Labarai

1


Jerin Littafan Shi’a Na 11


Aqidar Ahalus Sunna


Umar Labxo


2


بسم الله الرحمن الرحيم


Gabatarwa


Godiya ta tabbata ga Allah Maxaukakin Sarki. Tsira da aminci su tabbata ga Annabi Muhammad


(SAW) da Alayensa da Sahabbansa da waxanda suka bi tafarkinsu har zuwa Ranar Sakamako.


Bayan haka, yana daga cikin qa’idojin koyarwa da tarbiyya idan aka hana wa mutane abu


mummuna sai a musanya musu da wani kyakkyawa wanda zai maye makwafin na farkon kuma


ya cike gurbinsa. Bin wannan qa’ida ne ya sa, bayan bayanin vacin tafarkin Shi’anci da


muguscin aqidun ‘yan Shi’a a cikin littafai goma da suka gabata a wannan jeri, mu ka ga ya


zama wajaba mu kawo bayanin tafarkin Sunna da Aqidar Ahalus Sunna wacce ita ce aqidar


Annabi (SAW) da Sahabbansa, da Tabi’ai da waxanda suka bi tafarkinsu har ya zuwa yau.


Wannan littafi fassara ce ta littafin Al’aqidatul Wasixiyya na Shaihul Islami Ibnu


Taimiyya, Allah ya jiqan sa. Littafin ya tattare aqidar Ahalus Sunna a sauqaqe, tare da dogaro


kacokan wajen tabbatar da ita a kan Alqur’ani da Hadisai ingantattu a bisa fahimtar magabata


na-gari.


Rubuta aqidar Ahalus Sunna a sauqaqe tare da dogaro da Alqur’ani da Sunna a bisa


fahimtar magabatan al’umma, kamar yadda Ibnu Taimiyya ya yi a cikin wannan littafin, abu ne


da xaruruwan malaman Sunna suka yi tun daga qarni na biyu bayan Hijira har ya zuwa yau.


Wani malami na zamanin nan mai suna Abdussalam binu Barjis Aali Abdilkarim ya tattara


tarihin irin waxan nan littafai xari uku da talati da huxu (334) da manyan malaman Sunna suka


rubuta tun daga shekarar 167 B.H. har zuwa 1400 B.H., a cikin littafinsa mai suna Tarikhu


Tadwinil Aqidatis Salafiyya, wanda ya buga a shekara ta 1430/2009.


Littafan aqida yawanci suna qunsar qudure-qudure da Ahalus Sunna suke qudurewa a


matsayin imani, kamar qudure cewa imani ya haxa magana da aiki, da cewa ana sifanta Allah da


abinda ya sifanta kansa da shi ko Manzonsa ya sifanta shi da shi, da cewa Alqur’ani zancen


Allah ne ba halittacce ba ne, da cewa Allah shi ne Mahaliccin kome, da cewa abinda Allah ya so


shi yake kasancewa kuma abinda bai so ba ba zai kasance ba, da cewa Allah mai iko ne akan


dukkan kome, da cewa Ahalus Sunna ba sa kafirta mai sallah don ya aikata zunubi, da cewa suna


imani da ceto ga masu zunubai, da sauran su. Irin waxan nan abubuwa su ne tattare a cikin


littafin da muke gabatarwa a nan.


Wani abu da irin waxan nan littafai suke sifantuwa da shi, wanda kuma littafin da muke


fassarawa shi ma ya sifantu da shi, shi ne dogaro kacokan da ayoyin Alqur’ani da hadisan


Annabi ingantattu, kamar yadda muka ambata a baya kaxan, saboda al’amuran aqida babu ra’ayi


ko ijtihadi a cikin su. Don haka mai karatu zai ga ruwan ayoyi a cikin wannan littafi, a yawancin


lokuta ma babu wata fassara ko qarin bayani. Kamar yadda mai karatu zai lura da cewa,


3


yawancin hadisan da aka ambata a cikin littafin hadisan Sahihaini ne, watau Bukhari da Muslim,


waxanda su ne qololuwar inganci.


Wannan shi ne abinda yake gaskata abinda muka gabatar da ambaton sa a baya cewa,


wannan aqida ita ce aqidar Annabi (SAW) da Sahabbansa; domin an tsamota ne kai tsaye daga


Alqur’ani da Sunna, kuma gwargwadon fahimtar Sahabbai da Tabi’ai da waxanda suka bi su da


kyautatawa har zuwa ranarmu ta yau.


Kuma cewa wannan fahimta ita ce fahimtar Sahabbai da Tabi’ai ba wai faxi ne kawai da


baki ba, a’a haka abin yake. Idan mutum ya duba Kitabut Tauhid a cikin Sahihul Bukhari haka


zai gani. Haka nan, idan ya duba babin Tauhidi ko aqida a cikin littafan Hadisi duka: Muslim da


Abu Dawud da Tirmizi da Nasa’i da Ibnu Majah da Muwaxxa, da sauransu, haka zai gani.


Kuma wannan ita ce aqidar limaman Mazhabobi: Imam Malik da Shafi’i da Abu Hanifa


da Ahmad binu Hambal da mabiyansu. Ba’a samu kauce wa wannan aqida ba sai a wajen ‘yan


baya, a lokacin da ilmin Falsafa ya yaxu a tsakanin Musulmi kuma suka tasirantu da shi. A


wannan lokaci ne qungiyoyin bidi’a, kamar Mu’utazilawa, suka fara dogaro da hankali,


maimakon nassi, wajen fahimtar al’amuran aqida. Kuma ko ba’a faxi ba, hankali wanda a


xabi’arsa taqaitacce ne, ba zai wadatar ba a cikin al’amuran aqida da imani.


