Shi’a


kaf, magabatansu da na bayansu, sun haxu a kan wannan aqida.1


‘Yan Shi’a suna da nasu Alqur’ani dabam, wanda suke kira Mushafu


Faxima, watau Kundin Faxima. Dangane da wannan littafi, malaman Shi’a


suna dangana ruwaya ga Imaminsu na shida, Imam Ja’afar Sadiq, cewa wai


ya ce, “Faxima ta bar wani kundi wanda ba Qur’ani ba ne, amma kuma


kalmar Allah ce da ya yi wahayin ta zuwa gare ta. Shi kundin shiftar Annabi


ne kuma rubutun hannun Ali.”2 A wata ruwayar kuma, ya ce: “Shi kundi ne


da ya ninka Qur’ani uku kuma amma, na rantse da Allah, babu kalma xaya a


cikinsa ta Qur’aninku.”3


A ganinsu, Mushafu Faxima shi ne Qur’ani na gaskiya wanda


Imamansu suka gado shi daga Nana Faxima xiyar Manzon Allah (SAW) da


mijinta Ali binu Abi Xalib, Allah ya qara musu yarda. Muhammad binu


Hassan Alsaffar, wanda ake lasafta shi daga cikin manyan malaman Shi’a


magabata (ya rasu a shekara ta 290 B.H.), ya ruwaito a cikin littafinsa,


Basairud Darajati , daga Imam Abu Ja’afar wai ya ce, “Babu wani da zai iya


da’awar cewa ya tattare Alqur’ani dukkaninsa, zahirinsa da baxininsa, sai


masu wasici,” yana nufin Imamai. Har yau, a cikin littafin ya ruwaito daga


gare shi yana cewa, “Babu wani daga mutane wanda zai ce ya tattare


Alqur’ani dukkaninsa, kamar yadda Allah ya saukar da shi, sai maqaryaci.


Ba wanda ya tattare shi, ya haddace shi kamar yadda aka saukar da shi, sai


Ali binu Abi Xalib da Imamai a bayansa.”4


1 Duba Faslul Khidab na Aldabarsi, shafi na 34.


2 A duba Basa’irud Darajat na Alsaffar, shafi na 176.


3 Duba Alkafi na Kulaini, mujalladi na 1, shafi na 171,


4 Duba Basa’irud Darajatil Kubra fi Fada’ili Aali Mahammad na Muhammad binul Hassan binu


Farrukh Alsaffar, bugun Manshuratul A’alami, Teheran-Iran, 1362, shafi na 213.


8


Qur’anin ‘yan Shi’a ya sha bamban da Alqur’anin Musulmi ta fuskoki


masu yawa. Mun riga mun gabatar da bayanin bambancinsu ta wajen


jimillar ayoyinsu, inda Qur’anin ‘yan Shi’a yake da adadin ayoyi dubu goma


sha bakwai (17,000) dai-dai wa daida, a yayin da namu yake da ayoyi dubu


shida da xari biyu da talatin da shida (6,236) kacal. Ta fuskar tsawon surori


ma, littafan guda biyu sun sha bamban. Ga misali, ya zo a cikin Kitab


Sulaim binu Qais, mashahurin littafin nan na Shi’a wanda saboda ingancinsa


a wajensu suke masa laqabi da A.B.C. Din Shi’a, cewa wai Suratul Ahazab


wacce take da ayoyi 73 a Qur’aninmu, su a nasu Qur’anin adadin ayoyin


Baqara ne da ita, watau 286. Suratun Nur kuwa, wacce take da ayoyi 64, su


a wajensu ayoyi 160 ke gareta. Suratul Hujurati kuma, wacce a cikin


Qur’anin da muka sani ayoyinta 18 ne kacal, su a nasu Qur’anin ayoyinta 90


ne dai-dai wa daida.1


Ta fuskar adadin surori ma, akwai xan bambanci saboda akwai wasu


surori waxanda ‘yan Shi’a suke qudure cewa an xebe su daga cikin


Alqur’ani. Misali shi ne wata sura da suke kira Suratul Wilaya wacce suka


ce wai a cikinta Allah ya yi umarni da a naxa Ali binu Abi Xalib a matsayin


Khalifa bayan rasuwar Annabi (SAW). Wannan sura ba mu san ta ba, babu


ita a cikin Alqur’aninmu, amma su ‘yan Shi’a suna qudure cewa wai


Sahabbai ne suka xebe ta don cin amana, a faxinsu, domin su hana Ali binu


Abi Xalib haqqinsa na gadar Annabi, suka naxa Abubakar a makwafinsa.


