Labarai




35


dan wannan yafi girma lokacin da ta fadi sa yace ya ku


mutane na lallai ni na barranta dag abunda kuke shirka da


shi (78) lallai ni na fuskantar da fuska ta ga wanda ya kagi


halittar sammai da kasa ina mai karkata zuwa gare shi


kuma ni bana cikin masu shirka (79)” suratul An’am, aya ta:


74-79.


Hakan bai burge shi kuma da fiirar shi yaji a jikin sa cewa


akwai abun bauta da yafi wadannan halittun girma wadan da


basa cutarwa ko amfanarwa, har Allah ya shiryar da shi zuwa


ga sanin sa kuma ya zabe shi da manzancin sa, kuma shi tsira


da amincin Allah ya tabbata a gare shi ya kasance yana yawan


jayaiyya da mutanen sa musamman ma da dalilai na hankali


wadanda basa barin wani wuri na kokwanto wajen bata abun da


suke kudurcewa da kuma abunda suke bautawa komabayan


Allah, kamar yadda Allah ya baiyyana haka da fadar sa: “


kuma ka karanta musu labarin annabi Ibrahim (69) lokacin


da yace wa mahaifin sa da mutanen sa me kuke bauta ma


(70) sai sukace muna bauta wa wasu gumaka ne sai mu


doge muna masu gurfana a gare su (71) sai yace shin suna


jin ku in kuna kiran su (72) kuma suna amfanar da ku ne


ko cutarwa (73) sai suka ce a’a mu mun samu iyayen mu ne


haka suke aikatawa (74) sai yace kun ga ababen nan da


kuke bautawa (75) ku da iyayen ku na da (76) to lallai su


makiya ne a gare ni sai dai ubangijin talikai (77) wanda ya


halicce ni to shi ne zai shiryar da ni (78) kuma wand yake


ciyar da ni da shayar da ni (79) kuma in nayi rashin lafiya


to shi ne yake warkar da ni (80) kuma shi ne wanda yake


kashe ni sannan ya rayar dani (81) kuma shi ne wanda nake


kwadayin ya gafarta mun zunubai na ranar sakamako (82)


36


ya ubangiji ka bani wani hukunci kuma ka riskar da ni da


salihai (83) kuma ka sanya mun harshe na gaskiya a cikin


masu zuwa (84)” suratush Shu’ara’i, aya ta: 69-84.


Ya ci gaba da kirn mutanen sa tsira da amincin Allah ya tabbata


a gare shi zuwa ga kadaita Allah da bauta masa da kuma jifa da


dukkan abunda suke bautawa koma bayan Allah sai dai su sun


karyata shi kuma suka musa manzancin sa kuma sukayi


yunkirin kona shi da wuta sai Allah ya tsiratar da shi daga gare


su, kamar yadda Allah ya bada labarin sa da fadar sa: “ kuma


hakika mun baiwa Ibrahim shiriyar sa tun gabanin haka


kuma mu game da shi masana ne (51) lokacin da yace wa


mahaifinsa da mutanen sa wadannan wasu irin gumaka ne


da kuke bautama wa (52) sai sukace mun samu iyayen mu


ne muma suna bauta musu (53) sai yace hakika ku da


iyayen ku kun kasance cikin bata baiyananna (54) sai suka


e shin kazo mana da gaskiya ne ko kuwa kai kana cikin


masu wasa ne (55) sai yace ai ubangijin ku shi ne ubangijin


sammai da kasa wanda ya halicce su kuma ni mai shaida ne


akan haka (56) kuma wallahi sai na rusa gumakan ku


bayan kun juya baya kun tafi (57) sai ya sanya su a farfashe


sai dai babban su dan wata kila zasu komo zuwa gare shi


(58) sai sukace waye ya aikata haka ga allolin mu lalli shi


yana cikin azzalumai (59) sai sukace munji wani saurayi


yana ambaton su da batanci ana kiran shi Ibrahim (60) sai


sukace to kuzo da shi a gaban idan mutane ko zasu bada


shaida (61) sai sukace shin kai ne ka aikata haka ga allolin


mu ya kai Ibrahim (62) sai yace a’a wannan babban na


cikin su ne ya aikatato ku tambaye su mana in suna


magana (63) sai suka koma zuwa ga kawonan su sai sukace


37


lallai kune azzalumai (64) sa’annan sai suka sunkuyar da


kawunan su suka ce hakika ka san cewa wadancan basa


magana (65) sai yace to yanzu zaku dinga bautawa wani


abu koma bayan Allah wanda bazai amfane ku da komai ba


ko kuma ya cutar da ku (66) tur da ku da kuma abunda


kuke bautawa koma bayan Allah shin baza ku hankalta ba


(67) sai sukace ku kona shi kuma ku taimaki allolin ku in


har zaku aikata (68) sai mukace yake wuta ki kasance sanyi


da aminci ga Ibrahim (69) kuma sunyi nufin makirci a gare


shi sai muka sanya su sune masu hasara tababbu (70)”


suratul Anbiya’i, aya ta: 51-70.


Bayan mutanen shi sun karyata shi sai Allah ya umarci shi da


barin garin shi da matar shi Hajara da yaran sa Isma’il zuwa


makkah a inda Allah ya nuna wa Annabi Ibrahim wurin da


dakin ka’abah yake sai ya ginashi kuma yaran sa Ismail ya


taimake shi wanda ta tsatson shi ne na karshen Annabawa ya


fito wato Annabi Muhammad (S.A.W) wanda aka aiko shi


zuwa ga mutane baki daya har zuwa ranar alkiyama, dan


wannan gidan ya zama alkiblar musulmai dukkan su a gabas da


yamma, kamar yadda Allah ya baiyyana haka da fadar sa: “


kuma lokacin da Ibrahim yace ya ubangiji ka sanya


wannan gari ya zama amintacce kuma ka azurta mutanen


cikin sa da kayan marmari wanda sukayi imani daga cikin


su da Allah da rana ta karshi sai yace kuma duk wanda ya


kafurce to zan jiyar da shi ddi dan kadan sannan zan jefa


shi cikin azabar wuta kuma makoma tayi muni (126) kuma


lokacin da Ibrahim yake daga tushe na ginin ka’abah da


kuma Isma’il sai suka ce ya ubangiji ka amsa mana lallai


kai mai ji ne masani (127) ya ubangiji kuma ka sanya mu


38


mu zama masu mika wuya a gare ka da kuma zurriyyar mu


su zama al’umma masu mika wuya a gare ka kuma ka


nuna mana wuraraen bautan mu kuma ka yafe mana lallai


kai mai yawan karbar tuba ne mai jin kai (128) ya


ubangijin mu kuma ka aika da wani manzo daga cikin su


zuwa gare su wanda zai dinga karanta musu ayoyin ka


kuma ya sanar da su littafi da hikima kuma ya tsarkake su


lallai kai mabuwayi ne mai hikima (129) kuma babu mai


kauda kai daga tafarkin Ibrahim sai dai fa wanda ya


wawantar da kansa kuma hakika mun zabe shi a nan


duniya kuma lallai shi a lahira yana cikin salihai (130)


lokacin da ubangijin sa yace masa ka mika wuya sai yace


na mika wuya ga ubangijin talikai (131) kuma sai Ibrahim


yayi wasiyya da ita ga yaran sa da Yaqub cewa ya ku


yarana lallai Allah ya zabar muku addini kada ku sake ku


mutu sai dai kuna musulmai masu mika wuya (132)” suratul


bakara, aya ta: 126-132.


39


Shi ne wanda yayi magana da Allah, Allah ya mai magana ba


tare da wani shamaki ba, kamar yadda Allah ya baiyana haka


da fadar sa: “ lokacin da Musa yazo mikatin mu kuma


ubangijin sa yayi masa magana sai yace ya ubangiji ka


nuna mun kai in ganka sai yace baza ka iya gani na ba sai


dai kayi dubi zuwa ga wancan dutsen idan har ya tabbata a


inda yake to da sannu zaka ganni lokacin da ubangijin sa


yayi tajalli zuwa ga dutsen sai ya mai da shi a farfashe a


warwatse sai Musa ya fadi yana sumamme lokacin da ya


farfado sai yace tsarki ya tabbata a gare ka na tuba a


gareka kuma ni ne farkon muminai (143)” suratul A’raf, aya


ta: 143.


