Labarai




Abubuwa Bakwai Masu


Halakarwa(Yiwa Mace Mumina


Kazafi)


Yiwa Mace Mumina Kazafi: A yanzu za mu yi


bayani akan abu na bakwai kuma na karshe cikin


abubuwa bakwai da Ma'aikin Allah – tsira da amincin


Allah su tabbata a gareshi- ya lissafa cikin abubuwan


da suke halakar da wanda yake ta'amuli dasu ,


wannan abu shine Yiwa Mace Mumina Kazafi.


Kazafi Shine: Jifan mutum da aikata alfasha ta


zina, ko kore juna biyu ko ma Da ba tare da ya


bayar cikakkun shaiduba.


Alokacin da mutum ya jefa kanshi cikin irin


wadannan halayya ta kazafi to lalle ya jefa kansa


cikin halayyar da take halakarwa, domin yin kazafi


ba karamin bala'ibane, alokacin da mutum ai wance


mazinaciyace ko ya yi lalata da ita, ko wannan


ciknnanata bana mijintabane ko danta/'yarta ai bana


mijinta bane to lalle ya tsokano tsuliyar dodo dole ya


kawo cikakkun shaidu na mutane hudu maza


musulmai da zasu bada shaida akan hakan, idan


kuma mai kawo shaiduba ko ya kawo basu cikaba to


kowanne mutum gada cikinsu bulala tamanin (80)


za'a yi masa, kamar yadda bayanai zasu zo nan


gaba kadan.


Wannan shiri da musulunci yake dashi


bakaramin shiri bane domin kare mutunci, masu iya


Magana na cewa mutunci madarane in ya zube bai


kwasuwa, addinin musulunci yana daga cikin


4


manyan manufofinsa kare mutunci, wannan yasa


musulunci ya dauki irin wannan mataki


musammamma 'ya mace, domin alokacin da aka


bata mata suna to gaba daya anbata mata


rayuwarta, shi yasa ayoyin da suka yi Magana akan


kazafi sun anbaci macece basu anbaci namijiba


wannanko ba wai dan hukuncin ya sha daban bane


a'a hukuncin iri dayane ga duk wanda ya yi mace ko


namiji kazafi, kuma bai iya kawo cikakkakun


shaiduba, idan ko ya kawo shaidu da duk abinda


Shara'a ke bukata suka cika to baza'a kira wannan


da sunan kazafiba.


Yiwa mace mumina kazafi bai halattaba kuma


yana cikin abubuwan da suke halakarwa, saboda


haka dadin fira ko kiyayya kada ta dauki mutum ya


yiwa wata/wani kazafi ko yasa a yi.


Ayoyin Da Suka Yi Magana Akan Kazafi: Idan


ka tsaya ka kalli ayoyin zaka gansu kashi ukune


kuma duk suna cikin Suratun Nur.


Kashi Na Farko: Ayata: 4-5, Allah Madaukakin


sarki yana cewa: ''Wadanda suke jifan mata


masu kamunkai (da zina) sannan kuma basu


kawo shaidu huduba to ku yi musu bulala


tamanin (80), kuma kada ku sake karbar


shaidarsu har abada, kuma waddan sune


fasiakai. Saidai kawai wadanda suka tuba


bayan haka kuma suka kyautata to lalle Allah


mai yawan gafarane kuma mai yawan jinkai.''


Anan Allah madaukakin sarki ya bayyana


hukuncin duk mutumin da ya yiwa mace/namiji


kazafi kuma bai iya kawo shaidu huduba sai Allah ya


5


bayyana hukuncin da za'a yi masa. Abu na farko bulala tamanin (80), abu na biyu ba za'a sake karbar shaidarsaba har'abada, abu na uku kuma wannan mutumin fasikine. Sai idan ya tuba, to ananne malamai suke maganar shin inya tuba za'a ci gaba da karbar shaidarsa kuma shikenan shi ba fasiki bane? Amma ko ya tuba sai an yi mishi bulala tamanin. Kashi Na Biyu: Ayoyin da suka yi bayanin maigidan da ya yiwa matarshi kazafi kuma bai iya kawo shaiduba to shi tsinuwa za su yi da matar ta shi, Allah Yana cewa: ''Wadanda kuma suke jifan matansu (da zina) kuma ya kasance basu da shaidu saidai karankansu, to shaidar dayansu (itace) Rantsuwa hudu da Allah lalle shi yana cikin masu gaskiya * (Rantsuwa) ta biyar tsinuwar Allah ta haukanshi in ya kasance cikin makaryata. * Kuma abinda zai hana ayi mata azaba (haddi) shine ta yi Rantsuwa hudu da Allah cewar lalle shi (mijin) yana cikin makaryata *. (Rantsuwa) ta biyar lalle fushin Allah ya tabbata akanta in (mijin nata) ya kasance cikin masu gaskiya'' Surartun Nur, ayata: 6-8.