Wannan ita ce aqidarsu. Wal iyazu billah!!


Dangane da kalmomi da lafuzza da ma’anoni, babu wata sura a cikin


Alqur’ani kamar yadda muka san shi face ‘yan Shi’a sun zo da savanin


kalmomi ko ayoyi a cikinta. Za mu ba da ‘yan misalai kaxan. A qarshen


1 Duba Kitab Sulaim binu Qais na Sulaim binu Qais Alhilali Alkufi, bugun Mu’assasatul A’alami, Bairut,


ba tarihi, shafi na 122.


9


Suratul Fatiha suna karanta: Ihdinas siraxal mustaqim. Siraxa man an’amta


alaihim, gairil magdubi alaihim wa gairid dalin. A farkon Suratul Asri, suna


karanta: Wal asr innal insana la fi khusr. Wa innahu fihi ila akhirid dahr.


Illal lazina amanu wa amilus salihati, wa’atamaru bit taqwa, wa’atamaru bis


sabr. Suratul Fili kuma, watau Alam Tara Kaifa, suna fara ta kamar haka:


Alam ya’atika kaifa fa’ala rabbuka bi ashabil fili.


Waxan nan ‘yan misalai ne kawai muka kawo domin mai karatu ya


ganewa idanunsa. Wanda yake son ya ga waxannan sauye-sauye filla-filla,


to sai ya koma ga littafin Alshi’atu wal Qur’an na Ihsan Ilahi Zahir, Allah ya


yi masa rahama, domin shi ya tsamo waxan nan canje-canje waxanda suka


shafi surorin Alqur’ani guda 114 baki xaya daga littafan ‘yan Shi’a kuma ya


jera su, ya rattaba su, tare da ruwayoyinsu.


Wataqila mai karatu ya yi tambaya: Don me ‘yan Shi’a ba sa buga


wannan tafkeken “Qur’ani” nasu, wanda ya ninka na Musulmi har sau uku,


su sayar a kasuwa? Amsa ita ce, abinda yake hana su bayyana wannan littafi


nasu shi ne taqiya, watau munafunci da yaudara!! A haqiqa ‘yan Shi’a ba


Qur’aninsu kaxai suke voyewa ba; aqidarsu ta taqiya tana umarnin su da su


voye manyan littafan malamansu, waxanda suka qunshi aqidojinsu da


manufofinsu, sai ga manyan mabiyansu waxanda suka riga suka yi zurfi a


cikin tafarkinsu. Kaxan daga cikin littafansu suke sayarwa a kasuwa,


sauran sai dai a same su a manyan cibiyoyinsu da makarantunsu.


Qur’aninsu kuwa, idan akwai shi cikakke, to babu shakka ba mai ganin sa


sai manyan shaihinnansu, sai kuma almajirai amintattu.


Wannan ya sa ‘yan Shi’a suke qalubalantar mutane da cewa, idan


gaskiya ne suna da nasu Qur’ani dabam, kamar yadda ake dangana musu (ko


da yake mai karatu yana iya ganin cewa ruwayoyinsu ne suka tabbatar da


10


samuwarsa) to don me ba’a fito musu da shi su gan shi? Su kan yi tambaya:


Ina Qur’anin nasu yake?