Wannan ya sa dukkan maluma na gari suka zargi Ilmul Kalami, watau ilmin da yake


dogaro da hankali wajen warware mas’alolin Tauhidi da aqida. Kuma suka xaura himma wajen


rubuta irin waxan nan littafai na aqida waxanda muke gabatar da xaya daga cikin mafi


kyawunsu: Al’aqidatul Wasixiyya.


Mun yi fassara mai sauqi, da nufin ganar da kafatanin makaranta, kamar yadda muka


saba a cikin ayyukanmu, tare da kiyayewa da saqon da littafin yake isarwa, babu daxi, babu ragi.


A wajen fassara ayoyin Alqur’ani, mun dogara da Tarjamar Ma’anonin Alqur’ani Mai Girma


zuwa ga Harshen Hausa na Shaihu Abubakar Mahamud Gumi, ba mu fita daga cikinsa ba sai a


‘yan wurare kaxan. Dangane da hadisai kuwa, rashin tsayayyar fassara ga littafan Hadisai ta


tilasta mana dogaro da kai wajen fassara su, tare da qoqarin bayyana ma’anarsu da kiyayewa da


manufarsu.


Muna roqon Allah Maxaukaki ya xora mu a bisa doron sawaba, ya sa ihilasi da tsarkin


niyya a cikin ayyukanmu da maganganunmu, ya nesanta mu da riya da son-a-sani. Allah ya


amfane mu da abinda muka rubuta, ya sa ya zama guzurin zuwa kabari. Allahumma Amin.


4


Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jinqai


Aqidar Tawagar Masu Tsira


Godiya ta tabbata ga Allah wanda ya aiki Manzonsa da shiriya da addinin gaskiya domin


ya rinjayar da shi a kan addinai dukansu. Kuma Allah ya isa ya zama mai shaida.


Ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kaxai, ba shi da abokin tarayya,


don tabbatarwa ga tauhidinsa. Kuma ina shaidawa cewa, Muhammad bawansa ne, kuma


Manzonsa ne. Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, da Alayensa da Sahabbansa, tare da


sallamawa mai tarin yawa.


Bayan haka, wannan ita ce aqidar tawagar masu tsira, taimakakku har zuwa tsayuwar


alqiyama: Ahalus Sunna wal Jama’a. Shi ne imani da Allah da mala’ikunsa da littafansa da


Manzanninsa da tashi bayan mutuwa. Da imani da qaddara, alherinta da sharrinta.


Yana daga imani da Allah, imani da abinda ya sifanta kansa da shi a cikin littafinsa, da


abinda Manzonsa ya sifanta shi da shi, ba tare da karkatarwa ba ko vata ma’ana, haka nan ba tare


da takamaimai ko kamantawa ba. Amma suna imani da cewa, shi Allah Maxaukaki “Wani abu


bai zama kamar tamkarsa ba, kuma shi ne mai ji, mai gani.” (Suratush Shura: 11).


Don haka ba sa kore masa abinda ya sifanta kansa da shi, kuma ba sa karkatar da zance


ga barin mahallinsa. Ba sa ilhadi a cikin sunayen Allah da ayoyinsa. Ba sa takamaimaitar da


sifofinsa kuma ba sa kamanta su da sifofin halittunsa. Domin shi, tsarki ya tabbatar masa, ba shi


da takwara, ko sako, ko kini, kuma ba’a kwatanta shi da halittunsa, tsarki ya tabbatar masa, ya


xaukaka. Babu shakka shi, Maxaukaki, shi ne ya fi sanin kansa, ya fi sanin waninsa. Shi ne mafi


gaskiyar zance kuma mafi kyawun magana daga halittarsa.


Sa’an nan kuma, Manzanninsa masu gaskiya ne, ababen gaskatawa, savanin waxanda


suke faxi masa abinda ba su sani ba. Don haka ya ce, “Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka,


Ubangijin rinjaye, daga barin abinda suke siffantawa. Kuma aminci ya tabbata ga Manzanni.


Kuma godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu.” (Suratus Saffat: 180-182). Sai Ubangiji ya


tsarkake kansa ga barin abinda masu savawa Manzanni suke sifanta shi da shi, kuma ya yi


sallama ga Manzanni saboda kuvutar abinda suka faxi daga tawaya da aibu.


Shi, tsarki ya tabbatar masa, ya haxa tsakanin korewa da tabbatarwa a cikin abinda ya


ambaci kansa kuma ya sifanta kansa da shi. Saboda haka, babu karkacewa ga Ahalus Sunna wal


Jama’a ga barin abinda Manzanni suka zo da shi. Domin shi ne tafarki madaidaici, tafarkin


waxanda Allah ya yi ni’ima a gare su na Annabawa da Siddiqai da Shahidai da Salihan bayi.


5


Babi Na Xaya


Sunayen Allah da Sifofinsa a cikin Alqur’ani


Gamewa tsakanin Korewa da Tabbatarwa


a cikin Sifanta Allah Maxaukaki


Daga cikin wannan akwai abinda Allah ya sifanta kansa da shi a cikin Suratul Ikhlas,


wacce take dai-dai da sulusin Alqur’ani, inda yake cewa, “Ka ce: Shi ne Allah Makaxaici, Allah


wanda ake nufin sa da bukata. Bai Haifa ba, kuma ba’a haife shi ba. Kuma babu xaya da ya


kasance tamka a gare shi.”