Anan Allah madaukakin sarki ya yi bayanin idan miji ya yiwa matarshi kazafi kuma bai iya kawo shaidu huduba to 'Li'ani'' za su yi. Amma duk wanda ba miji bane to kodai ya kawo sahaidu mutane hudu maza musulmai ko kuma ayi mishi bulala tamanin, ba maganar shi wanda aka yiwa kazafi wai ya rantse idan ba haka bane, ko kuma shi da ya yi kazafin


6


cewa ya rantse duk babu kodai shaidu ko bulala tamanin. Kashi Na Uku: Ayoyin da suka yi Magana akan kazafin da aka yiwa mata muminai masu kamunkai natsattsu kammalallu to wadannan masu yiwa irin wadannan matan kazafi tsine musu aka yi duniya da lahira. Allah madaukakin sarki yana cewa: ''Lalle dukkanini wadanda ke jifan mata masu kamun kai gafalallu (daga aikata dukkanin alfasha) wadanda suke muminai to an tsine musu a duniya da kuma lahira, kuma suna da azaba maigirma* Aranar da harsunannu za su bada shaida akansu da hannayansu da kuma kafafuwansu ta sanadiyyar abinda suka kasance suna aikatawa* Awannan ranarce Allah zai cika musu sakamakonsu na gaskiya, kuma zasu sani lalle Allah shi wanda yake mai gaskiya kuma mai bayyanar da abubuwa''. Suratun Nur, ayata: 23-25.


Wannan ya nuna mana shi karankanshi kazafin ya kasu kashi-kashi, kashi na farko shine yiwa gama garin mutane wadanda suke suna da kyawawan halaye da kuma wanda ba'a rasaba, su aka anbaci hukunci yi musu kazafi a kashin farko, sai kuma wanda ya kasance tsakanin miji da mata. Sai wannan kashi na uku, wanda mutum zai ga mace/namiji mai kamun kai mai addini natsattse mumini kawai ya antayo ashar ya watsa mata/mashi ya dinga fadan wasu maganganu wanda da za'a tara mishi arzikin duniya domin ya kawo shaida akan haka ba zai iyaba. Domin wani ya dauka irin halin da


7


yake dashi to kowa haka yake, to kaga bayan ya


kasa kawo wadannan shaidu za'a yi masa hukuncin


kazafi anan duniya sanna kuma ya jira ranar


alkiyama, domin Allah baya bari a taba bayinsa na


kwarai, Ya Allah ka samu daga cikinsu, ka karemu


da sharrin masharranta ka tsaremu ka tsaremana


imanimmu, amin.


Kammalawa: Daga takaitattun bayananan ya


bayyana agaremu yadda musulunci ya dauki mutunci


da daraja da kima ya karewa kowa mutuncinsa


musamman 'ya mace, domin idan ba hakaba sai


kowa ya fadi abinda ya ga dama ko asashi ya fada


yana ganin bai huce aci tararshiba, amma idan


yasan zai sha bulalane to dole ya naba'a yasan me


zai fada, sai yazama yak are mutuncinsa dana


zuriyarsa kamar yadda yak are mutuncin wani dana


ziriyarsa.


Annanne kuma muka zo karshen wannan silsila


wacce take dauke da sharhin wannan hadisi da Abu


Hurairata ya ruwaito daga wurin Ma'aikin Allah na


wadannan abubuwa bakwai masu halakarwa, lalle


ma'aikin Allah ya isar da manzanci kuma tsira da


amincin Allah su tabbata a gareshi, hakika ta'amuli


da wadannan abubuwa tabbas yana halakarwa kuma


wannan kowa ya gani ya tabbatar wannan zai kara


imanine bisa imani. Akaro na gaba zamu kawo


bayanne kuma wadanda zasu haskaka mana


rayuwarmu da addininmu, Allah ya kaimu wannan


lokacin ya hadamu da imani, aimn.



Posts na kwanan nan

FALALAR AZUMIN KWANA ...

FALALAR AZUMIN KWANA SHIDA SHAWAL

TAKAITACCEN BAYANI MA ...

TAKAITACCEN BAYANI MAI ANFANI GA SABON SHIGA MUSULUNC

ZIKIRAI WADANDA AKE Y ...

ZIKIRAI WADANDA AKE YIN SU DA SAFE DA KUMA YAMMA

BIDI’AR ‘YAN SHI’A A ...

BIDI’AR ‘YAN SHI’A A RANAR ASHURA