Labarai

HUKUNCE-HUKUNCEN


SALLAR IDI


حاكم صلاة العيد


[Hausa - [هوسا


Malan Aliyu Muhammad Sadisu


2014 - 1435


2


HUKUNCE-HUKUNCEN


SALLAR IDI


Gabatarwa: Dasunan Allah Mai yawan rahama maiyawan jinkai, tsira


da amincin Allah su tabbata ga fiyayyan halittar Allah Annabin tsira


Annabi Muhammad, da Iyalan shi da Sahabban shi baki daya. Bayan


haka a wannan karon za mu karkata akalar mu zuwa wani bangare da


ya ke hararomu a 'yan kwanakin nan, wannanan bangaran kuwa shi


ne na SALLAR IDI! Domin mu ga yadda musulunci ya tsara mana


komai abinda ya rage kawai a garemu shi ne bi, komai angama, Allah


tabbatar da duga-dugammu akan tafarkin Ma'aikin Allah.


Mecece Sallar Idi:''Ita sallar idi sallace da ake gabatar da ita a wani


lokaci kebantacce, awata siffa kebantacciya, sau biyu a shekara''.


Kafin mu kai ga fashin bakin wannan ta'arifi na sallar idi, bari mu


gabatar da tabbatuwarta tukunna.


Tabbatuwar Sallar Idi: Sallolin idi guda biyu da musulunci yake da


su (Karamar Sallah da Babbar Sallah) kowacce ta tabbata a shara'a,


ba wai bikine haka kwai na gargajiyaba.


Tabbatuwar Karamar Sallah: itace sallar da ake gabatarwa a ranar


1 ga Shawwal, don godiya ga Allah akan baiwar da ya yi mana na


kammala azumin watan Ramadan, wannan sallar ta tabbata a Suratul-


A'alah aya ta:14-15, Allah madaukakin sarki yana cewa: ''Tabbas


duk wanda ya bayar da zakka (Fidda-kai) ya rabauta. Kuma ya


anbaci sunan UbangijinSa sannan kuma ya yi sallah''. Sai


malamai sukace 'Zakka da aka anbata a ayar farko itace zakkar fiddakai,


Sallah kuma da aka anbata a aya ta biyu itace, karamar sallah


domin itace ake fitar da zakkar Fidda-kai kafin a ta fi, sannan kuma ga


zikirin da aka an'anbata shine wanda ake yi lokacin tafiya sallar idin'.


Tabbatuwar Babbar Sallah: Ita kuma sallah ce da ake gabatar da


ita a ranar 10 ga watan Zul-Hajji. Ita ma babbar Sallah ta tabbata a


Suratul-Kauthar a aya ta: 2. a inda Allah madaukakin sarki yake cewa


''Ka yi Sallah domin Ubangijinka, kuma ka soke (abin


hadayarka)'', malamai sukace 'Babbar Sallah ce domin an hada


Sallah da Yanka' a ayar kamar wacce ta gabata an'hada Zakka da


3


Sallah. Wannan tabbatuwar wadannan sallolike nan ta ayoyin


alkur'ani, hakanamma sun tabbata ta ayyukan Ma'aikin Allah –Tsira da


amincin Allah su tabbata a gareshi-, Bukhari da Muslim da Abu-Daud


da Nasa'i duk sun ruwaito daga Jabir-Allah Ya kara masa yarda yace


''Na harci Sallar idi tare da Ma'aikin Allah –Tsira da amincin


Allah su tabbata a gareshi- sai ya fara gabatar da sallah kafin


Huduba ba tare da an yi kiran sallaba ko an tada Ikama''. Haka


shima Bara'u dan Azib –Allah Ya kara masa yarda yace ''Ma'aikin


Allah –Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi- ya yi mana


huduba a ranar babbar sallah, bayan ya idar da sallah sai yace


''Duk wanda ya yi wannan sallar tamu, kuma ya yi yanka irin


namu to yankanshi ya yi daidai, wandako ya yanka kafin ayi


sallah to wannan bashi (da ladan) yanka''. Wannan hadisin


malaman Hadisi bakwaine suka ruwaito shi.


Hukuncin Sallar Idi: Hukuncin sallar idi shine, Sunnace mai karfin


gaske, domin Ma'aikin Allah –Tsira da amincin Allah su tabbata a


gareshi- ya aikata ta kuma ya lizimceta, hakanan kuma ya fitar da


mata da kanan yara zuwa halartar wannan sallah. Saboda haka bai


kamata mutum ya yi sakaci da itaba har ya rasa samun wannan sallah


wanda saboda ita nema aka bada hutu a kasa baki daya, ka rufe


shagonka na kasuwanci ka dakatar da ayyukanka.


Lokacin Sallar Idi: Kamar yadda bayani ya gabata a ta'arifi cewa


sallace da ake gabatarwa a lokaci kebantacce to wannan lokacin kuwa


shine ''Daga lokacin da rana ta fito ta daga kamar tsawon


sandar mashi harzuwa lokacin da rana zata karkata daga


tsakiyar sama''. Amma malamai sukace 'An fi so a babbar sallah a yi


ta da wurwuri domin mutane su samu su koma gida domin su yanka


layyarsu a daidai lokacin walaha, sannan kuma su ci abinci domin basu


ci ba suka fito sallah. Amma akaramar sallah an fi so a dan jinkirta


sallar domin mutane su samu su gama fitar da Zakkar su ta fidda-kai,


su kuma ci abinci domin iti an fi so a ci kafin a fito sallah'.


Ladubban Sallar Idi: Akwai wadansu ladubba da yakamata a ladabtu


da su, wadannan ladubba suna da yawa daga ciki akwai:


1. Yin wanka da sanya turare da kuma sanya tufafi masu kyau


sababbine ko nada.


