Labarai

gari suka kasa biyan bashin, sai a xebo wani abu daga cikin


zunuban wanda aka zaluntar a jibga wa azzalumin. Qarshe kuma a


iza qeyyarsa zuwa wuta.


b) Tauye Haqqin Ma’aikaci: Wasu uwayen gida kuma, xabi’arsu ita


ce, tauye haqqin ma’aikaci daga haqiqanin abin da aka yi


yarjejeniya da shi tun asali. Irin waxannan mutane na da


mummunan tanadi a wurin Allah Subhanahu Wa Ta’ala don Ya


ce:


Ma’ana:


“Bone ya tabbata ga masu tauye haqqi” (33:1).


Misalin wannan baqar xabi’a, shi ne abin da wasu masu hannu da


shuni kan yi na xauko ma’aikata daga garuruwansu na asali, su kawo su


birni da yarjejeniyar biyansu wani adadi na kuxi duk bayan wani


qayyadajjen Lokaci. Amma kuma da an fara tafiya, aiki ya fara nisa, ya


riga ya zarge wuyansu, sai ya lallava ya canza waccan yarjejeniya, ya


tauye haqqin nasu na asali. Su kuma saboda rashin makarkata ko wata


takamammar hujja a hannunsu, dole sai su haqura, a yi ta sha’ani wai an


cuci baqauye, in ji xan birni!. Iyakar abin da irin waxannan ma’aikata ke


iya yi shi ne; Allah Ya isa.


Babbar illar da ke cikin irin wannan nau’i na zalunci ita ce, idan


mai irin wannan xabi’a musulmi ne, to zai tozarta musulunci a idon irin


waxannan ma’aikata har ya cire masu sha’awar addini idan su ba


musulmi ba ne. Duk mai irin wannan xabi’a ya sani yana da zunubi a


wurin Allah.


83


c) Niqe ma’aikaci: Wasu uwayen gidan kuma, xabi’arsu ita ce niqe


ma’aikaci. Ta hanyar tsawaita lokacin aikin nasa, ko qara masa


wani aikin ba kuma tare da yayi masa wata ‘yar toliya ba a kan


jingayarsa ta asali (Over time).


d) Jinkirta Haqqin Ma’aikaci: Wasu uwayen gidan kuma, tasu xabi’ar


ita ce, jinkirta biyan haqqin ma’aikaci. Wani Lokacin ma sai


ma’aikacin ya yi kamar yana yi, ta hanyar faxi tashi, hargowa da


qorafi. Wani lokacin ma sai ya nemi ceton alqali. Manufar irin


waxannan mutane ita ce su gajiyar da ma’aikacin ya fita batun


haqqin nasa dole, su canye ko su juya shi ta hanyar Riba zuwa


wani lokaci, kafin su ba shi. Alhali kuwa irin waxannan ma’aikata


ba su da abin da za su aika wa iyalinsu da suka baro gida, suka


taho birni don nema masu abinci. Ba ma wannan ba, ko abin da za


su sayi abin karin kumallo kullum ba su da. Bone ya tabbata kan


irin waxannan azzalumai a shu’umar ranar nan mai zuwa!


Abu Hurairata ya riwaito cewa, Manzon Allah Sallallahu Alaihi


Wasallama ya ce: “Allah Ya ce: zan yi fito na fito da wasu mutane uku a


ranar qiyama: 1) Mutumin da ya rantse da sunana kuma ya sava, 2)


Mutumin da ya sayar da xa a matsayin bawa, ya kuma sa kuxin aljihu da,


3) Mutumin da ya sa wani aiki ya kuma qi biyansa jingarsa” (Bukhari).


RASHIN ADALCI TSAKANIN ‘YA’YA


Wani abu kuma da shari’ar musulumci ta haramta, kuma wasu


mutane suka yi biris da shi, shi ne Rashin Adalci tsakanin ‘ya’ya. Ta


hanyar ba wa wani daga cikinsu abin da basu ba wani ko saura ba.


Wanda hakan ke tabbatar da sun fifita shi a kan saura.


84


Wasu malamai nagartattu, na ganin cewa, idan mahaifi na da wani


qwaqqwaran dalili na yin haka, to babu haramci. Kamar xan da ya fifita


xin ya kasance ya kevantu da buqatar abin, saboda rashin lafiyar da yake


fama da ita, ko wani bashi da ake bin sa, ko ya yi masa kyautar ne a


matsayin goron qwazon hardace alqur’ani da ya yi, ko wani aiki da ya yi


qoqarin samar wa kansa. Ko saboda yawan iyalinsa, ko shagala da neman


karatu da ya yi. Ko dai wani dalili mai kama da waxannan.


Amma kuma duk da haka sun ce, ana so mahaifin ya qulla niyya a


ransa, ta ba wa wani daga cikin sauran ‘ya’yan irin wancan abu, a duk


lokacin da xaya daga cikin irin waxancan buqatoci suka kama shi. Domin


kuwa qa’idar ta asali ita ce abin da Allah Subhanahu Wa Ta’ala ke


cewa;


Ma’ana:


Ku yi adalci, shi ne mafi kusa ga taqawa (5:8)


Babban abin da ke tabbatar da rashin halaccin irin wannan xabi’a


shi ne, abin da Nu’umanu xan Bashiru Raliyallahu Anhu ya Riwaito daga


Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama bayan mahaifinsa ya taho da


shi wurin Manzon, inda shi mahaifin na Nu’umanu ya ce wa Manzon;


“Na ba wa xan nan nawa wani bawa da nake da shi”. Sai Manzon Allah


Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: Ina fatar ka ba wa gaba xayan


‘ya’yanka irinsa”. Ya karva masa da cewa: “A’a”. Daga nan sai Manzon


Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce masa:” To, ka fasa wannan


kyauta (Bukhari: 5/211).


A wata riwaya kuma ce masa Manzon Allah Sallallahu Alaihi


Wasallama ya yi; “Ka ji tsoron Allah ka kuma yi adalci tsakanin


85


‘ya’yanka”. Daga nan shi kuma sai ya je ya tayar da waccan kyauta.


(Fathul Bari 5/211). A wata riwaya ta uku kuma, cewa aka yi Manzon


Allah ya ce masa: “Kar ka nemi in zama shedunka a kan wannan kyauta.


Don ba zan zama sheda a kan zalunci ba” (Muslim: 3/1243).


Babu laifi a shari’a a ba wa xa namiji ninkin abin da aka ba wa


xiya mace, kamar yadda hukuncin gado yake, inji Imamu Ahmad


Rahimahullahu. (Abu Dawuda: 204).


Wannan ita ce qai’da ta shari’a. Amma sai ga shi a zamaninmu na


yau a wasu gidaje, saboda rashin tsoron Allah, uwaye maza na fifita wasu


‘ya’ya nasu a kan wasu a cikin kyauta. Sun kuma kasa gane cewa, irin


wannan banbanci da suke nunawa tsakanin ‘ya’yan na iya haifar da


hassada da qiyayya da gaba a tsakaninsu.


Wasu uwayen kan nuna irin wannan banbanci ne ta hanyar yi wa


wani daga cikin ‘ya’yan nasu wata kyauta, wai don kawai ya yi kama da


danginsa na wajen uba a halitta. Ya kuma ba wa wanda ya ya yi kama da


dangin uwarsa qasa ga abin da ya ba na farko. Ko kuma ya ba wa ‘ya’yan


wata mata fiye da abin da ya ba na wata. Ko ya xauki ‘ya’yan wata ya


saka makarantar kuxi, ya bar na saura a makarantun gwamnati. Wannan a


qarshe ko shakka babu qaiqayi zai koma wa masheqiya. Don za a wayi


gari a mafi yawan lokuta ‘ya’yan da ya tozarta su xauke shi ba bakin


komai ba, ko har ma can gaba idan Allah Ya xaukaka su, su ma su


walaqanta shi. Tabbas haka na iya faruwa, don Manzon Allah Sallallahu


Alaihi Wasallama ya ce: “Hala ba ku son su ma ‘ya’yan naku su girmama


ku?” (Ahmad; 4/269).


86


ROQO BA BUKATA


Sahlu xan Hanzalata Raliyallahu Anhu ya riwaito cewa, Manzon


Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Duk wanda ya roqi mutane


kuxi alhali yana da abin da ke isar sa buqata, to yana roqar ma kansa


garwashin wuta ne kawai”. Sai sahabbai suka tambayi Manzon; “Mene


ne miqidarin abin da za a ce ya ishi mutum buqata har ya hana shi roqon


qari? Sai ya karva masu da cewa: “Idan ya mallaki abin da zai ci abincin


rana da na dare” (Abu dawuda: 2/281).


Haka kuma xan mas’udu Raliyallahu Anhu ya riwaito cewa,


Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Duk wanda ke roqon


mutane kuxi alhali yana da abinda ke isar sa biyan buqata, zai tashi Ranar


qiyama fuskarsa da farxe- farxe” (Ahmad; 1/388).


Duk da irin wannan tanadi da shari’ah ta yi wa mai roqo ba da


wata buqata ba. Wasu mutane a yau, sun sami sandar roqe-roqe har ma a


masallaci. Inda zasu je su dami mutanen da ke sallah da salati babu li


babu la. Su kan yi haka ne kuma ta hanyar shimfixa koke- koke na qarya.