Haka nan abinda ya sifanta kansa da shi a cikin mafi girman aya a Littafinsa, inda yake


cewa, “Allah babu wani ubangiji face shi, Rayayye, mai tsayuwa da kome, gyangyaxi ba ya


kama shi, kuma barci ba ya kama shi, shi ne da abinda yake cikin sammai da abinda yake cikin


qasa. Wane ne wanda yake yin ceto a wurinsa, face da izininsa? Yana sanin abinda yake a gaba


gare su da abinda yake a bayansu. Kuma ba su kewayewa da kome daga ilminsa, face da abinda


ya so. Kursiyyunsa ya yalwaci sammai da qasa. Kuma tsare su ba ya nauyayar sa. Kuma shi ne


maxaukaki, mai girma.” (Suratul Baqara: 255).


Gamewa tsakanin Xaukakarsa da Kusancinsa


da Azaliyyarsa da Abadiyyarsa1


A cikin faxin Allah, tsarki ya tabbatar masa, “Shi ne na farko, na qarshe, Bayyananne,


Voyayye, kuma shi ne Masani ga dukan kome.” (Suratul Hadid: 3). Da faxinsa Maxaukaki,


“Kuma ka dogara a kan Rayayye wanda ba ya mutuwa.” (Suratul Furqan: 58). Da faxinsa,


“Kuma shi ne Masani, mai hikima.” (Suratut Tahrim: 2). “Kuma shi ne mai hikima, mai


labartawa.” (Suratu Saba: 1).


Kewayewar Ilminsa da Dukan Halittarsa


“Ya san abinda yake shiga a cikin qasa da abinda yake fita daga gare ta, da abinda yake


sauka daga sama da abinda yake hawa a cikinta.” (Suratu Saba: 2). “Kuma a wurinsa mabuxan


gaibi suke, babu wanda yake sanin su face shi, kuma yana sanin abinda ke a cikin tudu da ruwa,


kuma wani ganye ba ya faxuwa, face ya san shi, kuma babu wata qwaya a cikin duffan qasa,


1 Azaliyyarsa: rashin farko, watau na tun fil azal. Abadiyyarsa: rashin karshe, watau na har abada.


6


kuma babu xanye, kuma babu qeqasasshe, face yana a cikin wani littafi mai bayyanawa.”


(Suratul An’am: 59).


Kuma da faxinsa, “Kuma wata mace ba ta yin ciki, kuma ba ta haihuwa, face da saninsa.”


(Suratu Faxir: 11 da Suratu Fussilat: 47). Da faxinsa, “Domin ku san lalle Allah mai iko ne a kan


dukan kome, kuma lalle Allah, haqiqa ya kewaye ga dukan kome da sani.” (Suratux Xalaq: 12).


Da faxinsa, “Lalle Allah shi ne mai arzutawa, mai ikon yi, mai cikakken qarfi. (Suratuz Zariyat:


58).


Tabbatar da Ji da Gani ga Allah Maxaukaki


A cikin faxin Allah, “Wani abu bai zama kamar tamkarsa ba, kuma shi ne mai ji, mai


gani.” (Suratush Shura: 11). Da faxinsa, “Lalle ne, Allah madalla da abinda yake yi muku wa’azi


da shi. Lalle ne Allah ya kasance mai ji ne, mai gani.” (Suratun Nisa: 58).


Tabbatar da So da Nufi ga Allah Maxaukaki


A cikin faxin Allah, “Kuma don me, a lokacin da ka shiga gonarka, ka ce: Abinda Allah


ya so (shi ke tabbata) babu wani qarfi face gami da Allah.” (Suratul Kahaf: 39). Da faxinsa,


“Kuma da Allah ya so, da ba za su yaqi juna ba, kuma amma Allah yana aikata abinda yake


nufi.” (Suratul Baqara: 253).


Da faxinsa, “An halatta muku dabbobin jin daxi, face abinda ake karantawa a kanku, ba


kuna masu halattar da farauta ba alhali kuwa kuna masu harama. Lalle ne, Allah yana hukunta


abinda yake nufi.” (Suratul Ma’ida: 1). Da faxinsa, “Domin haka wanda Allah ya yi nufin ya


shiryar da shi sai ya buxa qirjinsa domin Musulunci, kuma wanda ya yi nufin ya vatar da shi, sai


ya sanya qirjinsa mai qunci matsattse, kamar dai yana takawa1 ne cikin sama.” (Suratul An’am:


125).


1 Mai takawa zuwa sama kirjinsa kunci yake yi, saboda iskar numfashi tana raguwa gare shi, kamar yadda ilmin


Kimiyya ya tabbatar.


7


Tabbatar da Soyayyar Allah da Qaunarsa


ga Muminai masu Taqawa Gwargwadon


yadda ya Dace da Girmansa


A cikin faxin Allah, “Kuma ku kyautata; lalle ne, Allah yana son masu kyautatawa.”


(Suratul Baqara: 195). “Kuma ku daidaita.1 Lalle Allah na son masu daidaitawa.” (Suratul


Hujurat: 9). “To, matuqar sun tsaya sosai gare ku, sai ku tsayu sosai gare su. Lalle ne Allah yana


son masu taqawa.” (Suratut Tauba: 7). “Lalle ne, Allah yana son masu tuba, kuma yana son


masu tsarkakewa.” (Suratul Baqara: 222).


Da faxinsa, “Ka ce: Idan kun kasance kuna son Allah, to, ku bi ni, Allah ya so ku.”


(Suratu Aali Imrana: 31). Da faxinsa, “Lalle Allah yana son waxanda ke yin yaqi domin


xaukaka kalmarsa, a cikin safu kamar su gini ne mai xamfarar juna.” (Suratus Saff: 4). Da


faxinsa, “Kuma shi ne mai gafara, mai bayyana soyayya.” (Suratul Buruj: 14).