Kuma shi ne wanda aka fi ambato cikin manzanni bani isra’ila


a cikin Alkur’ani mai girma, an ambace shi a wurare dari


daashirin da tara wannan yana nuni akan matsayin wannan


Annabin da darajar sa mai girma, Allah ya karfafa shi da


mu’jizozi guda biyu, ta farkon su itace sanda wacce ta koma


kamar katon macijiya, amma dayar mu’jizar ita ce hannun sa


wanda yake shigar da shi cikin hammatan sa sai ya fito da shi


ya koma fari ba tare da mis ba, wannan na nuni akan gaskiyar


mazancin sa ga firauna da mutanen sa dan ko watakila su zama


dalili na gaskatawar su da imanin su ga Allah kamar yadda


Allah ya baiyyana haka da fadar sa: “ kuma Musa yace ya kai


fir’auna lallai ni manzo ne daga ubangijin talikai (104) da


gaskene bazan fadi komai bai game da Allah sai dai gaskiya


hakika nazo muku da hujjoji daga ubangijin ku to ka saki


40


mutanen bani isra’ila su tafi tare da ni (105) sai yace in har


kazo da hujjoji to ka kawo su mu gani in har kai ka


kasance cikin masu gaskiya (106) sai ya wurga sandar shi


sai gashi ta zama katon kumurcin maciji a baiyane (107)


kuma sai ya fito da hannun sasai ga shi yana haske fari tas


ga masu kallo (108)” suratul A’araf, aya ta: 104-108.


Allah ya aike shi zuwa wurin fir’auna da mutanen sa dan ya


kirasu zuwa ga bautar Allah shi kadai da watsar da dukkan


wani abu koma bayan sa bayan sun karkace daga addinin


gaskiya kuma sukayi girmankai da dagawa da kuma zalunci, ta


yadda fir’auna ya dunga kiran mutanen sa da su bauta masa


kuma yana umurtar su da yin bauta a gare shi irin wadda basa


yi wa Allah madaukaki, kamar yadda Allah ya baiyyana haka


da fadar sa: “ kuma sai fir’auna yace ya ku mutanen gari


ban san wani abun bauta a gare ku ba sai ni to ya kai


Hamana ka dauke ni akan tabo sai ka gina mun babban


gidan sama dan wata kila ko na leko Allahn Musa kuma


lallai ni ina zatan shi yana cikin makaryata (38)” suratul


Kasas, aya ta: 38.


Sai Annabi Musa amincin Allah ya tabbata a gare shi ya kira


shi ta hanyar hikima da sassaukan zance zuwa ga kadaita Allah


da bautar Allah shi kadai, sai Fir’auna ya yake shi kuma ya tara


mai bokaye dan su mai makirci, sai dai Annabi Musa amincin


Allah ya tabbata a gare shi ya yi rinjaye a kansu da ikon Allah,


bayan ya jefa sandar sa wacce ta hadiye sandunan bokayen da


igiyoyin su wadanda aka juyar da su suka koma suna tafiya


saboda tsafi suka zama kamar macizai kamar yadda Allah ya


baiyyana haka da fadar sa: “ sai iyan lagwada daga cikin


mutanen fir’auna sukace lallai wannan mai sirhiri ne


41


masani (109) yana so ne ya fitar da ku daga kasarku to


meye kuke umarni da shi (110) sai suka ce a kore shi da dan


uwan shi kuma ku tura gari gari dan tattaro mutane (111)


dan a zo maka da kowane mai sihiri masani (112) sai masu


sihirin fir’auna suka zo sai suka ce lallai mu munada wata


lada ne in mun kasance mu ne masu galaba (113) sai yace


eh kuma lallai ku zaku zama cikin makusanta (114) sai


suka ce ya Musa ko dai ka fara jefawa ko kuma mu ne


zamu fara jefawa (115) sai yace ku jefa lokacin da suka jefa


sai suka sihirce idanun mutane kuma suka firgitar da su


kuma sun zo da sihiri mai girma (116) sai mukayi wahayi


zuwa ga Musa cewa ka jefa sandar ka sai gashi tana hadiye


abunda suke jefawa (117) sai gaskiya ta baiyyana kuma


abunda suka kasance suna aikatawa ya blalace ya baci


(118) kuma sai aka rinjaye su a wannan wurin sai suka


komo suna kaskantattu (119) sai masu sihiri suka fadi suna


masu sujada (120)” suratul A’araf, aya ta: 109-120.


Fir’auna da mutanen sa sun karyata Annabi Musa amincin


Allah ya tabbata a gare shi sai Allah ya daura musu ukubobi iriiri saboda karayatawar da sukayi da kuma barna da suke yi


aban kasa, sai Allah ya aiko musu da ruwan dufana da fari da


kwarkwata da kwadi da jini, ayo yi filla-filla sai sukayi girman


kai kuma suka zama kafurai, sai daga baya Allah ya dage su


daga gare su saboda addu’ar Annabi Musa bayan sun nemi da


yayi addu’a ya roki ubangijin sa dan ya yaye su daga gare su


wta kila zasu gaskata kuma suyi imani, sai dai hakan bai kara


musu komai ba sai dai kangare wa da kafurci da girman kai,


kamar yadda Allah ya baiyyana haka da gadar sa:“ kuma


sukace duk abunda zaka zo mana da shi na ayoyi dan ka


42


sihirce mu da su to mu baza muyi imani da kai ba (132)sai


muka aika musu da dufaan da fari da kwarkwata da kwadi


da jini ayoyi ne a rarrabe sai sukayi girman kai kuma sun


kasance mutane mujirimai (133) lokacin da girgije ya fado


a kan su sai suka ce ya Musa ka roka mana ubangijin ka da


abunda ya saba maka da shi dan idan ka dauke mana


wannan girgijen to wallahi lallai zamuyi imani da kai kuma


lallai zamu saki bani isra’ila tare da kai (134) lokacin da


muka yaye musu girgijen zuwa wani lokaci wanda su zasu


kai shi sai gashi suna warware alkawari (135)” suratul


A’araf, aya ta:132-135.


Bayan wanna sabawar da taurin kai da kafurci baiyananne daga


Fir’auna da mutanen sa sai Allah ya umarci Annabi Musa


amincin Allah ya tabbata a gare shi da fita shi da mutanen sa


cikin dare sai ya fita daga masar shi da muminai cikin mutanen


sa daga cikin mutanen bani isra’ila dan su gudu da addinin su,


si Fir’auna da rundunar sa suka bi shi saboda kiyaiyya da


zalunci, lokacin da jama’ar biyu suka hango juna kuma ga teku


a gaban su kuma fir’auna da rundunar shi suna bayan su, sai


mutanen Annabi Musa suka ce:” lallai mu an kama mu” sai


Annabi Musa fada yana mai tabbaci da ubangijin sa cewa zai


kubutar da su da kuma irin alkawarin da yayi masa na samun


nasara akan abokan gaban sa:” a’a” sai Allah yayi masa wahayi


cewa ya bigi tekun da sandar sasai ya tsage biyu sai ya zama


kamar dutse mai girma dan Allah ya tsiratar da Annabi Musa


da wadan da suke tare da shi kuma ya nutsar da Fir’auna da


rundunar sa, kamar yadda Allah ya baiyyana haka d fadar sa: “


lokacin da jama’r biyu suka ga juna sai mutanen Annabi


Musa suka ce lallai mu za’a riske mu (61) sai yace a’a lallai


43


ni akwai ubangiji na a tare da ni zai shiryar da ni (62) sai


mukayi wahayi zuwa ga musa cewa ka bigi tekun da sandar


ka sai tekun ya rabe sai kowane bangare ya zama kamar


dutse mai girma (63) kumai sai muka kusanto da wadancan


jama’ar na daban (64) kuma sai muka kubutar da Musa da


wadanda suke tare da shi baki daya (65) sa’annan sai muka


nutsarda wadancan da suka rage (66)” suratush Shu’ara’i,


aya ta: 61-66.