Wasu daga cikin su ma har takardun qarya suke yawo da su a masallatan


sana damun mutane da dogon turanci. Wasu kuma iyalansu suke


rarrabawa a masallatan don gudanar da wannan mugunyar sana’a. Ba su


wannan masallaci ba su wancan. Alhali kuwa wasu daga cikinsu Allah ne


kawai ya san iyakar abin da suka mallaka. Sai kuwa idan sun mutu, a yi


ta jin sun bar kaza sun bar kaza. Alhali a lokacin da suke waxancan roqeroqe


suna rufe damar wasu mutane ne, da ba su mallaki komai ba, amma


tsoron Allah da tsaron mutunci sun hana su fitowa su roqa. Mutane kuma


zaton suke yi sun wadata. Qarshe sai a xauki abin da ya kamata a ba su a


ba waxannan jeqaqqin.


87


TURUN BASHI


Haqqin wani a hannun wani nada matuqar girma a wurin Allah. Ta


yadda har ta kai da mutum zai tava wani haqqi na Allah, ya kuma tuba,


Allah na iya yafe masa. Amma da zai tava haqqin wani mutum


xan’uwansa dole ne ya mayar masa da shi kafin ranar da Naira da Kobo


ba su da wani tasiri face kyakkawan aikin mutum.


Allah Ta’ala ba ya yafe wa wani haqqin wani. Saboda haka Yace:





Ma’ana:


Haqiqa Allah Yana umurnin ku ku bayar da amanoni


zuwa ga masu su (4:58).


Yawan cin bashi ba da niyyar biya ba, na xaya daga cikin


matsalolin da suka zama ruwan dare a cikin al’ummarmu a yau. Irin


wannan bashi ma wasu kan karve shi ba don suna da wata buqata ta gari


ba. Sai don kawai su faxaxa sana’o’insu, ko don su yi takarar sayen


motocin shiga ko kayan alatu ko wasu qyale-qyalin rayuwa da wasu


takwarorinsu. Wasu sukan mallaki irin waxannan kayayaki ne, ta hanyar


qulla yarjejeniyar biyansu kaxan – kaxan. A qarshe kuma sai su qare


cikin haramiya dumu- dumu.


Irin wannan xabi’a ta cin bashi a kai- akai ba kuma da niyyar biya


ba, na sa wasu mutane zama turayen bashi, wanda kuma qarshe yakan


haifar da talauci da kariyar arziqi. Don kauce wa faxawa cikin irin


wannan matsala ne, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya


gargaxi Al’umarsa da cewa: “Duk wanda ya karvi kuxin mutane a


matsayin bashi, da niyyar biya Allah zai ba shi ikon biya, amma wanda


88


ya karva ba da niyyar biya ba sai don ya kaxas, Allah zai kaxas da shi’


(Bukhari: 5/54).


Da yawan mutane a yau sun xauki wannan matsala ba bakin komai


ba. Alhali kuwa babbar matsala ce a wurin Allah. Wadda har ta kai ko


shahidi, tattare da irin ladar da yake da ita, ba za a yafe masa bashin


mutane da ke kansa ba. Tabbacin wannan magana shi ne hadisin da ke


cewa: “Tsarki ya tabbata ga Allah. Don bai sanya wani tsanani a cikin


addini ba, sai a cikin sha’anin bashi. Ina rantsuwa da wanda raina yake


hannunsa, da za a kashe mutum a wurin yaqi, a raya shi a kuma sake


kashe shi, a kuma sake raya shi a kuma sake kashe shi, to ba zai shiga


aljanna ba matuqar ana bin sa bashi, sai an biya shi. (Nasa’i: 7/314).


Ya kamata duk wanda ke irin wannan xabi’a ya tuba, kafin wuri ya


qure masa.


CIN DUKIYAR HARAM


Da yawa mutanen da tsoron Allah ya yi wa kaxan a zukata, ba su


damu da ta ko wace hanya za su sami kuxi ba, balle wadda za su kasha


su a cikin ta. Abin da kawai ya dame su, shi ne yadda ajiyarsu ta banki za


ta qara kauri, koda ta hanyar haramiya ce.


Saboda cika wannan guri, sai su shiga wawure kuxaxen bayin


Allah da suke amana a hannun su. Wasu kuma su kama ‘yan sace-sace ko


fashi da makami ko damfara ko haramtattar sana’a kamar Riba, ko cin


kuxin marayu, ko bokanci. Waxansu kuma sukan kama ‘yan


tabanjamanci ko waqa, ko tatsar taskar musulmi, ko tava kayan mutane,


ko yaudararsu ta hanyar karvar kayan da qarfi, ko tsawwala wa kayan da


suke sayarwa farashi. A yayin da wasu kuma ke tsira sana’ar baracebarace


ba da wani dalili ba. Ga su nan dai.


89


Da kuxin da waxannan mutane suka samu ta waxannan hanyoyi za


su sayi abinci ko tufafi da ababen hawa, ko su gina gidaje, ko su kama


haya, wasu ma har su sayi kayan alatu su zuba a gidajen. Alhali kuwa


Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: Duk tsokar jikin da ta


ginu da haramun wuta ce mafi cancanta da ita” (Xabarani: 19/136).


Kafin haka kuma a Ranar qiyama, Allah zai tambayi ko wane


mutum a kan yadda ya sami dukiyarsa da yadda ya kashe ta. Ta haka sai


kowa ya haxu da sakamakonsa daidai da aikinsa.


Da wannan muke kiran duk wanda ya san cewa akwai wata dukiya


hannunsa ta haram ya yi gaggawar rabuwa da ita, ya mayar wa mai ita


idan ya san shi, ya kuma nemi gafarar Allah. Kafin Ranar da kuxi ba su


da wani amfani sai dai aikin qwarai.


SHAN BARASA


Allah Maxaukakin Sarki na cewa a cikin Littafinsa mai tsaki:


Ma’ana:


Ya ku waxanda suka yi Imani! Haqiqa giya da caca da reful


da kiban quri’a, duk qazanta ce kawai daga cikin aikin


shaixan, sai ku nisance ta wa la’alla ku ce nasara” (5:90).


Wannan umurni da Buwayayyen Sarki Ya bayar na nisantar


waxannan abubuwa, da suka haxa da shan Giya, Babban dalili ne da ke


tabbatar da kasancewar gaba xayan haram. Kuma kawo giya da Sarkin ya


90


yi tare da gumaka, kafaxa- da kafaxa ya tabbatar cewa, ita ma haramun


ce.


Haka kuma Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya qara


tabbatar da haramcin shan giya, a wani hadisi da Jabir ya riwaito, inda ya


ce: “Allah Ya yi alkawalin shayar da duk wanda ya sha giya dagwalon


khibal. Sahabbai suka ce, “Ya Manzon Allah mene ne dagwalon khibal?


Sai ya ce: zufan ‘yan wuta ko rowan qurajensu! (Muslim: 3/1587). Haka


kuma xan Abbas ya riwaito cewa, Manzon Allah Sallallahu Alaihi


Wasallama ya ce: “Duk wanda ya mutu yana mashayi, zai haxu da Allah


a matsayin mai bautar gumaka” (Xabarani 12/45).


Yawan sunayen giya da banbancin kamfunan da suka sana’anta ta


ba zai tada ita daga haramci ba. Daman dai Manzon Allah Sallallahu


Alaihi Wasallama ya ce: “Wasu mutane daga cikin al’ummata zasu sha


giya suna kiran ta da wani suna” (Ahmad: 5/352). Kiranta da sunan


“Tsime” da “Burkutu” da makamanta su idan ya zama da nufin yaudara


to, mashayan ne ke yaudarar kansu. Kamar yadda Allah ya ce:


Ma’ana:


Suna (tunanin sun) yaudari Allah da waxanda suka yi imani,


alhali ba su yaudarar kowa sai kan su, kuma ba su


sakankancewa!” (2:9)


Shari’ar musulunci ta yi matuqar xaukar mataki a kan wannan


matsala ta giya da shan ta. Ta kuma warware zare da abawarta don kada


wani kokwanto ko tantama su shiga ga mutum a kai. Dubi abin da


Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ke cewa: “Duk abin da ke sa


maye giya ne, kuma ko wace irin giya haramun ce” (muslim: 3/1587).


91


Ka ga kenan wannan magana ta ma’aiki ta gama tabbatar mana da


cewa, duk abin da ke dagula hankali da tunani idan an sha shi to giya ne,


komai qanqantarsa. Kuma ko da an bashi sunaye daban daban, komai


yawansu dai, giya ce. Hukuncinta ko sananne ne.


A qarshe ma dai Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya


gaya wa mashaya giya farar gaskiya mai xaci, inda ya ce: “Duk wanda ya


sha giya har ta bugar da shi, ba za a karvi sallarsa ba har kwana arba’in.


Idan kuma ya mutu a cikin wannan hali makomarsa ita ce wuta. Idan


kuma ya tuba Allah zai gafarta masa. In ya koma sha har ya yi maye,


kuma za a sake qin karvar sallarsa ta kwana arba’in. Idan kuma ya mutu a


wannan hali, wannan karon ma wuta ya yi. Amma idan aka yi sa’a ya


tuba to, Allah zai yafe masa. Haka kuma da zai sake sha ya kuma sake


buguwa, karo na uku, nan ma za a ba sallarsa baya har tsawon kwana


arba’in. Da kuma zai kwanta dama a wannan hali, ba abin da zai hana shi


shiga wuta. Da kuma zai tuba Allah zai karvi tubansa.