Tabbatar da sifantuwarsa, Maxaukaki,


da Rahama da Gafara


A cikin faxin Allah, “Da sunan Allah, mai rahama, mai jin qai.” (Suratul Fatiha: 1). Da


faxinsa, “Ya Ubangijinmu! Ka yalwaci dukan kome da rahama da ilmi.” (Suratu Gafir: 7). Da


faxinsa, “Kuma (Allah) ya kasance mai jin qai ga muminai.” (Suratul Ahzab: 43). Da faxinsa,


“Kuma rahamata, ta yalwaci dukan kome.” (Suratul A’araf: 156). Da faxinsa, “Ubangijinku ya


wajabta rahama ga kansa.” (Suratul An’am: 54). Da faxinsa, “Kuma shi ne mai gafara, mai jin


qai.” (Suratu Yunus: 107 da Suratul Ahqaf: 8). Da faxinsa, “Sai dai Allah ne mafificin masu


tsari, kuma shi ne mafi rahamar masu rahama.” (Suratu Yusuf: 64).


Bayanin Yardar Allah da Fushinsa da Qiyayyarsa


da cewa Shi mai Sifantuwa ne da haka


A cikin faxin Allah Maxaukaki, “Allah ya yarda da su, kuma sun yarda da shi.” (Suratul


Ma’ida: 119 da Suratut Tauba: 100 da Suratul Mujadala: 22 da Suratul Bayyina: 8). Da faxinsa,


“Kuma wanda ya kashe wani mumini da ganganci, to, sakamakonsa Jahannama, yana


madauwami a cikinta, kuma Allah ya yi fushi a kansa, kuma ya la’ane shi.” (Suratun Nisa: 93).


Da faxinsa, “Wannan domin, lalle su, sun bi abinda ya fusatar da Allah, kuma sun qi yardarsa.”


1 Daidaitawa a nan yana nufin sulhuntawa tsakanin masu sabani.


8


(Suratu Muhammad: 28). “Saboda haka a lokacin da suka husatar da mu, muka yi musu azabar


ramuwa.” (Suratuz Zukhruf: 55).


Da faxinsa, “Kuma amma Allah ya qi zaburarsu, sai ya nauyayar da zamansu.” (Suratut


Tauba: 46). Da faxinsa, “Ya girmama ga zama abin qyama a wurin Allah, ku faxi abinda ba ku


aikatawa.” (Suratus Saff: 3).


Bayanin Zuwan Allah domin


Rabe Hukunci tsakanin Bayinsa,


Gwargwadon yadda ya dace da Girmansa


A cikin faxin Allah, “Shin, suna jiran, face dai Allah ya je musu a cikin wasu inuwoyi na


girgije, da mala’iku, kuma an hukunta al’amarin?.” (Suratul Baqara: 210). Da faxinsa, “Shin,


suna jiran (wani abu), face dai mala’iku su je musu, ko kuwa Ubangijinka ya je, ko kuwa sashen


ayoyin Ubangijinka ya je.” (Suratul An’am: 158). Da faxinsa, “A’aha! Idan aka niqa qasa


niqewa sosai, kuma Ubangijinka ya zo, alhali mala’iku na jere, safu-safu.” (Suratul Fajr: 21-22).


Da faxinsa, “Kuma a ranar da sama take tsatssagewa tare da gizagizai, kuma a saukar da


mala’iku, saukarwa.” (Suratul Furqan: 25).


Tabbatar da Fuska ga Allah Maxaukaki


A cikin faxin Allah, “Kuma fuskar Ubangijinka, mai girman jalala da karimci, shi ne


yake wanzuwa.” (Suratur Rahman: 27). “Ko wane abu mai halaka ne face fuskarsa.” (Suratul


Qasas: 88).


Tabbatar da Hannaye Biyu ga Allah Maxaukaki


A cikin faxin Allah mai girma da xaukaka, “(Allah) ya ce: Ya Iblis! Me ya hana ka, ka yi


sujada ga abinda na halitta da hannayena biyu?” (Suratu S.: 75). “Kuma Yahudu suka ce:


Hannun Allah abin yi wa ququmi ne. An sanya hannuwansu a cikin ququmi! Kuma an la’ane su


saboda abinda suka faxa. A’a, hannuwansa biyu shimfixaxxu ne, yana ciyarwa yadda yake so.”


(Suratul Ma’ida: 64).


9


Tabbatar da Idanu Biyu Ga Allah Maxaukaki


A cikin faxin Allah, “Sai ka yi haquri da hukuncin Ubangijinka, lalle kai fa kana


idanunmu.” (Suratux Xur: 48). “Kuma muka xauke Nuhu a kan (jirgi) na alluna da qusoshi.


Tana gudana, a cikin kiyayewarmu, domin sakamako ga wanda aka yi wa kafirci.” (Suratul


Qamar: 13-14). “Kuma na jefa wani so daga gare ni a kanka. Kuma domin a riqe ka da kyau a


kan ganina.” (Suratu X.H.: 39).