Allah ya karfafa Annabi Musa amincin Allah ya tabbata a gare


shi da wannan mu’ujizar wacce Fir’auna da mutanen sa basu


taba tsammanin ta ba, sai dai al’amarin Allah mai zartuwa ne


kuma abunda yayi nufi mai kasantuwa ne dan ya zama a cikin


haka akwai kubutar Annabi Musa da wadanda suke tare da shi


cikin muminai kuma dan ya zama a cikin ta akwai halakar


fir’auna da mabiyan sa dan ya zama aya ga wadanda suke


bayan sa da kuma abun izina, ta yadda tekun ya jeho shi waje


bayan ya halaka, kamar yadda Allah ya baiyyana haka da fadar


sa: “ kuma muka ketarar da bani isra’ila teku sai fir’auna da


rundunar sa suka bisu dan mugunta da kiyaiyya har zuwa


lokacin da nutsewa ta riske shi sai yace nayi imani cewa lallai


babu abun bauta sai wannan wanda bani isra’ila sukayi imani


da shi kuma nima ina cikin musulmai masu mika wuya (90)


shin a yanzu kuma alhali a baya ka bijire kuma ka sance cikin


masu barna (91) a yau zamu tsiratar da kai da gangan jikin ka


dan ka zama aya ga wadanda zasu zo a bayan ka kuma lallai da


yawa daga cikin mutane gafalallu ne game da ayoyin mu (92)”


suratu Yunus, aya ta: 90-92.


44


Shine shugaban mu Isah dan Maryam Annabi na karshe na bani


isra’ila, Allah ya aiko shi bayan Annabi Musaamincin Allah ya


tabbata a gare shi zuwa ga mutanen bani isra’ila lokacin da


suka baci kuma suka kauce daga ingantacciyar hanya, kamar


yadda Allah yabaiyana haka da fadar sa: “ kuma sai muka zo


da Isah dan Maryama a bayan su yana mai gaskata abunda


ya gabace shi na attaura kuma mun bashi injila a cikinta a


kwai shiriya da haske kuma yana gaskata abunda ya


gabace shi na attaura kuma shiriya ne da kuma tunatarwa


ga masu tsoran Allah (46)” suratul Ma’ida, aya ta: 46.


An haife shi ba tare da uba ba saboda wata hikima da Allah


yake nufi, hakika ya so ne ya baiyana wa halittunsa ikon sa ga


ga halittar sa, ta yadda ya halicci Adam ba uwa ba uba, kuma


ya halicci Hauwa’u daga namiji ba mace, sai kuma ya halicci


Isah ba namiji, saboda haka ne Allah ya fada a cikin suratu


maryam: “ kuma dan sanya shi ya zama aya ne ga mutane “


suratu Maryam, aya ta:21.


Misalin halittar sa kamar misalin halittar Adam ne Allah ya


halcce shi daga turbaya sannan sai ya ce masa “ kasance” sai ya


kasance, kamar yadda Allah ya baiyyana haka da fadar sa:”


lallai misalin Isah a wurin Allah kamar misalin Adam ne


Allah ya halicce shi daga turbaya sa’annan sai yace masa


kasance sai ya kasance (59)” suratu Ali imaran, aya ta: 59.


An aike shi zuwa ga bani isra’ila sai sukakaryata shi kuma suka


yake shi kuma suka cutar da shi, sai yayi hakuri kuma yaci


gaba da isar da sakon manzancin sa, kuma saboda yasan cewa


45


ba shi ne na karshen manzannin Allah ba sai yayi bushara da


wani manzo da zai zo a bayan sa sunan sa Ahmad2


(S.A.W),


Allah ya sanar da shi littafi da hikima da attaura da injila kuma


ya karfafa shi da mala’ika Jibrilu kuma ya kasance mai daraja a


nan duniya da kuma lahira kuma ya kasance cikin makusanta,


Allah ya bashi wasu mu’ujizozi wadanda suka ruda mtanen


lokacin sa, hakika shi yayi wa mutane magana alhali yana cikin


tsumman goyo, kuma ya kasanceyana hada tsuntsu na tabo sai


yayi busa a ci sai ya tashi sama ya zama tsuntsu da izinin Allah,


kuma yana warkar da mai kyasfi da kuturu kuma yana raya


matattu dukkkan wannan na faruwa ne da izinin Allah, kuma


yana baiwa mutane labarin abunda suka ci da abun da suka


taskace, kamar yadda Allah ya baiyyana haka da fadar sa: “


lokacin da mala’iku suka ce ya ke Maryam lallai Allah yana


miki bushara da wata kalma daga gare shi sunan sa


almasihu Isah dan Maryama mai daraja ne a duniya da


lahira kuma yana cikin makusanta (45) kuma yana magana


da mutane a cikin tsumman goyo da kuma bayan ya


manyanta kuma yana cikin salihai (46) sai tace ya ubangiji


ta yaya zan samu yaro kuma alhali babu wani mutum da ya


taba taba ni sai yace haka nan Allah yake halitta abunda


yaga dama idan ya kaddara wani lamari to kawai yana ce


masa ne kasance sai ya kasance (47) kuma zai sanar da shi


littafi da hikima da Attaura da Injila (48) kuma manzo ne


zuwa ga bani isra’ila cewa lallai ni nazo muku da hujjoji


daga ubangijin ku lallai ni ina halitta muku daga daga tabo


wani abu mai kama da tsutsu sai in yi busa a cikin sa sai ya


zama tsuntsu da izinin Allah kuma ina warkar da mai





2


- Ahmad daya ne daga cikin sunayen Annabi Muhammad S.A.W.


46


kyasfi da kuturu kuma ina raya matattu da izinin Allah


kuma ina baku labarin abunda kuka ci da abunda kuke


taskacewa a cikin gidajen ku lallai a cikin haka akwai ayoyi


a gare ku in kun kasance muminai (49)” suratu Ali imran,


aya ta: 45-49.


Da’awarsa ta kasance irin da’awar sauran iyan uwansa


manzanni kafin sa, sai ya kira mutanen sa zuwa ga bautar Allah


madaukaki, sai dai shi ya hadu da abun da ya hadu dashi daga


gare su na karyatawa da girmankai, kuma ba wanda yayi imani


da shi sai dai masu rauni cikin mutanen sa, yahudawa sun yi


yunkurin halaka shi da da’awar sa sai Allah ya tsiratar da shi


daga gare su ta yadda ya dauke shi zuwa sama, sai yahudawa


suka kashe mutumin da Allah ya sanya mai kama irin ta Annabi


Isah, sai yahudawa da wadanda suka rako su cikin kiristawa


sukayi zatan cewa an kashe shi, kuma shi zai sauko a karshen


zamani zuwa kasa kma zaiyi hukunci da shari’ar Annabi


Muhammad (S.A.W) daga baya sai Allah ya dau ran sa dan


tabbatar da fadar Allah madaukaki:” dukkan wanda ke kanta


mai karewa ne (26) kuma fuskar ubangijin ka ce zata rage


ta wanzo ma’abocin girma da karamci (27)” suratur


Rahman, aya ta: 26-27.