Amma da zai sake sha karo na huxu to, Allah Ya yi alkawalin


shayar da shi dagwalon khibal a Ranar qiyama. Sahabbai suka ce: Ya


Manzon Allah, mene ne dagwalon khibal? Ya ce: “Shi ne surkamin ‘yan


wuta” (Ibn majah: 3377).


AMFANI DA KASAKEN ZINARI DA AZURFA


Da yawa ka kan samu kasake da kwanoni na zinari ko azurfa, ko


waxanda aka yi wa ado da xayansu a gidajen masu hannu da shuni. Daxa


a manyan hotel- hotel nan ne uwa uba.


Irin waxannan kasake da ake qawatawa da wasu zane zane sun


yawaita a wasu qasashe na musulmi, saboda amfani da su da ake yi a


matsayin kyautuka na masamman. Wasu mutane da Allah bai ba ikon


92


mallakar irin waxannan kayayyaki a gidajensu ba, sai ka taras sun faxa


cikin wannan haramiya don za a gayyace su wasu gidaje don wata


hidima, qarshe a kawo masu abinci cikin irinsu.


Amfani da irin waxannan kayayyaki a irin waxannan hanyoyi


haramun ne a musulunci. Saboda haka ne Manzon Allah Sallallahu


Alaihi Wasallama ya gargaxi dukan musulmi daga amfani da su. Ummu


Salamata ta riwaito Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama na cewa:


“Duk wanda ke ci ko shan wani abu a cikin kaskon zinari ko azurfa yana


jefa garwashin wuta ne a cikin cikinsa” (Muslim: 3/1634).


Wannan haramci ya shafi duk wani nau’i na ababen amfani da aka


qera da zinari ko azurfa. Kamar Farantai, cokula masu yatsu, da marasa


yatsu, wuqaqe, tire- tire da makamantan su. Haka kuma ‘yan adikokin


alawa, irin waxanda ake bayarwa a matsayin kyautar alfarma ga baqi ko


amare da angwaye. Duk amfani da irin waxannan abubuwa haramun ne,


matuqar da zinari ko azurfa aka qera su.


Wasu mutane na iya cewa “To har da mu da ke kwalliya da su


kawai a cikin gilasai, abin ya shafa?” Eh, lalle ya shafe ku. Abin da kuke


yi xin nan bai halasta ba. Domin kuwa idan dai ana yalla ido a gan su, to


lalle wata rana sai an yi amfani da su. Malam Bin Baz ne ya faxi haka.


SHEDAR ZUR


Allah maxaukakin Sarki Ya ce:


Ma’ana:


93


Saboda haka ku nisanci qazantar gumaka, kuma ku nisanci


Zhedar Zur. Kuna masu tsayuwa ga gaskiya domin Allah, ba


masu yin shirka da Shi ba” (22:30-31).


Haka kuma Abdurrahaman xan Abubakar Raliyallahu Anhu ya


riwaito cewa, mahaifinsa ya ce: Wata rana muna zaune tare da Manzon


Allah Sallallahu Alaihi Wasallama sai ya ce : Kuna so in ba ku labarin


manya- manyan zunubbai? Ya ko maimaita tambayar har sau uku.


Sa’annan ya amsa masu da cewa: 1) haxa Allah da wani a cikin bauta, 2)


qin uwaye… Manzon Allah yana gincire sai ya tashi zaune. Sannan ya


ce: 3) Da kuma Shedar Zur. Mai riwayar (Sayyidina Abubakar) ya ce,


Annabi ya yi ta maimaita na ukun nan har muka yi sauraren ya dasa aya.”


(Bukhari: 5/261)


Gargaxi da jan kunnen mutane a kan su nisanci Shedar Zur abu ne


da shari’a ta faxa ta maimaita ta kuma nanata, saboda irin yadda mutane


ba su xauki yin hakan bakin komai ba. Duk da yake kuma an fahimci


cewa qiyayya da gaba ne kan sa wasu mutane faxa wa wannan haramiya


don fashe haushinsu akan wani wanda suke adawa da shi. Amma kuma


hakan ba ya zama hujja gare su. Musamman idan aka yi la’akari da irin


mummunan sakamakon da tagarar ke haifarwa wanda ya haxa da; i) Sa


mutane da yawa hasarar wasu haqqoqa nasu, ii) jefa wasu mutane da


yawa cikin baqar musiba ba su ji ba su gani ba, iii) share wa wasu mutane


da yawa hanyar samu da mallakar abin da ba su cancanta ba. Da


sauransu.


Wani babban misalin da ke tabbatar da irin yadda mutane ba su


xauki Shedar Zur bakin komai ba shi ne abin da kan faru a wasu


kotunanmu a yau. Nan take wani zai ce wa wani “Zo ka shede ni, ni


kuma in shede ka”. Alhali kuwa a wannan lokacin ne suka fara haxuwa.


94


Ka ga kenan ko wanensu zai shedi xaya a kan abin da bai san


komai game da shi ba, balle ya iya bayanin yadda ya faru dalla dalla.


Wato kamar ya shede shi a kan mallakar wani fili ko gida, ko ya wanke


shi daga wani bashi, alhali bai ko tava ganinshi ba kafin yau a kotu.


Turqashi!


Wannan ita ce tantagaryar qarya da Shedar Zur. Domin kuwa


Allah Subhanahu Wa Ta’ala cewa ya yi a yi sheda a kan abin da aka


sani:


Ma’ana:


Kuma bamu yi sheda ba face da abin da muka sani. Kuma bamu


kasance masu kiyaye aibi ba. (12:38)


SAURAREN KIXA


Kaxe- kaxe da waqe- waqe a idon shari’ar musulunci na xauke


hankalin masu yin su da sauraren su ne kawai daga tafarkin Allah


Subhanahu Wa Ta’ala zuwa ga na shexan. A kan haka ne xan Mas’udu


Raliyallahu Anhu yake rantsuwa da Allah Subhanahu Wa Ta’ala kan


cewa ayar nan da ke cewa:


Ma’ana:


Kuma daga cikin mutane akwai wanda ke sayen tatsuniyoyi


domin ya vatar da mutane daga hanyar Allah” (31;6).


95


Ya ce, wannan ayar tana magana ne a kan waqe- waqe. Haka kuma


Abu Amiru da Abu Maliki al- Ash’ari Raliyallahu Anhuma sun qarfafa


haramcin kixa da saurarensa, da hadisin da Manzon Allah Sallallahu


Alaihi Wasallama ke cewa a cikinsa: “Za a samu wasu mutane a cikin


al’ummata da ke halasta zina da tufafin al-Hariri da giya da kaxe-kaxe”


(Bukhari 10/51). Haka kuma Anas Raliyallahu Anhu ya riwaito cewa,


Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Nan gaba za a sami


girgizar qasa da aman duwatsu da shafe mutane su koma dabbobi a cikin


al’ummata, sakamakon fara shan giya da sauraren waqe-waqen mata da


kaxe-kaxen da za ayi” (Silsilah Sahiha 2203).


Ka ga kai tsaye Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya


haramta kaxe-kaxe. Sai kuma bushe bushe irin na kusumburwa da Siriqi


da sarewa duka sabgogi ne na bayyana qasaitar sarakuna da kambama su,


amma dai ba shari’a ce ta zo da su ba. Sannan kuma malamai magabata


irin su Imamu Ahmad Rahimahullahu Sun bayyana cewa, kayayyakin


kaxe kaxe da bushe bushe, irin su garaya da Goge da Molo da kwamsa da


duk masu kama da su, sun shiga cikin wannan harantawa da Manzon


Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya yi. Saboda mummunan tasirin da


suke da shi ya ma fi na duk wasu kayan kixa da ake amfani da su a


zamanin duhun kai, waxanda anka ambata a cikin wasu hadisai. Kai!


Yadda wasu ma daga cikin su ke sa maye da annashawa ko giya albarka.


Kamar yadda malamai irin su Ibnul Qayyim suka faxa.


Wannan haramci na qara tsanani da qamari lokacin da aka haxa


waxannan kaxe kaxe da bushe bushe da goge goge, da muryoyin mata


mawaqa. Uwa uba kuma idan waqoqin da suke yi xin suka qunshi


kalaman bege da soyayya da qauna, da siffanta kyawon halitta. A irin


haka malamai sun ce waqoqin na matuqar haramta, saboda suna share


96


hanya ne zuwa ga alfasha. Suna kuma tsirar da munafucci a cikin zukata.


A taqaice dai, kaxe- kaxe da waqe- waqe na daga cikin manya- manyan


abubuwan da ke sa mutane na kutsa kai ga varnace varnace. Kuma ga shi


raba mutane da su na da matuqar wahala saboda ci gaban zamani ya


sakaxa su cikin abubuwan amfani da dama kamar Agogayyen hannu,


qararrawar qofa, kayan wasan yara, Na’urori masu qwaqwalwa da Tarhotarho


da sauransu. Amma kuma kar a manta haramun ne. Allah Ya agaje


mu.