Tabbatar da Ji da Gani ga Allah Maxaukaki


A cikin faxin Allah, “Lalle Allah ya ji maganar wadda ke yi maka jayayya game da


mijinta, tana kai qara ga Allah, kuma Allah na jin muhawararku. Lalle Allah mai ji ne, mai


gani.” (Suratul Mujadala: 1). Da faxinsa, “Lalle ne, haqiqa, Allah ya ji maganar waxanda suka


ce: Lalle ne, Allah faqiri ne, mu ne wadatattu.” (Suratu Aali Imrana: 181). Da faxinsa, “Ko suna


zaton lalle mu, ba mu jin asirinsu da ganawarsu? Na’am! Kuma Manzanninmu na tare da su suna


rubutawa.” (Suratuz Zukhruf: 80). “Kada ku ji tsoro. Lalle ni, ina tare da ku, ina ji, kuma ina


gani.” (Suratu X.H.: 46). “Ashe, bai sani ba cewa Allah yana gani.” (Suratul Alaq: 14). “Wanda


yake ganin ka a lokacin da kake tashi tsaye. Da jujjuyawarka a cikin masu yin sujada. Lalle shi,


shi ne mai ji, Masani.” (Suratush Shu’ara: 218-220). “Kuma ka ce: Ku yi aiki, sa’an nan Allah


zai ga aikinku, da Manzonsa da Muminai.” (Suratut Tauba: 105).


Tabbatar da Hila da Kaidi ga Allah Maxaukaki


Gwargwadon yadda ya dace da shi


A cikin faxin Allah, “Kuma (Allah) shi ne mai tsananin hila.” (Suratur Ra’ad: 13). Da


faxinsa, “Kuma (kafirai) suka yi makirci, Allah kuma ya yi musu (sakamakon) makircin, kuma


Allah ne mafi alherin masu saka wa makirci.” (Suratu Aali Imrana: 54). Da faxinsa, “Kuma suka


qullamakirci, kuma muka qulla sakamakon makirci, alhali su ba su sani ba.” (Suratun Namli:


50). Da faxinsa, “Lalle ne su, suna qulla kaidi na sosai, kuma ni, ina mayar da kaidi (gare su)


kamar yadda suke qulla kaidi.” (Suratux Xariq: 15-16).


Sifanta Allah da Rangwame da Gafara


da Rahama da Buwaya da Iko


A cikin faxin Allah, “Idan kun bayyana alheri, ko kuwa kuka voye shi, ko kuwa kuka


yafe laifi daga cuta, to, lalle ne Allah ya kasance mai yafewa, mai ikon yi.” (Suratun Nisa: 149).


“Kuma su yafe, kuma su kau da kai. Shin, ba ku son Allah ya gafarta muku, alhali Allah mai


10


gafara ne, mai jin qai.” (Suratun Nur: 22). Da faxinsa, “Alhali kuwa rinjaye ga Allah yake kuma


da Manzonsa, kuma da muminai.” (Suratul Munafiqun: 8). Da faxinsa dangane da Iblis: “(Iblis)


ya ce: To, ina rantsuwa da buwayarka, lalle ina vatar da su gaba xaya.” (Suratu S.: 82).


Tabbatar da Suna ga Allah da Kore Kama da Shi


A cikin faxin Allah, “Sunan Ubangijinka, mai girman jalala da karimci, ya tsarkaka.”


(Suratur Rahman: 78). Da faxinsa, “Sai ka bauta masa, kuma ka yi haquri ga bautarsa. Shin ka


san wani takwara gare shi?” (Suratu Maryam: 65). “Kuma babu xaya da ya kasance tamka gare


shi.” (Suratul Ikhlas: 4). Da faxinsa, “Saboda haka kada ku sanya wa Allah wasu kishiyoyi,


alhali kuwa kuna sani.” (Suratul Baqara: 22). “Kuma akwai daga mutane wanda yake riqon


kinaye, baicin Allah, suna son su, kamar son Allah.” (Suratul Baqara: 165).


Kore Abokin Tarayya ga barin Allah Maxaukaki


A cikin faxin Allah, “Kuma ka ce: Godiya ta tabbata ga Allah wanda bai riqi xa ba, kuma


abokin tarayya bai kasance a gare shi ba a cikin mulkinsa, kuma wani masoyi saboda wulakanci


bai kasance a gare shi ba. Kuma ka girmama shi, girmamawa.” (Suratul Isra: 111). “Abinda yake


a cikin sammai da wanda yake a cikin qasa suna tasbihi ga Allah. Gare shi mulki yake, kuma


gare shi godiya take. Kuma shi, a kan kome, mai ikon yi ne.” (Suratut Tagabun: 1).


Da faxinsa, “Albarka ta tabbata ga wanda ya saukar da (Littafi) mai rarrabewa a kan


Bawansa, domin ya kasance mai gargaxi ga halitta.” (Suratul Furqan: 1). “Wanda yake da


mulkin sammai da qasa, kuma bai riqi abin haihuwa ba, kuma abokin tarayya bai kasance a gare


shi ba a cikin mulkinsa, kuma ya halitta dukan kowane abu, sa’an nan ya qaddara shi


qaddarawa.” (Suratul Furqan: 2).


Da faxinsa, “Allah bai riqi wani abin haihuwa ba, kuma babu wani abin bautawa tare da


shi. Idan haka ne, (akwai abin bautawa tare da shi), lalle ne, da kowane abin bautawar ya tafi da


abinda ya halitta, kuma lalle ne, da waxansu sun rinjaya a kan waxansu. Tsarki ya tabbata ga


Allah, daga abinda suke siffantawa. Masanin voye da bayyane. Sa’an nan ya xaukaka daga barin


abinda suke yi na shirka.” (Suratul Muminun: 91-92).


Da faxinsa, “Sa’an nan kada ku bayar da waxansu misalai ga Allah. Lalle ne Allah yana


sani, kuma ku, ba ku sani ba.” (Suratun Nahal: 74). Da faxinsa, “Ka ce: Abin sani kawai,


Ubangijina ya hana abubuwan alfasha: abinda ya bayyana daga gare su da abinda ya voyu, da


zunubi da rarraba jama’a, ba da wani hakki ba, kuma da ku yi shirki da Allah ga abinda bai


saukar da wani dalili ba gare shi, kuma da ku faxi abinda ba ku sani ba, ga Allah.” (Suratul


A’araf: 33).