47


Manzan Allah Muhammad (S.A.W) Annabin da bai san karatu


ba ko rubutu balarabe daga tstson Annabi Isma’ila dan


Ibrahima baban Annabawa, shi ne karshen manzanni kuma


mafificin su baki daya, an aiko shi zuwa ga mutane baki daya,


an haife shi a makkah bayan rasuwar mahaifin shi da watanni


kadan, sannan sai daga baya mahaifiyar shi ta rasu alhali yana


jariri, sai kakan sa Abdul mutallib ya raine shi, sai dan uwan


baban sa Abu dalib, kuma yayi kiwon dabbobi na wani lokaci


ga mutanen makkah, Allah ya aiko shi zuwa ga mutane baki


daya ba wai larabawa ba kawai, ya aiko shi dan jin dadin


mutane baki daya kuma dan ya baiyana musu hanyar gaskiya


da alheri kuma ya tsawatar da su daga hanyar barna da sharri,


rayuwar sa dukkanta ta kasance gaskiya ce da amana, ba’a


sanshi da yaudara da karya ba, ko cin amana da zamba,an


sanshi tsakanin mutane da amintacce sun kasance suna aje


amanaonin su a wurin sa, kuma suna aje kayan su a wurin sa in


zasuyi tafiya, kuma sun sanshi da gaskiya, saboda irin abunda


aka san shi da shi na gaskiya cikin abunda yake fada da kuma


bada labarin sa, wahayi ya sauka a gare shi yana da shekaru


arba’in, ya zauna a garin makkah shekaru goma sha uku yana


kiran mutane zuwa ga kadaita Allah da kuma barin bautar


gumaka sannan sai yayi hijira zuwa madinah mai haske ku a ya


kira mutanen ta zuwa musulunci sai suka musulunta sai Allah


ya saukar masa da sauran aiyuka na shari’o’in addini, kuma ya


ci makkah da yaki bayan shekaru takwas da yin hijiran sa kuma


ya rasu shekariun sa sittin da uku bayan an saukar masa da


Alkur’ani cikakke kuma shari’a ta cika dukkan ta kuma


48


larabawa suka shiga cikin musulunci kuma mabiyan sa suka


fara yada musuluni a bayan sa a cikin lunguna na doran kasa


wacce aka raya kai har zuwa wannan ranar tamu mutane suna


shiga cikin wannan addinin mai girma dan yarda da sukayi da


shi da kansu cew hi ne addini na gaskiya wnnan kuwa bayan


sun san hanyoyin ushen sa ingantattu.


49


Aiko da manzanni da kuma annabawa ya ci gaba har zuwa


wani lokaci mai tsawo bayan Annabi Nuhu amincin Allah ya


tabbata a gare shi har zuwa Annabi Isah amincin Allah ya


tabbata a gare shi wanda da shi ne aka cike Ammabawan bani


isra’ila dan al’amarin manzanci da annabci ya koma ga Annabi


Muhammad (S.A.W) dan ya zama na karshen Annabawa baki


daya, kamar yadda Allah ya bada labarin haka da fadar sa: “


Muhammadu bai zamo mahaifin daya daga cikin mazajen


ku ba sai dai shi manzan Allah ne kuma cikamakin


Annabawa kuma Allah ya kasance masani ne ga dukkan


komai (40)” suratul Ahzab, aya ta: 40.


Lallai Annabi Isah amincin Allah ya tabbata a gare shi yana da


wta irin daraja ta musamman a cikin zukatan musulmai saboda


shi zamanin sa yafi kusa da su kuma yana cikin wadanda


sukayi bushara a fili da zuwan Annabin su Muhammad


(S.A.W), kuma hakika mamakin kiristoci zai karu in suka san


cewa sunan Annabi Isah ya maimaitu a cikin Alkur’ani har sau


ashirin da biyar a lokacin da shi kuma Annabi Muhammad


(S.A.W) manzan musulunci wanda shi ne aka saukar wa


Alkur’ani cewa ba/a ambaci sunan ba sai sau biyar kawai!!


Wannan yana cikin ababen da ke nuni karara akan cewa lallai


Annabi Muhammad (S.A.W) shi Annabi ne da aka aiko kuma


lallai abun da ake saukar masa da shi wahayi ne ake yi masa ba


daga zancen shi bane, da ace kur’ani maganar shi ne to da


sunan shi zai fi maimaituwa fiye da kowane mutum na daban.


Saboda matsayin wannan Annabi mai girma wato Isah amincin


Allah ya tabbata a gare shi alkur’ani ya kunshi ayoyi masu


50


yawa wadanda sukayi magana game da shi da kuma dangin sa


na gari masu albarka.


Haka nan ma Maryam mai tasrki mahaifiyar Annabin Allah


Isah amincin Allah ya tabbata a gare shi da danginta suna da


matsayi na musamman a cikin zukatan musulmai, hakika


Alkur’ani yayi yabo a gare ta kuma ya siffanta mahaifiyarta da


cewa ita mai bauta ce mai tsarki wadda take da tushe mai


albarka da kuma matsira mai kyau da kuma dangi na gari, kuma


ya daure sunan dangi ta –iyalan Imran- iyalai masu karamci da


kuma zurriyya masu albarka tsatsaon Annabawa da manzanni


wadda Annabi Isah yake dangantuwa zuwa gare ta da sura ta


uku a cikin Alkur’ani ita ce suratu Ali imaran, dan girmamawa


da kuma karramawa a gare su kuma dan wannan iyalan su


zama sunan zaune cikin kwakwalen musulmai suna mau


karamci da daraja a wurin su, Allah madaukakai yace: “ lallai


Allah ya zabi Adam da Nuhu da iyalan Ibrahim da iyalan


Imrana ya fifita su akan talikai (33) zurriyya ne sashin su


daga sashi kuma Allah mai ji ne masani (34)” suratu Ali


imaran, aya ta: 33-34.


51


Alkur’ani mi girma yayi yabo ga Maryam iyar Imran


mahaifiyar Annabi Isah amincin Allah ya tabbata a gare shi,


mai gaskiya mai daraja mai tsarke wacce ta taso a gidan


kamewa da tsarki, a cikin wurare da dama a Alkur’ani an


siffanta ta da salihanci da tsarki da kuma tsoran Allah, Allah


madaukaki yace: “ da kuma Maryam yarinyar Imrana


wacce ta tsare farkinta sai muka yi busa a cikin sa daga


ruhin mu kuma ta gaskata da kalmomin ubangijin ta da


littattafan sa kuma ta kasance cikin masu kankantar da kai


(12)” suratut Tahrim, aya ta: 12.


Kuma Alkur’ani ya baiyana cewa lallai Maryam amincin Allah


ya tabbata a gare ta ta samu ne ta sanadiyyar addu’a mai


albarka da ta fito daga uwa mai albarka, Allah madaukaki yana


cewa: “ lokacin da matar Imrana tace ya ubangiji lallai ni


nayi alwashi a gare ka na abunda ke ciki na cewa zaiyi


bauta ne a gre ka to ka amsa daga gare ni lalli kai mai ji ne


masani (35)” suratu Ali imran, aya ta: 35.


Kuma lallai wannan addu’ar mai albarka itace ta zama sababi


na tsare ta da yaranta Isa amincin Allah ya tabbata a gareshi kar


shaidan ya samu galaba a kan su, ta yadda ubangijin ta ya


amshe ta kuma ya karfafa ta da wasu karamomi wadanda suke


nuni akan kyawon inda ta taso, ta yadda arzikinta ke zuwa mata


alhali tana zaune awurin ta kuma abunda ke zuwa mata na


arziki yana zuwa ne a lokacin da ba nashi ba na kayan marmari


da sauran su, kuma lura da ita ya zama karkashin Annabi


Zakariyya amincin Allah ya tabbat a gare shi mutumin kirki


52


dan ya kula da ita da kuma damuwa da lamuran ta kamar yadda


Allah ya baiyyana haka a cikin Alkur’ani da fadar sa: “ lokacin


da ta haife ta sai tace ya ubangiji lallai ni haifeta mace


kuma Allah yafi ni sanin abunda na haifa kuma amma


mace ba kamar namiji ba kuma lallai ni na sa mata suna


Maryama kuma lallai ni ina nema mata tsarin ka da


zuriyyarta daga shaidan jifaffe (36) sai ubangijin ta ya


karbe ta karba mai kyau kuma ya raya ta rayuwa mai kyau


kuma Annabi Zakariyya ya jibinci lamuran ta lokacinda


Zakariyya ya shiga wurin ta a wurin bauta sai ya samu


arziki a wajen ta sai yace ya Maryam a ina kika samu


wannan sai tace shi daga wurin Allah yake lallai Allah yana


azurta wanda yaga dama ba tare da lissafi ba (37)” suratu


Ali imaran, aya ta: 36-37.