TSEGUMI


Giba ko tsegumi na nufin yin maganar wani musulmi a kan wani


abu da ba ya so a ji, ko da kuwa abin gaskiya ne. Wataqila abin ya shafi


halittar jikinsa ne, ko irin riqonsa da addini, ko rayuwarsa ta yau da


kullum, ko xabiunsa. Haka kuma tattauna wasu kurakurai na wani, ko


kwaikwayon wata xabi’a tashi don a yi dariya duk na iya zama Giba.


Mafi yawan majalisu da wuraren haxuwar jama’a a yau sun zama


dandalin tsegunguma da cin naman mutane, da keta alfarmar musulmi.


Irin wannan xabi’a ko, na daga cikin abubuwan da Allah Subhanahu Wa


Ta’ala Ya haramta ga bayinsa, ta hanyar kwatanta masu ita da wani abin


da ko wace rayuwa ke qyama. Ya ce;


Ma’ana:


Kuma kada sashenku ya yi tsegumin sashe. Shin xayanku na


son ya ci naman xan’uwansa yana matacce? Ba za ku so ba.


Kuma ku ji tsoron Allah. (49:12)


97


Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya fito wa musulmi da


tantagaryar abin da wannan aya ke qoqarin cewa, akan haramcin


tsegumi, inda ya ce wa Sahabbai: “Ko kun san abin da ake ce wa Giba


(tsegumi)? Suka karva masa da cewa: “Allah da Manzonsa ne kawai suka


sani”. Sai ya ce, Giba ita ce ka tsegunta wani abu a kan xan’uwanka,


wanda kuma ba ya son a ji”. Sai kuma Sahabban suka sake tambayarsa da


cewa: To, me kake gani da abin da aka faxa a kansa gaskiya ne? Sai ya ce


masu: Idan abin da aka faxa a kansa gaskiya ne a lokacin giba ta tabbata.


Idan kuwa ba gaskiya ba ne ya zama qazafi kenan”. (Muslim: 4/2001).


Mutane, musamman a yau, sun yi biris da wannan lamari, sun


xauki Giba ba bakin komai ba. Alhali kuwa abu ce mai tsananin girma da


haxari a wurin Allah kamar yadda Manzon Allah Sallallahu Alaihi


Wasallama ya bayyana, cewa: “Riba nau’i Saba’in da biyu ce. Mafi


qarancin zunubi daga cikinsu ita ce, wadda zunubinta ke daidai da na


wanda ya yi jima’i da mahaifiyarsa. Mafi girmanta kuma ita ce wadda


zunubinta ke daidai da na keta rigar mutuncin xan’uwa musulmi (cin


namansa)” (Silsilah Sahiha: 1871).


Maganin wannan kuwa shi ne, kada mutum ya yi. Idan kuma yana


zaune da mutane, suka sa faifan wani; suna sara da sassaqa to, ya yi


qoqarin ba shi kariya mai tsafta. Manzon Allah Sallallahu Alaihi


Wasallama ya umurci Musulmi da yin haka inda yake cewa: “Duk wanda


ya rufa wa xan’uwansa musulmi asiri, Allah zai tsare fuskarsa daga shiga


wuta Ranar Qiyama” (Ahmad: 6/450).


GULMA


Gulma ita ce safa da marwa a tsakanin mutane, ana jekadancin


maganganun sashen su zuwa ga sashe, da nufin tayar da wata fitina da


98


haifar da qiyayya da gaba a tsakaninsu. Wannan xabi’a haramun ce.


Kuma Allah Subhanahu Wa Ta’ala Ya la’anci waxanda duk ke yin ta.


Ya ce:


Ma’ana:


Kada ka bi duk mai yawan rantsuwa, walakantacce. Mai


zunxe, mai yawo da gulma. (69:10-11).


Haka kuma Huzaifata ya riwaito cewa, Manzon Allah Sallallahu


Alaihi Wasallama ya ce: “Duk wanda ke yawo da gulma ba ya shiga


aljanna” (Bukhari: 10/472).


Haka kuma xan Abbas ya ce: “Wata rana Manzon Allah Sallallahu


Alaihi Wasallama ya wuce kusa da wata maqabarta a Madina sai ya ji


hargowar wasu mutane biyu, ana yi masu azaba a cikin qaburburansu. Sai


ya ce: Ai ana yi masu azaba ne, amma ba don wani babban zunubi ba.


Kai! Amma fa ko laifukan nasu manya ne. Saboda xayansu ba ya tsalki


idan ya gama bauli. Xayan kuma yana yawo ne da gulma” (Bukhari


1/317).


Wannan kenan. To kuma mafi munin Gulma duk bata fi wadda


zata haifar da matsala tsakanin mata da miji ba. Ko wadda za a tsegunta


wa wani maigida abin da ma’aikatansa ke cewa, don a haifar da wata


qullalliya tsakaninsu.


Gaba xayan waxannan xabi’u da ire-irensu haramun ne. Kuma


nisantar su ya zama wajibi.


KWARMATO


Allah maxaukakin Sarki na cewa:


Ma’ana:


Ya ku waxanda suka yi imani! Kada ku shiga gidajen da ba


gidajenku ba, sai kun sami izini, kuma kuna yi wa masu su


sallama” (24: 27).


Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya warware zare da


abawar wannan aya, da ya bayyana cewa an wajabta wa musulmi neman


izni ne, kafin ya shiga gidan da ba nasa ba, don kada ya ga wani abin da


ba a so ya gani. Manzon yace: “An gindaya neman izni ne don a kange


gani” (Bukhari: 11/24).


Wannan mugunyar xabi’a ta kwarmato, ta zama ruwan dare


tsakanin jama’a a waxannan kwanuka namu. Musamman idan gidajen


mutane na kusa da juna ko ma suna xafe ta yadda qofofi da tagoginsu ke


fuskantar juna. Sai ka taras maqwabta na amfani da wannan dama suna


leqen cikin gidajen maqwabtansu a kai a kai, maimakon su riqa kau da


kansu. A yayin da waxansu kuma da ke kan tudu kan mayar da leqen


gidajen maqwabtansu da ke kware abin yi da gangan ta hanyar tagoginsu


ko wani abu mai kama da haka. Ko Shakka babu wannan cin amana ne,


kuma wuce iyaka ne a cikin haqqin da maqwabci ke da shi na walwala


(privacy). Kuma wata hanya ce da ke zama sanadiyyar faruwar wasu


abubuwa na haram masu yawa. A kan haka ne shari’ah ta xauki idon mai


kwarmato ba bakin komai ba. Manzon Allah Sallallahu Alaihi


Wasallama ya ce: “Duk wanda ya leqa gidan wasu ba tare da izninsu ba,


to ya halatta gare su su soke idaniyarsa xaya” (Muslim 3/1699).


100


A wata ruwayar ma cewa ya yi : “Su soke idaniyarsa, kuma ba


diyya ba qisasi” (Ahmad: 2/385).


WARIYA


Wariya a nan na nufin kevancewar mutane biyu daga cikin uku


don wata tattaunawa ta asiri. Wannan xabi’a ta zama kamar ado a cikin


mutane alhali kuwa wata hanya ce da shaixan kan bi, ya raba kan


musulmi, har a wayi gari wasu na qyamar wasu.


Wannan xabi’a haramun ce a shari’a, kuma Manzon Allah


Sallallahu Alaihi Wasallama ya bayyana irin hikimar da ke cikin


haramcin ta da cewa, idan kuna ku uku, kada biyu su ware suna ganawa


su bar xaya. Su bari har sai sun yawaita. Don kada xayan ya samu


damuwa” (Bukhari: 11/83).


Sannan kuma wannan hukunci bai taqaita ga mutane biyu kawai


ba. Ba ya halatta ko mutane uku su ware su bar xaya, na huxunsu, tilo.


Haka haka. Abin da Shari’a ta haramta a nan a taqaice shi ne, warewa a


bar mutum xaya, komai ko yawan waxanda suka ware xin. Haka kuma


haramun ne mutane biyu su canza harshe suna magana da wani yare da


na ukunsu ba ya fahimta. Domin ko shakka babu hakan zai sa ya ji ya


tozarta. Kuma duk wanda kenan zai fahimci sun yi haka ne don su cuta


masa a zuci, da sauransu.


JAN WANDO A QAS


Kalmar “Isbal” kalma ce ta Larabci wadda ke nufin sa wando dogo


har ya wuce idon sau. Mutane a yau ba su xauki wannan xabi’a bakin


komai ba. Alhali kuwa komai ce a wurin Allah. Domin kuwa Manzon


Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce, a wani hadisi da Abu zarri ya


101


riwaito: “Mutane uku Allah ba zai haxa baki da su ba gobe qiyama. Kai!


Ko kallon rahama ba zai yi masu ba, balle Ya tsirar da su. Za su tabbata


cikin azaba mai raxaxi. i) Wanda wandonsa ke wuce idon sawunsa, ii)


wanda ke yi wa mutane gori da, iii) Wanda ke rantsuwa a kan qarya idan


zai sayar da wani abu” (Muslim: 1/102).