11


Tabbatar da Daidaitar Allah a kan Al’arshinsa


A cikin faxin Allah Maxaukaki, “Mai rahama, ya daidaita a kan Al’arshi.” (Suratu X.H.:


5) a wurare bakwai a cikin Alqur’ani. A cikin Suratul A’arafi ya ce, “Lalle ne Ubangijinku Allah


ne, wanda ya halitta sammai da qasa a cikin kwanaki shida, sa’an nan kuma ya daidaita a kan


Al’arshi.” (Suratul A’arafi: 54). Kuma ya ce a cikin Suratu Yunus (AS): “Lalle Allah ne


Ubangijinku wanda ya halicci sammai da qasa a cikin kwana shida, sa’an nan kuma ya daidaita a


kan Al’arshi.” (Suratu Yunus: 3).


A cikin Suratur Ra’ad kuma ya ce, “Allah shi ne wanda ya xaukaka sammai, ba da


ginshiqai ba waxanda kuke ganin su. Sa’an nan ya daidaita a kan Al’arshi.” (Suratur Ra’ad: 2).


Kuma a cikin Suratu X.H. ya ce, “Mai rahama ya daidaita a kan Al’arshi.” (Suratu X.H.: 5).


Haka nan a cikin Suratul Furqan ya ce, “Sa’an nan ya daidaita a kan Al’arshi, mai rahama.”


(Suratul Furqan: 59). Kuma a cikin Suratus Sajada ya ce, “Allah ne wanda ya halitta sammai da


qasa da abinda yake a tsakaninsu a cikin kwanuka shida, sa’n nan ya daidaita a kan Al’arshi.”


(Suratus Sajada: 4). Kuma ya ce a cikin Suratul Hadid: “Shi ne wanda ya halitta sammai da qasa


a cikin wasu kwanuka shida, sa’an nan ya daidaita a kan Al’arshi.” (Suratul Hadid: 4).


Tabbatar da Xaukakar Allah a bisa Halittunsa


A cikin faxin Allah, “A lokacin da Ubangiji ya ce: Ya Isa! Lalle ni mai karvar ranka ne,


kuma mai xaukake ka ne zuwa gare ni.” (Suratu Aali Imrana: 55). Da faxinsa, “Allah ya


xaukake shi zuwa gare shi.” (Suratun Nisa: 158). “Zuwa gare shi magana mai daxi ke hawa,


kuma aiki na qwarai yana xaukar sa.” (Suratu Faxir: 10).


Da faxinsa, “Kuma Fir’auna ya ce: Ya Hamana! Ka gina mini bene, xammanina za ni isa


ga qofofi. Qofofin sammai, domin in yi ninqaya zuwa ga abin bautawar Musa. Kuma lalle ni,


haqiqa, ina zaton sa maqaryaci.” (Suratu Gafir: 36-37). Da faxinsa, “Shin ko kun amince cewa


wanda ke cikin sama, ba zai iya shafe qasa tare da ku ba, sai ga ta tana mai girgiza? Ko kun


amince cewa wanda ke cikin sama ba zai iya sako muku iskar guguwa ba? To, za ku san yadda


(aqibar) gargaxina take.” (Suratul Mulk: 16-17).


Tabbatar da Kasancewar Allah Tare da Halittarsu


A cikin faxin Allah Maxaukaki, “Shi ne wanda ya halitta sammai da qasa a cikin wasu


kwanuka shida, sa’an nan ya daidaitu a kan Al’arshi, yana sanin abinda ke shiga cikin qasa da


abinda ke fita daga gare ta, da abinda ke sauka daga sama da abinda ke hawa cikinta, kuma shi


12


yana tare da ku, duk inda kuka kasance. Kuma Allah mai gani ne ga abinda kuke aikatawa.”


(Suratul Hadid: 4).


Da faxinsa, “Wata ganawa ta mutum uku ba za ta kasance ba face Allah shi ne na huxu


xinta, kuma babu ta mutum biyar face shi ne na shida xinta, kuma babu abinda ya kasa wannan


kuma babu abinda yake mafi yawa face shi yana tare da su duk inda suka kasance, sa’an nan ya


ba su labari game da abinda suka aikata a Ranar Qiyama. Lalle Allah masani ne ga dukan kome.”


(Suratul Mujadala: 7).


Da faxinsa, “Kada ka yi baqin ciki, lalle ne Allah yana tare da mu.” (Suratut Tauba: 40).


Da faxinsa, “(Allah) ya ce: Kada ku ji tsoro. Lalle ni, ina tare da ku, ina ji, kuma ina gani.”


(Suratu X.H.: 46). Da faxinsa, “Lalle Allah yana tare da waxanda suka yi taqawa da waxanda


suke su masu kyautatawa ne.” (Suratun Nahal: 128). Da faxinsa, “Kuma ku yi haquri. Lalle ne


Allah yana tare da masu haquri.” (Suratul Anfal: 46). Da faxinsa, “Da yawa qungiya kaxan ta


rinjayi wata qungiya mai yawa da izinin Allah, kuma Allah yana tare da masu haquri.” (Suratul


Baqara: 249).


Tabbatar da Magana ga Allah Maxaukaki


A cikin faxin Allah mai girma da xaukaka, “Kuma wane ne mafi gaskiya daga Allah ga


labari?” (Suratun Nisa: 87). Da faxinsa, “Wane ne mafi gaskiya daga Allah ga magana?”