Ita ta kasance cikin masu bauta tsira da amincin Allah ya


tabbata a gare ta cikin wadanda babu kamar su a wajen bauta a


lokan su, Allah yayi mata baiwa da zabinta da yayi a cikin


matan lokacin ta, sai mala’iku sukayi mata bushara da hakan,


kamar yadda Allah ya bada lagarin haka a cikin Alkur’ani da


fadar sa: “ kuma lokacin da mala’iku suka ce ya ke maryam


lallai Allah ya zabe ki kuma ya tsarkake ki kuma ya zabe ki


ya fifita ki akan matan talikai (42) ya ke Maryam ki


kankan da kai ga ubangijin ki kuma kiyi sujada kuma kiyi


ruku’i tare da masu ruku’i (43)” suratu Ali imaran, aya ta:


42-43.


Kuma ma kari akan karamcin ta da bayanin falalar ta amincin


Allah ya tabbata a gare ta ya karu ta yadda Allah ya saukar da


sura kacukan da sunan ta (suratu Maryam) kuma itace sura ta


goma sha tara a cikin Alkur’ani, kuma it ce sura daya tilo


53


wacce take dauke da sunan mace a cikin Alkur’ani, kuma a


cikin wannan surar akwai yabo da girmamawa ga Maryam


wanda babu irin shi a cikin littattafan kiritoci ko bible- bible


din su, duk da cewa babu wata sura ko daya a cikin Alkur’ani


mai dauke da sunan daya daga cikin matan Annabi (S.A.W),


kamar Khadijah ko Aisha ko kuma yaran sa mata kamar


Fadima ko kuma iyan uwan sa Allah ya kara yadda a gre su,


haka nan kuma babu sura mai dauke da sunan dangin sa, sai dai


ma an samu sura ne mai dauke da alkawari na narkon azaba ga


daya daga cikin dangin sa shi ne baffan sa Abu Lahab wanda


Alkur’ani yayi hukunci cewa shi dan wuta ne, kuma wannan


babu kokwanto a cikin sa wanda haka ke nuni akan gaskiyar


manzancin sa, saboda da ace daga abunda ya rubuta ne da


kansa kamar yadda suke cewa da sun samu kwarzanta kansa a


cikin sa da kuma iyalan sa.


Kuma hakika Manzan musulunci Muhammad (S.A.W) yayi


yabo akan Maryama amincin Allah ya tabbata a gare ta kuma


ya lissafa ta cikin mafiya alherin matan duniya, a inda yace: “


mafi alherin matan duniya su ne: Maryam iyar Imran da


Khadija iyar Khuwailid, da fatima iyar Muhammad


(S.A.W) , da Asiya matar Fir’auna” sahihu ibn hibban.


Kuma Manzan musulunci Muhammad (S.A.W) yayi mata


shaida da cewa tana cikin mafiya falalan matan aljannah, sai


yace: “ mafiya falalan matan aljannah: Khadijah iyar


Khuwailid, da Fatima iyar Muhammad, da Maryam iyar


Imran, da Aiya iyar muzahim matar Fir’auna”. Sahihu ibn


hibban.


54


Alkur’ani mai girma yayi yabo ga Annabi Isah dan Maryam


amincin Allah ya tabbata a gare shi kuma ya siffanta shi da


wasu irin siffofi da suke nuni akan daukakar darajarsa a wurin


Allah madukaki, ta yadda ya sanya shi ya zama bushara ne ga


mahaifiyar sa Maryam amincin Allah ya tabbat aa gare ta, ta


yadda zai bata kayutan yaro zai halicce shi wata irin halitta da


ta sabawa hanyar halittan sauran mutane, zai halicce shi da


kudurarr shi da kuma ikon shi da kalmar “kun” kuma zai zama


mai daraja a duniya da lahira kuma yana cikin makusanta kuma


Annabi mai karamci mai tsarki wanda za’a karrama shi kum a


karfafe shi da wau irin mu’ujizozi, kuma manzo ne zuwa ga


bani isra’ila, kamar yadda Allah madaukaki ya ce: kuma yana


magana da mutane a cikin tsumman goyo da kuma bayan


ya manyanta kuma yana cikin salihai (46) sai tace ya


ubangiji ta yaya zan samu yaro kuma alhali babu wani


mutum da ya taba taba ni sai yace haka nan Allah yake


halitta abunda yaga dama idan ya kaddara wani lamari to


kawai yana ce masa ne kasance sai ya kasance (47) kuma


zai sanar da shi littafi da hikima da Attaura da Injila(48)”


suratu Ali imran, aya ta: 45-48.


55


Allah yayi bayani a cikin Alkur’ani mai girma hakikanin


Annabi Isah dan Maryam amincin Allah ya tabbata a gare shi


da kuma irin abunda Allah madaukaki ya kebance shi da shi na


mu’ujizozi, sai ya baiyyana yadda aka haife shi bayani mai


warkarwa isasshe lafiyaiyyen hankali na karbar sa da kuma


ingantaccen mandiki, ta yadda ya ajiye shi a inda ya dace da shi


a matsayin sa na Annabi sai ya sanya shi mutum bawa ga Allah


wanda aka tsarkake daga alfasha da kuma abunda yahudawa


suka jefe shi da shi cewa wai shi dan zina ne- Allah ya tsare shi


daga hakan- da kuma irin abunda wasu suka jefe shi da shi na


cewa shi dan Allah ne ko kuma shi Allah ne- Allah ya daukaka


daga haka daukaka mai girma-, Alkur’ani baya ganin cewa


haihuwar Annabi Isah amincin Allah ya tabbata a gare shi ba da


uba ba abu ne da zai sa a bauta masa ko kuma ya maida shi dan


Allah- - Allah ya daukaka daga haka daukaka mai girma- a’a ai


a cikin haka akwai dalili da ke nuni akan cikan ikon Allah akan


nau’o’in halitta, domin Allah ya halicci Adam ba tare da namiji


da macce ba, kuma ya halicci Hauwa’u daga namiji ba macce,


kuma ya halicci Annabi Isah daga macce ba namiji, kuma sai


ya halicci sauran halittu daga namiji da macce, Allah


madaukaki yana cewa: “ lallai misalin Isah a wurin Allah


kamar misalin Adam ne ya halicce shi daga turbaya sannan


sai yace masa kasance sai ya kasance (59) gaskiya ce daga


ubangijin ka kada ka kasance cikin masu jayaiyya (60) duk


wanda yayi jayaiyya da kai game da shi bayan abunda yazo


maka na ilimi to kace ku taho mu kira yaran mu da yaran


ku da matan mu da matan ku da mu kan mu da ku kan ku


sannan sai muyi mubahala sai mu sanya tsinuwar Allah ta


56


tabbbata akan makaryata (61) lallai wannnan shi ne


labarin gaskiya kuma babu wani abun bauta da gaskiya sai


dai Allah kuma lalllai Allah shi ne mabuwayi mai hikima


(62) kuma idan suka juya baya to lallai Allah masani ne ga


mabarnata (63) kace yaku ma’abota littafi ku taho zuwa ga


wata kalma wacce take daidaita tsakanin mu da ku cewa


kada mu bautawa kowa sai Allah kuma kada muyi shirka


da shi da komai kuma kada shashin mu su riki sashi


ababen bauta koma bayan Allah to in sun juya baya to kuce


musu ku shaida lallai mu musulmai ne (64) ya ku ma’abota


littafi dan me kuke jayaiyya game da Ibrahim alhalin ba’a


saukar da Attaura da Injila basai a bayan sa shin baza kuyi


hankali ba (65) ku dunnan yanzu kunyi jayaiyya a cikin


abunda kuke da ilimi to dan me kuke jayaiyya a cikin


abunda baku da ilimi akan sa kuma Allah ya san komai


kuma ku baku sani ba (66) Ibrahim bai zama bayahude ba


ko kuma banasare sai dai shi ya kasance ne mai mika wuya


ga Allah musulmi kuma bai kasance cikin mushirikai ba


(67)” suratu Ali imaran, aya ta: 59-63.