An sami wasu mutane a yau da, idan aka yi masu tanbihi a kan


wannan xabi’a sai su ce; Ai ba don wani alfahari ko taqama na sa


wandona har ya wuce idon sau ba”. To, wannan Magana riya ce a


kaikaice. Kuma ba karvavviya ba ce. Haramcin sanya wando har ya wuce


idon sau, abu ne da ya haxe kowa. Wanda ya yi a kan fankama da


alfahari da wanda bai yi a kan haka ba. Domin kuwa cewa Manzon Allah


Sallallahu Alaihi Wasallama ya yi: “Duk abin da ya gota idon sau na


wando rabon wuta ne” (Ahmad: 6/254).


Wannan shi ne hukuncin wanda ya yi Isbal ba don wata fankama


da feshi ba. Kuma wanda ya yi haka Saboda girman kai da feshi da


fankama, hukuncinsa ya fi tsanani. Don cewa Manzon Allah Sallallahu


Alaihi Wasallama ya yi: “Duk wanda ya zuba tufafinsa har suka ja qasa


saboda girman kai, Allah ba zai dube shi da ijiyar rahama ba ranar


qiyama (Bukhari: 3465).


Shari’ar ta tsananta hukunci ne a kan wannan saboda haxa hancin


laifi biyu da ya yi a lokaci xaya, kuma a cikin mas’ala xaya wato zuba


tufafi su wuce idon sau da kuma alfahari.


Kar ka yi mamakin shigowar “tufafi’ a cikin wannan magana


domin xan Umar Raliyallahu Anhu ya riwaito cewa: “Isbal” na iya


tabbata ta hanyar gyafto (wando) ko riga ko rawani. Kuma duk wanda ya


wuce iyaka da xayansu saboda alfahari da girman kai, Allah ba zai dube


shi da ijiyar rahama ba a ranar qiyama. (Abu Dawuda: 4/353).


102


Amma kuma shari’ah ta yi rangwame ga mata, su tsawaita


tufafinsu da misalin kamu xaya ko biyu, don gudun iska ya kaxa a hangi


wani abu na jikinsu. Amma ba ya halatta su wuce haka. Kamar yadda


wasunsu kan yi musamman a tufafin bukukuwansu na aure, waxanda


keda doguwar geza a baya. Ta yadda har sai abokan amarya sun kama


mata ita, ta baya.


QAWA DA ZINARI GA MAZA


Abu Musal Ash’ari Raliyallahu Anhu ya riwaito cewa Manzon


Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Qawa da Siliki da zinari ta


mata ce daga cikin al’ummata. Amma an haramta su ga maza


(Ahmad:4/393).


Kasuwanninmu a yau cike suke da abubuwan amfani na maza,


kamar: Agogayyen Hannu, da Tabarau, da Aninai, da Alqalumma da


makamantansu, da aka qera da zinari mai daraja daban-daban, ko kuma


aka yave qarfen na asali da shi. Agogayen hannu a yau su ne maza suka


fi gasa da juna a cikin mallakarsu duk kuwa da kasancewarsu na zinari.


Xan Abbas Raliyallahu Anhu ya riwaito cewa, Manzon Allah


Sallallahu Alaihi Wasallama ya ga wani namiji sanye da zoben zinari,


nan take ya karve shi ya kuma yi jifa da shi, ya ce; “Ko akwai wani daga


cikinku da zai iya xaukar garwashin wuta ya liqa ga hannunsa? (Yana


nufin duk namijin da ya sanya zoben zinari kamar ya xauki garwashin


wuta ne ya liqa a hannunsa) Da Manzon ya bayar da baya, sai wasu suka


ba wancan mutumin shawarar ya xauki zobensa mana, ya ci gaba da


amfani da shi (ta hanyar sayarwa ya amfana da kuxin) shi ko ya ce


faufau, Wallahi tunda Manzon Allah ya karve shi ya yas ba ni ba shi


(Muslim; 3/1655).


103


TSIRAICI


Wata hanya da maqiyan Musulunci ke bi suna kawo mana hareharen


ba zata a cikin siga ta zamani, ita ce hanyar qirqire-qirqiren salailai


daban-daban na kayan ado ta fuskar xinke-xinke, waxanda kullu yaumin


suke canza wa sanfari da sunan yayi, waxanda kuma aka wari gari sun


sami mutaqar karvuwa a qasashenmu na musulumi.


Irin waxannan kaya ba sa rufe komai na jikin mace. Saboda


kasancewarsu qanqana, Shar-shar kuma tani tani. Ta yadda bai kamata


macen da ta san kunya ta saka su ko gaban mace ‘yar’uwarta, ko wani


muharraminta ba. Balle wanda ba su ba. Amma kuma Alhamdu lillahi, da


ma Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya riga ya faxa mana irin


haka za ta bayyana ga matan qarshen zamani. A wani hadisi da Abu


Harairata Raliyallahu Anhu ya riwaito:”Akwai wani nau’i biyu na


mutanen ‘yan wuta da za su bayyana can gaba: i) Wasu mutane da ke


yawo da wasu manyan buloli masu kama da wutsan sanuwa sana bugun


mutane da su, da ii) Wasu mata masu tafiya kamar tsirara suna kakkarya


jiki, kansu kamar tozayen raqumma, a karkace. Da su da aljanna faufau.


Kai ! ko qanshinta ba za su ji ba. Duk da yake ko wanda ke nisan wuri


kaza da kaza yana jin sa (Muslim; 3/1680)


Irin waxannan mata, da dabi’unsu sun bayyana kamar yadda


Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ambata, babu abin da ya


rage mana illa mu nisance su.


Haka kuma irin waxannan tufafi na tsiraici sun haxa da irin


dogayen rigunan da mata ke sakawa a yau masu tsage-tsage, da wasu


yaggwai can qasa, ga su kuma da faxin. Ta yadda da macce ta zauna


al’aurarta za ta bayyana a fili. Na farko kenan. Ga shi kuma ta yi koyi da


104


kafirai, don su aka sani da irin waxannan kaya masu nuna tsiraici. Muna


roqon Allah ya kiyashe mu.


Wasu tufafin Kuma da su ma, saka su tsiranci ne, ko da sun rufe


jiki, su ne waxanda ke da miyagun hotunan da suka haxa da kamar:


Hotunan Mawaqa da Nigogi (‘yan rawa), da kwalaben giya da hotunan


dabbobi masu rai. Waxanda dukansu haramun ne a musulunci. Wasu


kuma na xauke ne da hoton kuros ko Tamburran qungiyoyin asiri, ko dai


wasu miyagun kalamai da ba su dace da duk wani mutum mai muruwa


ba. Duk da yake wani lokacin muninsu ba zai bayyana ga waxanda ke


sanye da kayan ba. Saboda an yi rubutun ne da wani yare na mutanen


qetare.


SAJIN GASHI (Atacimen)


A idon Shari’ar musulunci, duk macen da za ta sadar da gashin kanta


na asali da wanda ba na asali ba, daxa na kanta ne, ko wanda aka yanko


daga jikin wata dabba kai tsaye kamar doki, to ta yi al-gussu. Algussu


kuwa haramun ne.


Asma’u ‘yar Abubakar Raliyallahu Anha ta ce: “Wata mata ta zo


wurin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ta ce, Ya Manzon


Allah, akwai wata ‘ya tawa da zan wanke jibi. Amma kafin yau ta yi


wani xan zazzavi har gashin kanta ya zuba. Ko ina iya yi mata sajin


gashi?’ Ya karva mata da cewa: A’a. Allah Ya la’anci duk wadda ta yi


Sajin gashi da wadda aka yi ma shi (Muslim: 3/1676).


Haka kuma Jabiru xan Abudullahi ya ce: “Manzon Allah


Sallallahu Alaihi Wasallama ya hana mace ta yi sajin wani abu ga kanta


(Muslim: 3/1679).


105


A bisa dalilin waxannan hadisai, duk wani nau’i na sajin gashi da


ake yi a yau a gidajen gyaran gashi na mata, ko wane irin nau’i ne, to


haramun ne. Haka kuma hulunan gashi da wasu taurarin ‘yan wasa ke


amfani da su a finafinai rashin tarbiyya ne, kuma haramun ne.


HARKAR ‘YAN DAUDU


Namiji ya yi qoqarin komawa mace, ko mace ta yi qoqarin


komawa namiji ta hanyar kwaikwayon xabi’un juna, mummunar xabi’a


ce a idon shari’ar musulunci.


A xabi’ance ma kamata ya yi namiji ya yi ta tattali da qoqarin


tabbata namiji. Ita ma mace, ta yi nata tattali da qoqarin na tabbata mace.


Don wannan shi ne abin da Allah Subhanahu Wa Ta’ala Ya shirya


kowanen su a kai asalatan. Kuma qoqarin sava wa wannan tsari nasa na


sa nagartattar rayuwa ta ‘yan adamtaka ta yi wuya a bayan qasa. Domin


hakan zai sa amon rayuwar jama’a ya xauki wani salo irin na hatsin bara,


wato wake-wake a komai.


Irin wannan xabi’a haramun ce. Dalili kuwa shi ne, a tsarin shari’ar


musulunci, duk abin da aka ce Allah Ta’ala ko Manzonsa ya la’anci mai


shi, to ya zama haramun ke nan.