To wannan tambaya tasu malamansu sun amsa ta da kansu. Shaihinsu,


Hussain Alkhurasani yana cewa, “ Mu ‘yan Shi’a muna qudure cewa akwai


wani Alqur’ani da Imam Ali ya rubuta da hannunsa mai albarka, bayan da


ya qare yi wa Annabi sutura kuma ya zartar da wasiyyarsa. Littafin ya ci


gaba da zama a hannun Imamai a matsayin amana daga Allah har ya iso ga


Imam Mahadi wanda ya adana shi kuma zai fito da shi a yayin da zai


bayyana.”1


Wannan ruwaya tana tabbatar da cewa Qur’anin ‘yan Shi’a ya kasance


akwai shi, kuma ya ci gaba da zama a hannun Imamai har na tsawon


kimanin shekaru 250 daga zamanin Sayyidina Ali(RA) zuwa zamanin


Mahadinsu (watau Imaminsu na 12) wanda aka haife shi a shekara ta 255


bayan Hijira. Wannan Imamin nasu shi ne ya tafi da littafin a lokacin babbar


fakuwarsa, kuma zai komo da shi a lokacin da zai bayyana a qarshen duniya.


‘Yan Shi’a suna qudure cewa Imaminsu na 12, wanda suke kira


Mahadi ya faku fakuwa biyu, babba da qarama. A lokacin qaramar fakuwa,


wacce ta yi tsawon shekara 65, ya riqa saduwa da manyan almajiransa


waxanda ya riqa aiko su da saqwanni zuwa ga mabiyansa. Kuma a shekara


ta 259 bayan Hijira, ya shiga fakuwa babba, wacce yake kai har zuwa yau,


kuma wacce a cikinta ba ya saduwa da kowa. Wannan babbar fakuwa za ta


qare a qarshen duniya, sa’ad da Mahadin zai bayyana don ya qaddamar da


wasu ayyuka masu ban tsoro da ban mamaki.2 Mai son ganin waxan nan


ayyuka, sai ya duba littafinmu mai taken Mugun Nufin ‘Yan Shi’a ga


Al’umma.


1 Duba Al’islam ala Dau’it Tashayyu’i na Hussain Alkhurasani, ba tarihi, shafi na 204.


2 Domin bayanin wannan tatsuniya, duba A Critical Revision of Shi’ah na Imam Musa Musawi, bugun the


Supreme Islamic Council, Columbia-Amurka, 1412/1992, shafi na 77-78.


11


Har yau, wani malamin nasu ya ba da bayani mai kama da wannan.


Ya ce, “Bayan rasuwar Annabi, Sarkin Musulmi (yana nufin Ali) ya xauko


Alqur’ani a cikin mayafinsa, ya kawo wa Abubakar da Umar suna zaune a


Masallaci su da wasu mutane. Ya ba su shi, amma sai suka ce: Ba ma


bukatar Qur’aninka; muna da namu Qur’anin, ya ishe mu! Sai ya ce: Shi ke


nan, ba za ku qara ganin sa ba daga yau, sai Mahadi ya bayyana!”1


Waxan nan bayanai daga malaman Shi’a, idan sun gaskata, suna


tabbatar da cewa Qur’anin ‘yan Shi’a ya kasance akwai shi a hannun


Imamansu, kuma almajiran Imamai sun karanta shi har lokacin da Imami na


12 ya shiga das hi kogo inda ya faku fakuwarsa ta qarshe. Saboda haka sai


su jira shi daga nan har sanda jaki ya tsuri qaho!


Akwai wani xan Shi’a wanda ya tava yin wata burga. Ya xauko


Qur’ani cikakke na Musulmi, wanda aka buga a qasar Iran, ga tambarin


Jumhuriyar Islama rangaxau a bangon littafin. Sa’an nan ya ce, “Kun ce


‘yan Shi’a ba su yarda da Qur’ani ba, ya aka yi suka buga wannan?” Sai aka


ce masa, ai buga Qur’ani ba shi ne yarda da shi ba. Idan ‘yan Shi’a sun yarda


da Alqur’ani don me suke kafirta waxanda ya yi wa shaida da imani, watau


Sahabban Annabi(SAW)? Sai gogan naka ya yi turus! Allah ya tsarshe mu


vata.