Haihuwar Annabi Isah haihuwa ce irin ta mutane, Allah ya


halicce shi a cikin mahaifa kamar yadda ya halicci sauran


halittu, ikon mahalicce ya baiyyana a cikin haihuwar sa ta


yadda ya halicce shi ba uba kamar yadda ta baiyyana ga sauran


halittu da yawa, sai Allah madaukaki ya baiyyana hakikanin


Annabi Isah amincin Allah ya tabbata a gare shi kafin halittar


sa da kuma bayan halittar sa da fadar sa madaukaki: “ kuma ka


ambata a cikin littafin Maryama lokacin da ta fita tabar


mutanen ta ta tafi wuri mai nisa (16) sai ta riki wurin buya


daga gare su sai muka aika mata da mala’ikan mu sai yazo


57


mata a siffar mutum madaidaici (17) sai tace lallai ni ina


neman tsarin mai rahama daga gare ka in kai me tsoran


Allah ne (18) sai yace lallai ni dan sako ne na ubangijin ki


dan in baki kyautar yaro mai tsarki (19) sai tace ta yaya zai


zamu inada yaro alhali babu wani mutum da ya taba ni


kuma ni ba karuwa ba (20) sai yace haka ubangijin ki ya ce


kuma hakan mai sauki ne a gare ni kuma dan mu sanya shi


ya zama aya ga mutane da kuma rahama daga gare mu


kuma hakan al’amari ne da aka riga a hukunta (21) sai ta


dauki cikin sa sai ta tafi da shi wani wuri mai nisa (22) sai


nakuda ta zo mata a gefen wani tushen bishiyar dabino sai


tace kaice na dama na mutu kafin wannan lokacin kuma in


zama abr mantawa (23) sai ya kirata daga kasanta cewa


kada kiyi bakinciki hakika ubangijin ki ya sanya idn ruwa


a kasanki (24) kuma ki girgiza tushen dabinonnan dabinai


danyu masu dadi zasu fado akan ki (25) to ki ci kuma ki sha


kuam ki ji sanyin ido idan har kin ga wani daga cikin


mutane to ki ce lallai ni nayi alwashin azumi ga mai


rahama bazan yi magana da wani mutum ba a yau (26) sai


ta zo da shi wurin mutanen ta tana dauke da shi sai sukace


ya ke Maryam hakika kinzo da wani babban al’amari (27)


ya ke iyar uwar Annabi Haruna mahaifin ki ba mutumin


banza bane kuma mahaifiyarki ba karuwa bace (28) sai tayi


nuni zuwa gare shi sai sukace ta yaya zamuyi magana da


wanda ke cikin tsumman goyo jariri (29) sai yace lallai ni


bawan Allah ne ya bani littafi kuma ya sanya ni a matsayin


Annabi (30) kuma ya sanya ne mai albarka a duk inda nake


kuma yayi mun wasiyya da sallah da kuma zakkah


matukar ina raye (31) kuma ni mai biyaiyyane ga


58


mahaifiyata kuma bai sanya ni na zama mai girman kai ba


tababbe (32) kuma aminci ya tabbata a gare ni ranar da


aka haife ni da kuma ranar da zan mutu da kuma ranar da


za’a tashe ni rayaiyye (33) wannan shi ne Isah dan Maryam


zance na gaskiya da suke kokwantu a kan sa (34) bai


kamata ba ga Allah ya riki wani a matsayin yaro tsarki ya


tabbata a gare shi idan yayi nufi aukuwar wani abu to


kawai yana ce masa ne kasance sai ya kasance (35)” suratu


Maryam, aya ta: 16-35.


Kuma Alkur’ani mai girma ya baiyyana cewa lallai daukar


cikin da Maryam tayi na Annabi Isah ya faru ne da busa daga


mala’ika Jibrilu amincin Allah ya tabbata a gare shi ta yadda ya


zo mata a siffa ta mutum kuma Allah ya umarce shi ya hura


gefen hannun rigar ta, sai iskar ta sauka zuwa farjin ta, sai ta


dau ciki nan take, Allah ya tsare ta ta zama kamar yadda


yahudawa suke tuhumarta cewa ita mazinaciya ce kuma yaran


ta dan zina ne, shi tsarkakakke ne daga haka da mahaifiyar sa


Maryam amincin Allah ya tabbata a gare ta tsarkakakkace daga


datti kuma tsarkakakka ce daga alfasha, Alkur’ani ya barrantar


da ita daga dukkan haka, kamar yadda Allah ya baiyyana haka


a cikin Alkur’ani da fadar sa: “ da kuma wcce ta tsre farjin ta


sai muka yi busa a cikin sa daga ruhin mu kuma muka


sanya ta ita da yaran ta suka zama aya ga talikai (91)”


suratul Anbiya’i, aya ta:91.


59


Alkur’ani ya yi bayanin hakikanin Isah dan Maryam amincin


Allah ya tabbata a gare shi kuma ya bada labari cewa shi bawan


Allah ne Allah yayi ni’ima a gare shi kuma ya zabe shi dan isar


da sakon sa zuwa ga bani isra’ila bayan Annabi Musa, kuma ya


baiyyana cewa mahaifiyar sa ta kasance mai gaskiya ce mai


tsarki duk irin abunda ke samun mutane to itama yana samunta


da yaran ta, su suna ci kuma suna sha kuma suna bacci su tashi


kuma suna ji zafin ciwo kuma suna kuka, to duk wanda haka


shi ne siffar sa to taya zai zama abun bauta? Kuma shi Allah


abun bauta ya tsarkaka daga dukkan wannan, kamar yadda


Allah ya bada labarin haka da fadar sa: “ Msihu dan Maryam


ba kowa bane face Manzo wanda hakika manzanni sun


gabata kafin sa kuma mahaifiyar sa mai gaskiya ce sun


kasance suna cin abinci ka duba kaga yadda muke


baiyyana musu ayoyi sannan ka duba kaga yadda ake


kirkira musu karya (75)” suratul Ma’ida, aya ta: 75.


Allah bai cancanta da mata ba ko yaro domin shi tsarki ya


tabbata a gare shi shi ne ubangijin halittu baki daya babu abun


bautawa da gaskiya sai shi kuma babu abun bauta koma bayan


sa, dan haka jingina wa Allah da yana daga cikin karya mafi


girma a gare shi, duk wani abu da ba Allah ba to halitta ne


bawan sa ne kuma yana karkashin klawar sa yana mai jayuwa a


gare shi makaskanci a gare shi yana mai tabbatar da haka kodai


da harshen sa ko kuma fidirar sa kamar yadda Allah ya


baiyyana hak da fadar sa: “ kuma sukace Allah mai rahama


yana da da (88) hakika kunzo da wani abu mai girma (89)


60


sama ta kusa ruguzowa saboda shi kuma kasa ta tsasttsage


kuma duwatsu su fadi a farfashe (90) saboda sunce Allah


yana da yaro (91) kuma baya kamata ga mai rahama ya


riki wani a matsayin yaro (92) babu wani abu a cikin


sammai da kasa face sai duk sun je wurin mai rahama suna


bayi (93)” suratu Maryam, aya ta: 88-93.


To ta yaya zai zama yanada yaro kuma yaro ba’a samun shi sai


da sakamakon abubuwa biyu daidai da juna kankankan ko


kuma kusa da juna, alhali shi Allah babu irin shi kuma babu


kama da shi, kamar yadda Allah ya baiyyana haka da fadar sa:


“ kace shi ne Allah makadaici (1) Allah wanda ake nufin sa


dan biyan bukatu (2) bai haifa ba kuma ba’a haife shi ba


(3) kuma babu wanda ya kasance daidai da shi (4)” suratul


Ikhlas, aya ta: 1-4.