2. Hakanan yana daga cikin labudda a ci abinci kafin a fita sallar idi a


karamar sallah, da kuma jinkirta cin abinci a babbar sallah har sai an


yi sallah, da kuma cin wani abu na hantar dabbar layyah ga wanda ya


yi. Ankarbo daga Buraidah –Allah Ya yarda da shi- yace; ''Ma'aikin


4


Allah –Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi- ya kasance baya


fita zuwa masallcin idi a karamar sallah har sai ya ci abinci, kuma ya


kasance baya cin abinci a babbar sallah har sai ya dawo daga


masallacin idi, sai ya ci wani abu na dabbar layyarsa''.wannan Hadisi


Tirmizine ya ruwaito.


3. Kana yana daga cikin ladubba yin kabarbari, kuma lafazinta shine:


Allahu Akbar, Allahu Akbar, La'ilaha Illallahu, Allahu Akbar,


Allahu Akbar, Walillahil Hamd.


4. Yin gaisuwar sallah wato kacewa dan'uwanka musulmi ''Allah Ya


karba mana ya karba muku''.


Siffar Sallar Idi: Kamar yadda ya gabata a farkon bayani cewa


sallace da ake gabatar da ita a wata siffa kebantatta, wannan siffa


kuwa itace; wannan sallah ana yin ta ne Raka'a biyu, kuma ana


bayyana karatun, ba tare da angabatar da kiran sallah ba, ko tada


ikama, sannan kuma ba'a gabatar da nafila kafin sallar ko bayan


sallar. A raka'ar farko bayan kabbarar harama anayin kabarbari shida


kafin fara karatu (wato kabarbari bakwai kenana). A Raka'a ta biyu


bayan kabbarar tasowa sai a yi kabarbari biyar, kafin fara karatu


(wato kabarbari shida kenan), wadannan kabarbari liman da mamu


duk suna yinsu sai dai mamu baya karatun sallah saboda karatun


liman, sannan sai ayi sallar kamar sauran salloli, bayan liman ya yi


Tahiya ya yi sallama sai ya gabatar da Huduba, sannan yana da


matukar muhimmanci a tsaya a saurari hudubar, wadannanfa sune


ayyukan ranar, amma wacce gaggawa mutane suke yi suke barin


sauraron Hudubar?.


Wanda bai samu sallar idi ba ya samu ya yi sallah Raka'a


hudu kamar nafilfili, idan kuma ya ga dama ya yi ta a siffar sallar idi.


Idan kazo ka sami liman yana Tahiya sai ka zauna tare da


shi, idan ya yi sallama sai ka mike ka kawo raka'oinka biyu a siffar su


da ta gabata.


Wadansu Mas'aloli: A yanzu za'a kawo wadansu halaye da mutum


yakan samu kanshi a ciki idan ya zo ya samu tuni anfara sallah.


1. Idan mutum ya zo ya sami liman ya kammala kabarbari ya fara


karatu ya zai yi?. Amsa: Anan zaka yi wadannan kabarbarin,


kasancewar ba abune mejan lokaci ba, sannan sai ka raurari karatun


liman.


2. Idan ka zo ka sami liman ya fara kabarbari amma bai gamaba, to


anan zaka yi sauran kabarbarin da suka ragewa liman tare da shi,


sannan sai ka kawo wadanda suka wuceka, koda liman ya fara karatu,


5


kenan anan ba zaka yi wadanda suka wucekaba a lokacin kabarbarin


liman.


3. Idan kazo ka sami liman yana Ruku'u sai ka yi kabbarar harama


kadai ka bishi, ba sai ka kawo sauran kabarbarinba.


Tambihi: Ya kamata mu san girman wadannan salloli da matsayinsu a


addini, tunda har yakai Ma'aikin Allah –Tsira da amincin Allah su


tabbata a gareshi- yana cewa a fita sallar har da mata da kananan


yara, har mata marasa tsarki idan sun je sai su yi nesa da wurin sallah


idan anzo huduba suma sai su anfana. Kada mu sha'afa akan wannan


sallarne aka bada hutu duka kasa, aka rufe shaguna kada mutum ya


shagala a wannan lokaci da abinda zai hana mishi samun wannan


sallah. Sannan kuma a kula da yara da irin suturar da za su sa, domin


idan ka ga wadansu yaran ba kace 'ya'yan musulmi bane, wannan


baidace ba kuma baikamata, wasu kuma rawa kamar mazari, Allah Ya


sawwaka, amin.


Kammalawa: Daga wadannan bayanai da suka gabata ya bayyana a


garemu cewar sallar idi ba wata gargajiya bace ibadace da Allah ya


shar'anta ta ta harshen fiyayyan halitta Annabi Muhammad –Tsira da


amincin Allah su tabbata a gareshi-, itako ibada anayinta akan yadda


aka tsarata ne, Allah ya karbi ibadarmu ya sa ayi sallah lamilafiya ya


tsaremu ya tsare mana imaninnu, amin.


Rbutawa :


Malan Aliyu Muhammad Sadisu



Posts na kwanan nan

SAKO DAGA MUSULMI MAI ...

SAKO DAGA MUSULMI MAI WA'AZI ZUWA GA MUTUM KIRISTOCI

FALALAR AZUMIN KWANA ...

FALALAR AZUMIN KWANA SHIDA SHAWAL

TAKAITACCEN BAYANI MA ...

TAKAITACCEN BAYANI MAI ANFANI GA SABON SHIGA MUSULUNC

ZIKIRAI WADANDA AKE Y ...

ZIKIRAI WADANDA AKE YIN SU DA SAFE DA KUMA YAMMA