Xan Abbas Raliyallahu Anhu ya riwaito cewa Manzon Allah


Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Allah Ya la’anci Maza masu


kwaikwayon mata. Ya kuma la’anci mata masu kwaikwayon maza


(Bukhari: 10/332). Haka kuma xan Abbas xin ya riwaito wani hadisin da


Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ke cewa a cikinsa: “Allah Ya


la’anci mata maza, da maza mata (Bukhari: 10/333)


“Kama” da waxannan hadisai ke ta Magana, na iya kasancewa ta


fuskar kwaikwayon kai da komowa, magana da tafiya. Haka kuma


106


hadisan na tabbatar mana da cewa haramun ne xayan jinsunan nan biyu


ya yi kama da xan uwansa, ta hanyar saka duk wani abu da, a xabi’a xaya


jinsin aka sani da shi.


A kan haka haramun ne namiji ya xaura Sarqar wuya, ko ta hannu,


ko ta qafa, ko ‘yan kunne da sauransu, kamar yadda fitsararru ke yi a


Turai. Haka kuma haramun ne mace ta yi amfani da duk wani abu da a


xabi’a na maza ne, kamar: Riguna da Jallabiyoyi, da sauransu. Abin da


ma aka fi buqata a cikin ko wace al’umma shi ne tufafin mata ya sava da


na maza kwatakwata. Domin Abu Hurairata ya riwaito wani hadisi da


Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ke cewa a cikinsa: “Allah Ya


la’anci namijin da ke sa kayan maza, da macen da ke sa kayan mata (Abu


Dawuda: 4/355).


BUDURWAR ZUCIYA


Buduruwar Zuciya a wannan babi, na nufin duk wani yunquri da


wanda shekarunsa suka miqa zai yi don canza wata halittar Haliqu a


jikinsa kamar hurhura, ta hanyar yi mata baqar garura, don ya koma layin


matasa.


Nagartaccen ra’ayi na malaman Sunnah ya tafi a kan cewa, irin


wannan Sabga haramun ce. Saboda wani nau’i ne na Al-gussu. Kuma an


dace da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya hani musulmi


xabi’ar a cikin wani hadisi da ke cewa: “Za a yi wasu mutane a qarshen


zamani da za su riqa ture farin gashinsu da baqar garura har ya riqa


walqiya kamar gaban baqar tantabara. To, ko qanshin aljanna ba za su ji


ba. (Abu Dawuda).


Irin wannan sabga ta yawaita matuqa ga mutanen da Allah


Subhanahu Wa Ta’ala Ya yi wa ni’imar farin gashi tun suna da qurciya


ko waxanda mutuwa ta fara barbaxa wa gishiri. Wanda hakan ke


107


yaudarar mutane, ta hanyar mayar da tsoho yaro ko kuma tsohuwa ta


koma yarinya. Ka ga an mayar da gaskiya qarya kenan.


Ba tura farin gashi ya koma wata kala ne haramun a shari’ar


musulunci ba. A’a, ture shi ya koma baqi ne haramun. Saboda ai, ta


tabbata Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama na shafa wa farin


gashinsa lalle, ya koma ja- ja- ja ko qasa –qasa. Abin ma bai tsaya ga shi


ya yi wa kansa ba, har umurni ya yi da haka. Don a lokacin da aka ci


garin Makka da yaqi, aka zo da Abu quhafata (Mahaifin Halifa


Abubakar) don su gaisa. Ya ga gemu da sajensa irin na dattijai, ya yi fari


kamar auduga sai Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Ku suturta


wannan farin gashi da yi masa turi. Amma kada ku sa baqi


(Muslim:3/1663).


Wannan hukunci na haramcin ture gashi ya koma baqi, ya haxa


maza da mata. Amma su ma, suna iya yin wata kalar.


ADO DA HOTUNAN ABU MAI RAI


Abdullahi xan Mas’udu Raliyallahu Anhu ya riwaito cewa,


Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Mutanen da za su


haxu da azaba mafi tsanani Ranar qiyama su ne masu sassaqa gumaka


(Bukhari: 10/382).


Haka kuma Abu Harairata ya riwaito cewa, Manzon Allah


Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Allah Ta’ala Ya ce, “Babu wanda ya


kai shisshigin wanda ke qoqarin yin halitta irin tawa. In gaskiya ne ya


halitta gero da alkama mu gani (Bukhari: 10/385). Kuma xan Abbas


Raliyallahu Anhu ya ce wani hadisi da ya karvo daga Manzon Allah


Sallallahu Alaihi Wasallama: “Za a saka wa ko wane gunki da mutum ya


sassaqa rai daga ran wanda ya sassaqa shi, a yi ta azabtar da shi a cikin


108


wutar Jahannama”. Ya kuma qara da cewa: “Wanda ko duk sassaqa ta


zamo sana’arsa, to, ya tsaya ga sassaqa itace, ko wani abu maras rai”


(Muslim: 3/1671).


Ka ga kai tsaye, waxannan hadisai, sun haramta sassaqa hotuna ko


zana su ko xaukar hoton su matuqar dai na ababe masu rai ne.


Tunda kuwa haka ne, ya zama wajibi a kan duk wani musulmi na


qwarai ya karvi wannan hukunci da shari’ah ta yi da hannu biyu- biyu, ba


tare da wata jayayya ba. Duk da yake wasu na iya kafa hujja da cewa,


“Eh! To ai, mu ba bauta wa waxannan hotuna muke yi ba, don ba sujada


muke yi musu ba”.


Amma kuma duk mai hankalin da ya dubi wannan matsala da idon


basira zai tsinkayo tare da fahimtar irin hikimar da haramta irin


waxannan abubuwa ta qunsa. Saboda mafi yawan ayyukan fitsara na


faruwa ne ta hanyar hotuna. Musamman zinace-zinace. Domin ta hanyar


kallace-kallacen hotunan banza ne qwazaba ke toroqo da bululluqai, daga


nan har a kai ga varna.


Bisa wannan dalili ne ma, mala’ikun rahama ke qaurace wa duk


wani gida da ake ajiye hotuna a cikinsa. Kamar yadda Manzon Allah


Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Mala’ikun Rahama ba su shiga duk


wani gida da ke akwai kare a cikinsa ko hotuna (Bukhari: 10/380).


Wani abin mamaki da xaure kai shi ne, duk da wannan haramci,


mutane a yau musamman masu hannu da shuni, ba su fasa aje gumakan


wasu dabbobi ba, kai har da na mutane, a cikin gidajensu da sunan qawa


ko ado. Alhali kuwa akwai wasu mutane da ke bauta wa wasu daga cikin


waxannan abubuwa.


To, haramcin abubuwa irin waxannan ya fi qamari da tsanani.


Sannan sauran hotunan da ake ratayewa na mutane da wasu dabbobi na bi


109


masu. Qarshe kuma waxanda ba rataye su ake yi ba suna bi masu a


haranci. Domin da yawa Sukan sa waxanda suka aje su, girmama su, da


sabunta juyayi da jimami a cikin zukatansu. Duk da yake wasu mutane


kan kafa hujja da cewa Suna aje hotunan mutanen ne, da suka haxa da na


uwayensu ko shugabanni ko malamansu, ko masoyansu ko wasu gwaraje


da suke ganin bajintar su ko suke sha’awarsu, don tunawa da su. Alhali


kuwa ita tunawa da wani abu a zuciya ake yin ta. Ba sai da hoto ko


mutum mutumi ba. Kuma mafi kyawon tunawa da mutum, bayan ya


qaura, ita ce, idan ya faxo a zuciyar wani nasa, to ya yi masa kyakkyawar


addu’a, ta hanyar roqa masa gafara da Rahamar Allah Subhanahu Wa


Ta’ala.


Saboda haka, babu wani musulmi da ke da wani uzuri na aje wani


hoto a xakinsa ko liqa shi a jikin bango ko abin hawansa. Lalle ne ya yi


waje da duk wani hoto ko mutum mutumi na mutum ko dabba da ke


gidansa. Sai fa idan hakan ta gagara. Balle kuwa ba zata gagara ba.


Hotuna irin waxanda ke jikin gwangwanaye da kwalayen abinci,


waxanda ba makawa sai musulmi sun yi ta’amuli da su, ko waxanda ke


cikin wasu littafai na karatu. Ana so mutum ya yi iyakar qoqarinsa na


ganin ba su zame masa allaqaqai ba.


Babu laifi idan an aje hotuna irin waxanda babu makawa sai an aje


su, kamar waxanda ake maqalawa ga takardun shedar qare karatu ko


katin sheda, ko lasisi, ko irin waxanda ke saqe a kan dardumai.


Allah Subhanahu Wa Ta’ala na cewa:


Sai ku bi Allah da taqawa gwargwadon abin da kuka


sami iko: (64:16).


110


QARYAR MAFARKI


Da gangan wasu mutane ke qirqira mafarki, har su ce sun ga wani


abu a cikinsa, don kawai neman girma a idon mutane ko wani abin


duniya, alhali qarya suke yi ba su ga komai ba. Kai! Ko mafarkin ma ba


su yi ba. A yayin da wasu mutanen kuma kan yi haka ne don su tsorata


wasu magabata da ke masu barazana ko wani abu mai kama da haka.


Irin waxannan qaryace-qaryace kan yaudari hankalin mutane,


saboda rashin isassar wayewa da cikakken Ilimi, da kuma imanin da suke


da shi ga mafarki.