Kuma kirkirawa Allah yaro maganace ba sabuwa ba ta dade


sosai kamar yadda mutum ya dade, ta fara bayana ne bayan fara


baiyanar shirka a cikin mutane, mushirikan larabawa sun yi


karyan cewa wai Allah yayi surukuntakata da aljanu sai ya haifi


mala’iku wanda suke cewa su yaran Allah ne mata- Allah ya


daukaka daga abunda suke fada daukaka mai girma- sai Allah


madaukaki yace: “ ka tambaye su shin ubangijinka nada


yara mata su kuma suna da maza (149) kuma shin mun


halicci mala’iku mata ne alhali su suna gani (150) ku saura


lallai su suna fadan haka ne daga abunda suka kirkira na


karya (151) cewa Allah ya haihu kuma lallai su makaryata


ne (152) ya zabi mata fiye da maza (153) me yasame ku ne


yaya kuke yin hukunci (154) shin baza kuyi tunani ba (155)


ko kuma kunada wata hujja ne baiyyananna (156) to kuzo


da littafin ku in har kun kasance kunada gaskiya (157)


61


kuma suka sanya dangantaka tsakaninsa da aljanu kuma


su aljanu sun san cewa lallai su za’a gurfanar da su (158)


tsarke ya tabbata ga Allah daga abunda suke siffantashi da


shi (159) sai dai bayin Allah wanda aka kubutar (160)”


suratus Saffat, aya ta:149-160.


Kuma da yawa daga cikin yahudawa da kiristoci sun jinginawa


Allah yaro saboda zalunci da kuma karya, dan koyi da wadanda


suka gabace su a fadan wannan maganar wacce lafiyaiyyen


hankali bai yadda da ita kamar yadda Allah ya baiyyana haka a


cikin Alkur’ani da fadar sa: “ kuma yahudawa sunce Uzairu


dan Allah ne su kuma kiristoci suka ce Almasihu dan Allah


ne wannan shi zantuttukan su da bakunan su suna


kwaikwayon zantuttukan wadanda suka kafurta gabanin


su, Allah ya tsine musu ta yaya suke kirkirawa Allah karya


(30) sun riki manyan malaman su da kuma masu bautan su


ababen bauta koma bayan Allah da kuma almasihu dan


Maryam kuma ba’a umarce su ba sai dai su bautawa Allah


shi kadai babu wanin abun bauta da gaskiya sai shi tsarki


ya tabbata a gareshi daga abunda suke shirka da shi (31)”


suratut Taubah, aya ta: 30-31.


Kuma hakika Alkur’ani yayi hukunci dakafurta duk wanda ya


kudurta cewa Annabi Isah dan Maryam shi Allah ne ko kuma


shi yaran Allah ne ko kuma shi ne Allah daya cikin uku, kuma


ya baiyyana cewa da’awar almasihu tsira da amincin Allah ya


tabbata a gare shi ta kasance ne dan tabbatar da tauhidi da kuma


kira zuwa gare shi da kuma rashin yin shirka da Allah dan koyi


da wadanda suka gabace shi cikin Annabawa da manzanni


kamar yadda Allah ya bada labarin haka da fadar sa: “ hakika


wadanda sukace lallai Allah shi ne Almasihu dan Maryam


62


sun kafurta kuma Almasihu yace ya ku mutanen bani


isra’ila ku bautawa Allah ubangiji na kuma ubangijin ku


lallai duk wanda yayi shirka da Allah to hakika Allah ya


haramta masa aljannah kuma makomarsa wuta kuma


azzalumai basuda wasu mataimaka (72) hakika wadanda


suka ce lallai Allah daya ne cikin uku sun kafurta kuma


babu wani abun bauta sai dai abun bauta guda daya kuma


idan basu hanu ba daga abunda suke fada to lallai azaba


mai radadi za ta shafi wadanda suka kafurta daga cikin su


(73) shin baza su tuba zuwa ga Allah ba kuma su nemi


gafarar sa kuma Allah mai yawan gafartawa ne mai jin kai


(74)” suratul Ma’idah, aya ta: 72-74.


Kuma hakika dalilai na hankali wadanda Alkur’ani ke korowa


sun kasance suna nuni akan cewa lallai Allah shi ne mahalicci


mai iko mai jujjuya al’amura ubangijin komai kuma


mamallakin sawanda yake halitta abunda yaga dama kuma yake


aikata abunda yake so, kuma ababen da suke aukuwa ta hannun


Annabi Isah amincin Allah ya tabbata a gare shi na mu’ujizozi


suna faruwa ne da umarnin Allah da ikon saba wai daga wani


umarni bane ta bangare Annabi Isah, kuma suna baiyyana cewa


lalai Annabi Isah da mahaifiyar sa basa mallakan cutarwa ko


amfanarwa ga kawunan su ko ga wanin su cikin mutane kuma


basa mallakar rayuwa ko tashi daga kabari, kuma Allah


madaukaki baya da bukatuwa a gare su ko kuma wata halitta


daga cikin halittun sa, sai dai su halittu ne suke da bukata a gare


shi dukkan su suna tsananin bukatar rahamar sa, inda Allah


madaukaki ya fada: “ hakika wadanda sukace lalai Allah shi


ne almasihu dan Maryama sun kafurta kace musu to waye


ke mallakar wani abu a wurin Allah in ya so ya halakarda


63


Almasihu dan Maryama da mahaifiyar sa da wadanda suke


ban kasa baki daya kuma abunda ke cikin sammai da kasa


da abun da ke tsakanin su na Allah ne yana halitta abunda


ya so kuma Allah mai iko ne akan dukkan komai (17)”


suratul ma’idah, aya ta: 17.


Kuma hakika Allah ya saukar da ayoyin Alkur’ani suna


tsawatar da bani isra’ila suna hana daga wuce iyaka a cikin


addinin su duka fadan wani abu game da Allah ba tare


dagaskiya ba, kuma suna baiyya cewa lallai Annabi Isah


amincin Allah ya tabbata a gare shi wanda kiristoci ke raya


cewa shi Allah ne ko kuma dan Allah ne ko kuma shi daya ne


cikin uku cewa shi mutum ne kamar sauran mutane, yana kira


zuwa ga Allah kuma yana bautan Allah kuma baya girman kai


ya zama bawa mai kaskantar da kai ga Allah da umarnin sa,


kuma duk wanda toge kuma yayi girman kai ga bautar Allah to


lalo makomar sa itace azaba da kuma dauwwama a cikin wutar


jahannama, kamar yadda Alkur’ani mai karamci ya baiyyana


haka da fadar Allah madaukaki: “ ya ku ma’abota littafi kada


ku wuce gona da iri a cikin addinin ku kuma kada ku fadi


komai game da Allah sai dai gaskiya lallai shi Almasihu


Isah dan Maryaam Manzan Allah ne kuma kalmarsa ce da


ya jefata ga Maryama kuma ruhi ne daga gare shi to kuyi


imani da Allah da manzannin sa kuma kada kuce Allah uku


ne ku hanu daga haka shi yafi alheri a gare ku lallai Allah


abun bauta ne guda daya tsarki ya tabbata a gare shi a ce


yanada yaro dukkan abunda ke cikin sammai da kasa nashi


ne kuma Allah ya isa ya zama wakili (171) Almasihu bazai


yi girman kai ba dan ya zama bawa ga Allah hakanan ma


mala’iku makusanta kuma duk wanda ya doge ya ki bauta


64


masa kuma yayi girman kai to zai tada su zuwa gare shi


baki daya (172) to amma wadanda sukayi imani kuma suka


aikata aiyuka na kwarai to zai cika musu ladan su kuma ya


kara musu daga falalar shi amma kuma wadanda suka


bijire sukayi girman kai to zai azabtar da su azaba mai


radadi kuma baza su samu wani masoyi ko mataimaki ba


koma bayan Allah (173) ya ku mutane hakika gaskiya ta zo


muku daga ubangijin ku kuma mun saukar da wani haske


zuwa gare ku mabaiyyani (174) to duk wadanda sukayi


imani da Allah kuma sukayi ruko da shi to da sannu zai


shigar da su cikin wata rahamadaga gare shi da wata irin


falala kuma zai shiryar da su wata hanya mukakkiya zuwa


gare shi (175)” suratun Nisa’i, aya ta: 171-175.