(Suratun Nisa: 122). Da faxinsa, “Kuma lokacin da Allah ya ce: Ya Isa xan Maryama!” (Suratul


Ma’iada: 116). Da faxinsa, “Kuma kalmar Ubangijinka ta cika, tana gaskiya da adalci.” (Suratul


An’am: 115).


Da faxinsa, “Kuma Allah ya yi magana da Musa, magana sosai.” (Suratun Nisa: 164). Da


faxinsa, “Daga cikinsu akwai wanda Allah ya yi masa magana.” (Suratul Baqara: 253). Da


faxinsa, “Kuma a lokacin da Musa ya je ga miqatinmu, kuma Ubangijinsa ya yi masa magana.”


(Suratul A’araf: 143). Da faxinsa, “Kuma muka kira shi daga gefen dutse na dama, kuma muka


kusanta shi yana abokin ganawa.” (Suratu Maryam: 52). Da faxinsa, “Kuma a lokacin da


Ubangijinka ya kirayi Musa: Ka je wa mutanen nan azzalumai.” (Suratush Shu’ara: 10).


Da faxinsa, “Kuma Ubangijinsu ya kira su: Shin, ban hana ku ba daga waccan itaciya?”


(Suratul A’araf: 22). Da faxinsa, “Kuma ranar da ya kira su, sa’an nan ya ce: Mene ne kuka


karva wa Manzanni?” (Suratul Qasas: 65). Da faxinsa, “Idan wani daga mushirikai ya nemi


maqwabtakarka, to, ka ba shi maqwabtakar har ya ji maganar Allah.” (Suratut Tauba: 6). Da


faxinsa, “Alhali kuwa, haqiqa, wata qungiya daga gare su sun kasance suna jin maganar Allah,


sa’an nan kuma su karkatar da ita daga bayan sun gane ta, alhali su, suna sane.” (Suratul Baqara:


75). Da faxinsa, “Suna son su musanya maganar Allah ne. Ka ce: Ba za ku bi mu ba. Kamar


wannan ne Allah ya ce, a gabanin haka.” (Suratul Fathi: 15).


13


Da faxinsa Maxaukaki, “Ka karanta abinda aka yi wahayi zuwa gare ka, na littafin


Ubangijinka. Babu mai musanyawa ga kalmominsa.” (Suratul Kahaf: 27). Da faxinsa, “Lalle ne


wannan Alqur’ani yana gaya wa Bani Isra’ila mafi yawan abinda su suke sava wa junansu a


ciki.” (Suratun Namli: 76).


Tabbatar da Saukar da Alqur’ani


daga Allah Maxaukaki


A cikin faxin Allah mai girma da xaukaka, “Kuma wannan Littafi ne, mun saukar da shi,


mai albarka ne.” (Suratul An’am: 92 da 155). Da faxinsa, Da mun saukar da wannan Alqur’ani a


kan dutse, da lalle ka ga dutsen yana mai tawali’u, mai tsattsagewa saboda tsoron Allah.”


(Suratul Hashri: 21).


Da faxinsa, “Kuma idan muka musanya wata aya a matsayin wata aya, kuma Allah ne


mafi sani ga abinda yake saukarwa, sai su ce: Abin sani kawai, kai maqirqiri ne. A’a, mafi


yawansu ba sa sani. Ka ce: Ruhul Qudusi ne ya saukar da shi, daga Ubangijinka da gaskiya,


domin ya tabbatar da waxanda suka yi imani, kuma (domin) shiriya da bushara ga Musulmi.


Kuma lalle ne, haqiqa, muna sanin (cewa) lalle ne su, suna cewa: Abin sani kawai, wani mutum


ne yake karantar da shi. Harshen wanda suke karkatar da maganar zuwa gare shi, Ba’ajame ne,


kuma wannan (Alqur’ani) harshe ne Balarabe bayyananne.” (Suratun Nahali: 101-103).


Tabbatar da Ganin Muminai


ga Ubangijinsu Ranar Alqiyama


A cikin faxin Allah Maxaukaki, “Wasu fuskoki, a ranar nan, masu annuri ne. Zuwa ga


Ubangijinsu masu kallo ne.” (Suratul Qiyama: 22-23). “A kan Karagu, suna ta kallo.” (Suratul


Muxaffifin: 23). Da faxinsa, “Waxanda suka kyautata yi, suna da abu mai kyawu1 kuma da


qari.” (Suratu Yunus: 26). Da faxinsa, “Suna da abinda suke so a cikinta, kuma tare da mu akwai


qarin2 ni’ima.” (Suratu Q.: 35).


Irin bayanan da muka gabatar a sama suna da yawa a cikin Alqur’ani. Wanda ya yi


darasun Alqur’ani, tare da tunani, yana mai neman shiriya daga gare shi, tafarkin gaskiya zai


bayyana gare shi.


1 Hadisi ya fassara abu mai kyau da Aljanna, kari kuma shi ne ganin Ubangiji a cikin Aljannar.


2 Karin ni’ima shi ne ganin Ubangiji a cikin Aljanna.


14


Babi Na Biyu


Sunayen Allah da Sifofinsa a cikin


Hadisan Annabi (SAW)


Sa’an nan kuma sai Sunnar Manzon Allah (SAW), domin ita Sunna tana fassara


Alqur’ani kuma tana bayyana shi, kamar yadda take fayyace shi, tana shiryarwa zuwa gare shi.


Dukan sifofin da Manzo (SAW) ya sifanta Ubangijinsa, mai girma da xaukaka, da su a


cikin hadisai ingantattu waxanda masana suka yi na’am da su, ya wajaba a yi imani da su, kamar


Alqur’ani ba bambanci.