Wannan xabi’a na xaya daga cikin xabi’un da shari’ar musulunci ta


haramta. Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Mafi


girman qarya ita ce danganta mutum ga wanda ba mahaifinsa ba. Ko


iqirarin ganin wani abu (a cikin mafarki) a kan qarya. Ko a jingina wa


Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama abin da bai ce ba (Bukhari:


6/540).


Haka kuma ya ce: “Duk wanda ya yi qaryar ya yi mafarkin wani


abu alhalin bai yi ba za a titasta masa xaure ‘ya’yan sha’ir biyu. Ba kuma


zai iya ba (Bukhari: 12/427).


Xaure qwayar sha’ir biyu wuri xaya abu ne da baya yiwuwa.


Kamar yadda wancan mafarki da aka yi qaryar yi bai kasance ba.


TOZARTA QABURBURA


Abu Hurairata Raliyallahu Anhu ya riwaito cewa, Manzon Allah


Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Da xayanku zai zauna a kan


garwashin wuta, har ya ruru ya qone tufafinsa, ya kai ga fatar jikinsa, ya


fi alheri gare shi bisa ga ya zauna a kan qabari (Muslim: 2/667).


111


Kafin zama a kan qabari ma, wasu mutane nada xabi’ar tattakawa


da yin tafiya a kansa, ba tare da wata damuwa ba. Musamman a lokacin


da aka tafi maqabarta don nufe wani. Wasu ma har da takalmi a


qafafunsu. Haka za su bi qaburburan da ke maqwabtaka da wanda suka


kai, suna tattaki a kai, ba kunya ba tsoron Allah, balle su tuna da wata


alfarma da mamatan da ke kwance wurin ke da. Alhali kuwa wannan


matsala mai matuqar nauyi ce. Musamman idan aka yi la’akari da faxar


Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama da ya ce: “Da zan yi tattaki a


kan garwashi ko kaifin takobi, ko in wanke takalmina da xayan qafata, ya


fi soyuwa gare ni bisa ga in yi tattaki a kan qabarin wani musulmi (Ibnu


majah: 1/499).


Wannan kenan. To ina ga waxanda ke yankar filin maqabarta su


gina gidaje ko shaguna? Wasu mutanen ma saboda tsananin rashin kirki


da taskai, har bayan gari sukan yi a cikin maqabarta, suna damun bayin


Allah da ke kwance wurin da qazanta. Irin waxannan mutane na


fuskantar babban haxari. Domin kuwa Manzon Allah Sallallahu Alaihi


Wasallama ya ce: “Wanda ke biyan buqatarsa a cikin maqabarta daidai


yake da wanda ke biyan ta a cikin tsakiyar kasuwa (Wato asirinsa a tone


yake).


Haka kuma wannan gargaxi da kashedi ya haxa har da waxanda ke


zubar da shara a cikin maqabarta. Ta hanyar amfani da damar kasancewar


bangayen maqabartun sun zube, ko an daina amfani da su. Duk irin halin


da maqabarta take ciki, haramun ne a yi mata irin wannan tozarci.


Kai! Har waxanda ke zuwa ziyara a maqabartu wajibi ne su cire


takalminsu, matuqar dai za su ratsa qaburburan da ke ciki.


RAGGON TSARKI


112


Karantar da xan Adamu kowace irin tagara da za ta sa ya ci gaba


da zama mutum kammalalle, na daga cikin abubuwan da addinin


Musulunci ke alfahari da su. Don babu wani addini ko tsarin rayuwa da


ya riga shi a wannan fagen.


Yin cikakken bankwana da qazantar fitsari ko gayaxi a lokacin da


suka fita daga jikin mutum, ta hanyar wankewa da ruwa ko hoge tas-tas


tas, na xaya daga cikin waxannan darussa. Amma kuma mutane da dama


sun yi biris da wannan koyarwa ta musulunci. A inda suke sakaci har


jikinsu da tufafinsu su yi kace-kace da xayan wannan najasa. Ta yadda ko


sun yi sallah Allah ba zai karva ba. A qarshe kuma su taras da azaba a


cikin qaburburansu. Kamar yadda xan Abbas ya riwaito cewa: “Manzon


Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya wuce ta wata maqabarta a garin


Madina sai ya ji qarar wasu mutane biyu ana yi masu azaba a cikin


qaburburansu. Sai ya ce: “Ana azabtar da su ne, ba don wani babban laifi


ba. Kai! Babban laifi ne shi ma: Xayan dai ba ya tsabtaci al’aurarsa da


kyau idan ya yi fitsari. Xaya kuma ba ya da aiki sai yawo da tsegumi


(Bukhari: 1/317).


Akwai ma hadisin da Manzon Allah ke cewa a ciki: “Mafi yawan


azabar qabari a kan fitsari take (Ahmad: 2/326).


Abubuwan da kan haddasa irin wannan matsala ta rashin samun


cikakken tsarki, sun haxa da: i) Gaggawa a gama, ii) Tsugunawa Wuri


Mai Tsauri, iii) Rashin damuwa da wankewa da kyau.


Wata babbar matsala kuma da ke taka gagarumar rawa a wannan


hauji, ita ce irin yadda muka yi nisa matuqa a cikin kwaikwayon al’adun


Turawa. An wayi gari wasu wuraren da muke fitsari a yau irin na Turawa


ne, da ake xafawa a bango kuma a fili. Ta yadda ma duk wanda zai wuce


yana ganin wani abu na tsiraicin wanda ke biyan buqata a wurin.


113


Ka ga irin waxannan mutane laifinsu ya zama biyu kenan, ga


qazanta ga tsiraici.


TSINCE


Allah maxaukakin Sarki Ya ce:


Ma’ana:


Kuma kada ku yi leqen asirin (‘yan uwanku) (49:12)


Xan Abbas Raliyallahu Anhu ya riwaito cewa, Manzon Allah


Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Duk wanda ya tsinci maganar da


wasu mutane ke yi, ba tare da sun sani ba, za a zuba ruwan narkakkar


darma a kunnuwansa ranar qiyama (Xabarani: 11/248-249)


Idan wanda ya yi irin wannan haramtaccen aiki, ya yi ne da nufin


kai wannan magana da ya tsinta a wani wurin, don ya tayar da wata wuta,


to, Gummi ta haxu da Anka kenan; ga laifin tsince, ga kuma


annamimanci. Wannan mutum ya tave domin kuwa Manzon Allah


Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Annamimi (mai tsince don ya haxa


faxa) ba ya shiga aljanna (Bukhari: 10/472).


CUTAR DA MAQWABCI


Haqqin maqwabci a kan maqwabcinsa abu ne mai girma a wurin


Allah Subhanahu Wa Ta’ala. Saboda haka ne Sarkin ya haramta cutarwa


a tsakaninsu. Inda ya ce:


114


Ma’ana:


Kuma ku bauta wa Allah, kuma kada ku haxa wani da shi,


kuma ku kyautata ma mahaifa. Kuma ku kyautata ga


ma‘abuta zumunta da marayu da matalauta, da maqwabci


na kus da na nesa, da aboki na gefe, da xan hanya, da abin


da hannuwanku na dama suka mallaka. Haqiqa Allah ba ya


son wanda ya kasance mai taqama, mai yawan Alfahari


(4:36)


Haka kuma, Abu Shuraihu Raliyallahu Anhu ya riwaito cewa


Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Wallahi ba ya da


imani, wallahi ba ya da imani, wallahi ba ya da imani. Sahabbai Suka ce:


waye shi ya Manzon Allah? Ya ce : Wanda maqwabcinsa ba ya tsere wa


sharrinsa. (Bukhari: 10/443)


Matsayin maqwabci a wurin maqwabci abu ne mai matuqar girma.


Wanda har ta kai Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya sa


maqwabci shi ne ma’aunin gane kirki ko rashin kirkin mutum.


Xan Mas’udu ya riwaito cewa, wani mutum ya ce wa Manzon


Allah Sallallahu Alaihi Wasallama, ya Manzon Allah, ya zan yi in gane


kirki ko rashin kirkina? Sai Ma’aki ya ce masa: “Duk lokacin da ka ji


maqwabtanka na cewa kana da kirki, to, kana da shi. Idan kuwa ka ji


suna cewa ba ka da shi, to, lalle ba ka da shi xin”. (Ahmad: 1/402)


115


Cutar da maqwabci na iya tabbata ta fuskoki da dama. Duk wanda


ya hana maqwabcinsa jingina wani katakon runfa ga bangon da ya raba


su, suke kuma da haqqi gaba xaya a cikinsa, ko ya faxaxa nasa gini, ta


yadda xayan zai sami qarancin hasken rana ko iska, ba kuma tare da


izinin xayan ba. Ko ya fasa, ko buxe tagoginsa ta yadda zai riqa leqen


gidan xayan. Yadda ba wani abu na asiri da za a iya yi a xaya gidan sai


bisa idonsa. ko ya dinga damunsa da kaxe-kaxe a kan fayafan garmaho,


ko hargowa, musamman a lokacin da yake baccin dare ko na rana, ko ya


xauki sabgar jibge shara a qofar gidan xayan. Duk wanda ke yi wa


maqwabcinsa xayan waxannan xabi’u, to, ya cutar da shi matuqa. Daxa


balle tava iyalinsa ko dukiyarsa Manzon Allah Sallallahu Alaihi


Wasallama na cewa: “Da mutum zai yi zina da mace goma can nesa, ya


fi sauqi gare shi, bisa ga ya yi da matar maqwabcinsa. Da kuma zai fasa


wasu gidaje goma can nesa, ya fi sauqi gare shi bisa ga ya fasa gidan


maqwabcinsa (Bukhari:103).