Bayan mun gabatar da bayani a kan wannan aqida kamar yadda take a


cikin littafan ‘yan Shi’a masu inganci a wajensu, muna ganin babu wani


Musulmi da yake buqatar wani qarin bayani dangane da abinda aqidar ta


tattare na kafirci da jahilci da vata. Amma saboda yankan hanzari ga masu


kiran kansu ‘yan Shi’a, bari mu yi bayanin kafircin wannan aqida a taqaice.


1 Duba Nur Al’anwar fi Sharhis Sahifatis Sajjadiyya na Ni’imatullahi Aljaza’iri, bugun Darul Mahajjatil


Baida, Bairut, 1420, shafi na 175.


12


Da farko dai aqidar ta qaryata Alqur’ani mai girma saboda a cikinsa


Allah mai girma da xaukaka ya tabbatar da cewa ya tsare Littafinsa ta yadda


qari ko ragi ba za su shige shi ba. Ubangiji Maxaukaki ya ce, “Lalle, mu ne


muka saukar da Ambato (Alqur’ani), kuma lalle mu, masu kiyayewa ne gare


shi.” (Suratul Hijr: 9). A wata ayar kuma, ya tabbatar da cewa varna ba ta


shiga wannan littafi ko ta halin qaqa: “Waxan nan da suka kafirta game da


Alqur’ani a lokacin da ya je musu, kuma lalle ne, haqiqa, littafi ne


mabuwayi. Varna ba za ta je masa ba daga gaba gare shi, kuma ba za ta zo


ba daga baya gare shi. Saukarwa ce daga Mai Hikima, Godadde.” (Suratu


Fussilat: 41 – 42).


Na biyu, wannan aqida har ila yau, tana qaryata Alqur’ani ta wata


fuskar dabam; domin tana kafirta ko fasiqantar da waxanda Allah ya bayar


da labari cewa ya yarda da su kuma ya yi musu gafara: su ne Sahabban


Annabi(SAW), Allah ya qara musu yarda baki xaya. Aqidar ta kafirta


Sahabbai ta hanyar dangana musu sauya Alqur’ani, da voye abinda Allah ya


saukar, da yin qari da ragi a cikinsa. Allah yana faxi dangane da Sahabban


Annabinsa: “Kuma magabata na farko daga Muhajirina da Ansar da


waxanda suka bi su da kyautatawa, Allah ya yarda daga gare su, su kuma


sun yarda daga gare shi, kuma ya yi musu tattalin gidajen Aljanna: qoramu


suna gudana a qarqashinsu, suna madauwama a cikinsu har abada. Wancan


ne babban rabo mai girma.” (Suratut Tauba: 100).


Xan uwa mai karatu ka dubi abinda Allah ya ce dangane da Sahabban


Annabinsa, har ma da waxanda suka bi su da kyautatawa, sa’an nan ka dubi


abinda ‘yan Shi’a suka jingina musu na sauya maganar Allah da cin amanar


Manzonsa, za ka san cewa lalle ‘yan Shi’a sun yi nisa daga barin shiriya.


Muna roqon Allah ya arzuta su da tuba kyakkyawa, da komawa ga


13


tafarki madaidaici: tafarkin Sunnar Annabi(SAW). Mu kuma, ya nesantamu


da irin wannan vata mabayyani.



Posts na kwanan nan

SAKO DAGA MUSULMI MAI ...

SAKO DAGA MUSULMI MAI WA'AZI ZUWA GA MUTUM KIRISTOCI

FALALAR AZUMIN KWANA ...

FALALAR AZUMIN KWANA SHIDA SHAWAL

TAKAITACCEN BAYANI MA ...

TAKAITACCEN BAYANI MAI ANFANI GA SABON SHIGA MUSULUNC

ZIKIRAI WADANDA AKE Y ...

ZIKIRAI WADANDA AKE YIN SU DA SAFE DA KUMA YAMMA