Daga cikinsu akwai:


Tabbatar Saukar Ubangiji zuwa Saman Duniya


Gwargwadon yadda ya Dace da Girmansa


A cikin faxin Manzon Allah (SAW), “Ubangijinmu yana sauka zuwa saman duniya a


kowane dare, a sulusin daren na qarshe. Sai ya ce: Wa zai roqe ni, in amsa masa? Wa zai


tambaye ni, in ba shi? Wa zai nemi gafarata, in gafarta masa?” (Bukhari da Muslim).


Tabbatar da cewa Allah yana Murna,


yana Dariya, yana Mamaki


A cikin faxin Manzon Allah (SAW), “Allah ya fi tsananin farin ciki da tuban bawansa


mumini mai tuba, daga xayanku da abin hawansa.”1 (Bukhari da Muslim). Da faxinsa, “Allah


yana dariya zuwa ga mutane biyu, waxanda xayansu yake kashe xaya, kuma duka su shiga


Aljanna.”2 (Bukhari da Muslim).


Da faxinsa, “Ubangijinmu yana mamaki da xebe qaunar bayinsa, alhali alherinsa yana


kusa. Yana duban ku, kuna cikin qunci, kuna xebe qauna, sai ya yi ta dariya, yana sane da cewa


buxinku yana kusa.” (Hadisi ne kyakkyawa).


1 Wannan dogon hadisi ne ya takaice shi. Hadisin yana buga misali da mutumin da abin hawansa dauke da


guzurinsa ya bata a daji. Ya fitar da rai da samunsa, kuma ya kusa mutuwa saboda kishirwa, sai ga abin hawan ya


gan shi. Allah ya fi murna da tuban bawansa daga murnar mai abin hawan nan da abin hawansa.


2 Dayan kafiri ne zai kashe Musulmi sai ya zama ya yi shahada. Sai daga baya shi kuma mai kisan ya musulunta, sai


shi ma ya shiga Aljanna.


15


Tabbatar da Qafa da Sawu


ga Allah Maxaukaki1


A cikin faxin Manzon Allah (SAW), “Jahannama ba za ta gushe ba, ana jefa (mutane) a


cikinta, tana cewa: Akwai qari? Har sai Ubangijin buwaya ya sanya qafarsa a cikinta (a wata


ruwayar, ya sanya sawunsa), sai sashenta ya motse zuwa sashe, sai ta ce: Ya isa! Ya isa!”


(Bukhari da Muslim).


Tabbatar da Kira da Sauti da Zance


ga Allah Maxaukaki


A cikin faxin Manzon Allah (SAW), “(Ubangiji) Maxaukaki yana cewa: Ya Adamu! Sai


y ace: Amsawarka! Amsawarka! Sai ya kira shi da sauti: Allah yana umarnin ka, ka fitar da wata


tawaga daga zuri’arka zuwa wuta.” (Bukhari da Muslim). Da faxinsa, :Babu xaya daga cikinku


face Ubangijinsa zai yi Magana das hi, babu mai tafinta tsakaninsu.”


Tabbatar da Xaukakar Allah


a bisa Halittarsa


da Daidaitarsa a bisa Al’arshinsa


A cikin faxin Manzon Allah (SAW) a cikin ruqiyya ga mara lafiya, “Ubangijinmu Allah


wanda yake cikin sama, sunanka ya tsarkaka. Umarninka yana cikin sama da qasa. Kamar yadda


rahamarka take cikin sama, ka sanya rahamarka cikin qasa. Ka gafarta mana kurakuranmu da


zunubanmu, kai ne Ubangijin muminai. Ka saukar da wata rahama daga rahamarka, da wata


waraka daga warakarka a kan wannan mara lafiya. Sai (mara lafiyar) ya warke.” (Hadisi ne


kyakkyawa. Abu Dawud da waninsa suka ruwaito shi).


Da faxin Manzo (SAW), “Ba za ku amince mini ba, alhali ni amintaccen wanda ke cikin


sama ne.” (Hadisi ne ingantacce). Da faxinsa, “Kuma Al’arshin yana kan ruwa, kuma Allah yana


kan Al’arshin, kuma yana sane da halin da kuke ciki.” (Hadisi ne kyakkyawa. Abu Dawud da


waninsa suka ruwaito shi). Da tambayarsa ga wata Baiwa, “Ina Allah yake? Ta ce: Cikin Sama.


Ya ce: Ni wane ne? Ta ce: Kai Manzon Allah ne. Sai ya ce (da ubangijin Baiwar): Enta ta; domin


hqiqa ita mumina ce.” (Muslim ya ruwaito shi).


1 Allah yana da kafa da sawu, saboda Annabi ya tabbatar da haka. Saboda haka, sai a yi imani da cewa yana da su.


Ba’a tawili ko a karkatar da ma’anarsu, amma kuma ba’a cewa takamaimai ga yadda suke. Sai dai ana imani cewa,


sun saba da na bayi; saboda Ubangiji halittu ba sa kama da shi.


16



Posts na kwanan nan

SAKO DAGA MUSULMI MAI ...

SAKO DAGA MUSULMI MAI WA'AZI ZUWA GA MUTUM KIRISTOCI

FALALAR AZUMIN KWANA ...

FALALAR AZUMIN KWANA SHIDA SHAWAL

TAKAITACCEN BAYANI MA ...

TAKAITACCEN BAYANI MAI ANFANI GA SABON SHIGA MUSULUNC

ZIKIRAI WADANDA AKE Y ...

ZIKIRAI WADANDA AKE YIN SU DA SAFE DA KUMA YAMMA