Bone ya tabbata ga mutanen da ke da xabi’ar amfani da damar


waxansu maqwauta nasu da basu kasancewa gida da dare don yanayin


aikinsu, sai su faxa gidajensu su aikata varna. Ranar qiyama sun shiga


uku.


TAUSHE HAQQIN MARAYU


Yana daga cikin dokokin shari’ar musulunci cewa, yana da


matuqar kyau mutum ya yi qoqari iyakar zarafi ya yi haqurin cutarwar da


xan’uwansa zai yi masa. Na farko kenan. Kuma haramun ne shi ya zama


farkon wanda zai yi cutar.


Taushe haqqin maraya, wani zalunci ne da cutarwa, wanda kuma


shari’a ta haramta. Abu ne mai sauqin gaske wanda za a gada ya taushe


116


haqqin wasu daga cikin magadansa, tun kafin ya mutu. Wannan na


faruwa idan ya yi amfani da sauran nunfashinsa a duniya, ya rubuta wata


wasiyya a kan abin da zai bari na dukiya. A irin wannan dama ce wasu


kan taushe haqqen wasu marayu ta hanyar kore su daga cikin magadansu


na haqiqa. Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya yi gargaxi da


babbar murya ga duk mai irin wannan hali, da ya ce: “Duk wanda ya


cutar da wani Allah zai musguna masa, duk kuma wanda ya tsananta wa


wani Allah zai tsananta masa (Ahmad: 3/453).


Wata hanyar kuma da mutum ke iya karva sunan mai taushe


haqqin marayu ita ce, a wasiyyarsa ya ware wa wani magadi, fiye da abin


da shari’ah ta yanka masa ko ya yi wasici da ba wa wani mutum fiye da


kashi xaya bisa uku na dukiyarsa.


Irin wannan matsala ma nada ‘yar dama a qasashen da musulunci


ke jagoranci. A qasashen da ko ba dokokin shari’ar musulunci ne ake


aiwatarwa ba, da yawa ake samun irin waxannan matsaloli. Kuma ko sun


faru babu yadda magadi zai yi ya karvi haqqinsa wanda Allah Ya shata


masa. Domin dokokin da kutunan da za a iya kai kuka gare su, ke


aiwatarwa, na iya xaure wa irin wannan zalunci gindi, musamman idan


da hannun wani lauya a ciki. Ga shi ko Allah Ta’ala ya ce:


Ma’ana:


Bone ya tabbata gare su daga abin da hannayensu ke


rubutawa, kuma bone ya tabbata gare su daga abin da suke


sana’antawa (2:79).


117


DARA


Dara da Ludo da Karta da Diraf da makamantansu, na duk wata


wasa, da ake dibilwa da hannu da qwaqwalwa don fitar da gwani a cikin


ta, haramun ne a musulunci. Dalili kuwa shi ne, dukansu qofofi ne da ke


kai masu wasannin zuwa ga caca. Saboda haka ne Manzon Allah


Sallallahu Alaihi Wasallama ya yi mana ahir da su ya ce: “Duk wanda ke


Dara daidai yake da wanda ya cava hannunsa cikin naman alade ko


jininsa (Muslim: 4/394).


Haka kuma Abu musa Raliyallahu Anhu ya riwaito cewa, Manzon


Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Duk wanda ke Dara, ya sava


wa Allah da Manzonsa (Ahmad: 4/394).


LA’ANTAR MUSULMI


Mutane da yawa kan kasa ja wa halshensu lizzami lokacin da suka


fuskanta. A sakamakon haka sai nan- da nan su furta kalmomin la’anta ga


wasu mutane, ko dabbobi, ko sandararrun abubuwa. Wasu ma har


kwanaki da awoyi suke la’anta. Da makamantansu. Kai! Saboda tsananin


shaqawa da rashin taskai ma, wasu har kawukansu, ko ‘ya’yansu sukan


la’anta. Wasu ma’aura kuma kan la’anci juna lokaci xaya, ko lokuta


daban-daban.


Wannan matsala nada matuqar girma a idon shari’ah. Saboda haka


ta haramta ta. Kuma Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce, a


wani hadisi da Abu zaidi Sabitu xan Dhahhaku ya riwaito cewa: “Duk


wanda ya La’anci mumini, to zunubinsa daidai yake da na wanda ya


kashe shi (Bukhari: 10/465).


118


Al’adance, irin wannan xabi’a ta la’ance- la’ance, ta fi yawaita a


bakunan mata a cikin ko wace al’umma. Saboda haka Manzon Allah


Sallallahu Alaihi Wasallama ya bayyana cewa wannan xabi’a ce zata


kasance dalilin shigar mafi wayansu wuta. Kuma su, da duk wanda ke


irin wannan sabga, basu cikin waxanda zai ceto ranar qiyama.


Wani babban haxari ma duk bai fi kasancewar la’antar duk da


mutum ya yi ba bisa qa’ida ba, zata dawo kansa. Daxa kome kuwa ya


la’anta. Kaga kenan qaiqayi ya koma kan masheqiya. Da haka kuma


mutum ya nisanta kansa daga rahamar Allah.


KUKAN MUTUWA


Kukan mutuwa ta hanyar hargowa da kururuwa, da faxuwa ana


tashi, yagar fuska da keta tufafin da ke jiki, kamar an yi sabuwar hauka,


abu ne da shari’ar musulunci ta haramta.


Mata su suka fi yin irin wannnan mugunyar xabi’a. Kai! Wasu ma


daga cikinsu har aske gashin kansu sukan yi, da yin wasu xabi’u da suka


sava wa hankali. Waxanda ke nuna cewa ba su karvi wannan qaddara ta


rashi da hannu biyu ba. Kuma ba shirye suke su yarda da hukuncin Allah


kome xacinsa ba.


Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya la’anci duk mai irin


wannan xabi’a. Abu Umamata Raliyallahu Anhu ya riwaito cewa,


“Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya la’anci duk macen da ke


yagar fuskarta, ta kece tufafin da ke jikinta, ta yi ta hargowa, tana faxin


bone yoyo! (Ibnu majah: 1/505).


Haka kuma Abdullahi xan Masu’du Raliyallahu Anhu ya riwaito


cewa, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce: “Duk wanda ke


119


yagar fuskarsa, ya kece tufafinsa, ya kuma yi kururuwa irin ta jahiliyyah,


ba ya tare da mu (Bukhari: 3/163).


Haka kuma Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce:


“Idan mai kukan mutuwa irin na jahiliyya ta mutu ba ta tuba ba, ranar


qiyama za ta tashi da rigar qaya da maxaurin qarangiya (Muslim: 934).


MARI DA TSAGA


Wasu uwaye da malamai nada xabi’ar sa hannu ko wani abu su


mari ‘ya’yansu ko xalibansu ko masu yi masu hidima, da nufin


ladabtarwa. Ladabtarwa kuwa gaskiya ce. Amma fuskar xan Adamu na


xaya daga cikin abubuwan da Allah Subhanahu Wa Ta’ala Ya karrama.


Kai mata mari kuwa tozartawa ne, da rena hikimar Allah, da walaqanta


abin da ya girmama.


Abun kan wuce mari. Wasu mutane har aska, ko wani abu mai


kaifi sukan sa su yi wa fuskar ‘ya’yansu raxam, da nufin tabbatar da wata


al’ada ta gida a matsayin alama. A yayin da wasu kuma dabbobinsu suke


yi wa tsagar, wai don a banbance tsakanin garken wane da na wane.


Kuma hakan za ta taimaka ga gane ai wannan dabbar ta wane ce. Idan ta


yi vatan kai nan take sai a mayar masa da abarsa.


Marin xan Adam haramun ne a shari’ar musulunci. Saboda hakan


kan iya sa a rasa wani abu daga cikin martabobin da Allah Subhanahu


Wa Ta’ala Ya sa a cikinta. Kamar: Gani, ko ji, ko shaqe. Wanda a qarshe


za su kai wanda ya yi abun ga nadama. Kuma diyya za ta hau kansa.


Abin da ya shafi xan Adam kenan. Ta fuskar dabbobi kuwa, su ma


shari’ah ta haramta yi masu wuta a fuska ko wata tsaga a matsayin alama.


Idan ma har ya zama dole sai an yi masu wata alama, saboda kasancewar


haka al’ada, to sai dai a yi masu a jiki ba a fuska ba, kuma ba da wuta ba.



Posts na kwanan nan

TAKAITACCEN BAYANI MA ...

TAKAITACCEN BAYANI MAI ANFANI GA SABON SHIGA MUSULUNC

ZIKIRAI WADANDA AKE Y ...

ZIKIRAI WADANDA AKE YIN SU DA SAFE DA KUMA YAMMA

BIDI’AR ‘YAN SHI’A A ...

BIDI’AR ‘YAN SHI’A A RANAR ASHURA

ANNABI ISAH AMINCIN A ...

ANNABI ISAH AMINCIN ALLAH YA TABBATA A GARESHI A CIKIN ALKUR’ANI 1