Kuma a bangare guda na masu cewa shi Allah ne kokuma


yaran Allah ne ko kuma shi Allah daya ne cikin uku hakika su


kuma yahudawa sun kasance suna zargin Annabi Isah ne


amincin Allah ya tabbata a gare shi da cewa shi rai ne na


shaidan mai sharri kuma shi mayaudari ne makaryaci, sai


Alkur’ani ya baiyyana lalacewar zancen su kuma ya baiyyana


cewa Annabi Isah Annabi ne da aka aiko me gaskiya ne cikin


abun da yake isarwa daga ubangijin sa, kamar yaddad Allah


madaukaki ya fada: “ lallai Almasihu Isah dan Maryama


manzan Allah ne kuma kalmar sa ce da ya jefa ta zuwa ga


maryam kuam ruhi ne daga gare shi to kuyi imani da Allah


da kuma manzannin sa....” suratun Nisa’i, aya ta: 171.


Sai dai wannan ruhin irin sauran ruhi ne da aka halitta an


jingina ta ne zuwa ga Allah ta fuskar darajtawa da kuma


karramawa a gare shi, kuma ita kalmar ruhi bawai wani


kebantaccen abu bane da aka kebance Annabi Isah da shi ba shi


65


kadai Annabi Adam amincin Allah ya tabbata a gare shi an


jingina ransa zuwa ga Allah dan girmamawa da karramawa a


gare shi, kamar yadda Allah ya bada labarin haka a cikin littafin


sa da fadar sa: “ lokacin da ubangijin ka ya ce wa mala’iku


lallai ni zan halicci wani mutum daga tabo (71) to idan na


daidaita shi kuma na busa masa daga rai na to ku fadi a


gareshi kuna masu sujada (72)” suratu Saad, aya ta: 71-72.


Kuma kamar yadda ya gabata wurin haihuwar Annabi Isah


amincin Allah ya tabbata a gare shi, inda Allah ya kira mala’ika


Jibril amincin Allah ya tabbat a gare shi ruhi daga Allah


madaukaki lokacin da ya aike shi zuwa wurin maryam amincin


Allah ya tabbata a gare shi dan ya bata kyautar Annabi Isah: “


kuma ka ambata a cikin littafin Maryam lokacin da ta bar


mutanen ta ta tafi wuri mai nisa (16) sai ta riki wurin buya


daga gare su sai muka aika mata da ruhin mu sai ya zo


mata a matsayin mutum madaidaici (17)” suratu Maryam,


aya ta: 16-17.


Hakanan ma Allah ya kira Alkur’ani da suna ruhi saboda


zukata na rayuwa da shi saboda irin abunda ya ke kwararo mata


na kwanciyar hankali da natsuwar zuciya haka nan kuma


al’umma na rayuwa da shi da abunda ke tabbatar msusu da


maslahohin duniya wanda ke ba kowane me hakki hakkin sa sai


rayuka tsaru da mutunci da dukiyoyi, kamar yadda Allah ya


baiyyana haka da fadar sa: “haka nan kuma mukayi maka


wahayin ruhi daga gare mu kai baka kasance kasan meye


rubutu ba ko kuma imani sai dai munsanya shi ya zama


haske muna shiryadda wanda muka gada da shi cikin bayin


mu kuma lallai kai kana shiryarwa zuwa ga hanya


madaidaiciya (52)” suratush Shura, aya ta: 52.


66


Alkur’ani mai girma ya baiyana cewa dukkan Annabawa su


daga zurriyyar Annabi Nuhu suka fito da Annabi Ibrahim


amincin Allah ya tabbata a gare su, kuma dukkan littafan da


suka sauka daga sama an saukar da su ne akan manzanni ne


daga zurriyyar wadannan Annabawan ne biyu masu karamci,


kuam yana daga cikin abunda ba kokwanto a cikin sa cewa


lallai Annabin mu Muhammad (S.A.W) yana daga cikin


zuriyyar Annabi Isma’ila dan Ibrahim amincin Allah ya tabbata


a gare su, kamar yadda Allah ya baiyyana haka da fadar sa: “


kuma hakika mun aiki Nuhu da Ibrahim kuma muka sanya


Annabci da littafi a cikin zurriyyar su su biyu daga cikin su


akwai shiryaiyyu kuma da yawa daga cikn su fasikai ne


(26)” suratul Hadeed, aya ta: 26.


Kuma yana daga cikin tushe na imani a wurin musulmai imani


da manzannin Allah madaukaki dukkan su, hakika umarni ya


zo a cikin Alkur’ani na cewa a girmama su da kuma sansu da


kwarzanta su da kuma kariya a gare su da kuma yada soyaiyyar


su a cikin mutane da kuma imani da abunda aka saukar musu


daga Allah madaukaki, kuma daga cikin wadannan manzannin


akwai Annabi Isah dan Maryam amincin Allah ya tabbata a


gare shi wanda yake da daraja mai girma da matsayi madaukaki


a wurin musulmai, Allah madaukaki yana cewa: “ kuce munyi


imani da Allah da abunda aka saukar mana da abunda aka


saukar wa Ibrahim da Isma’il da Ishaq da Ya’aqubu da


Asbad da abunda aka baiwa musa da Isah da abunda aka


baiwa Annabawa daga ubangijin su bama rarrabe wa


67


tsakanin daya daga cikin su kuma mu masu mika wuya ne


a gare shi (136) idan sunyi imani da irin abunda kukayi


imani da shi to hakika sun shiryu in kuma suka juya baya


to lallai su suna cikin tabewa da sabani kuma da sannu


Allah zai kareka daga gare su kuma shi mai ji ne masani


(137)” suratul Bakara, aya ta: 136-137.


Hakika bani sra’ila kafin aiko da Annabi musa sun kasance


masu rauni kaskantattu kuma ana bautar da su a ban kasa kamar


yadda Allah ya bada labarin haka da fadar sa: “ kuma lokacin


da muka tsiratar da ku daga mutanen Fir’auna suna gana


muku muguwar azaba suna kashe yaran ku maza kuma


suna raya yaran ku mata kuma a cikin haka akwai


jarabawa mai girma daga ubangijin ku (141)” suratul


A’araf, aya ta: 141.


Sai Allah ya yi musu baiwa na aiko da Annabi Musa amincin


Allah ya tabbata a gare shi sai Allah ya daukaka su da wannan


aikowan mai daraja sai halin da suke ciki ya canza daga


kaskanci zuwa daukaka kuma daga talauci zuwa wadata kuma


daga tozarci zuwa daraja sai suka zama sunyi nasara.


Sai zamani yayi tsawo akan mutanen bani isra’ila sai da yawan


su suka kauce daga tsarin Allah wanda Annabi Musa ya zo da


shi sai sukayi zalunci kuma sukayi barna a ban kasa sai suka


karyata kuma suka kashe Annabawa da salihai daga cikin su sai


wasu daga cikin su suka karyata tasi alkiyama da hisabi da


azaba kuma suka nutse a cikin bin san rai da ababen more


rayuwa kuma suka ci ukiyoyin mutane da barna, sai Allah ya


aiko musu da Annabi Isah dan Maryam a matsayin manzo


kuma ya sanar da shi Attaura da Injila dan ya maida su zuwa


68


tsarin ubangiji da kuma mabubbuga tatacciya ingantacciya


wanda zai kubutar da su daga abunda suke ciki na bata kamar


yadda Allah ya bada labarin haka da fadar sa: “ kuma sai biyo


da Annabi Isah dan Maryam a bayan su yana mai gaskata


abunda ya gabace shi na Attaura kuma mun bashi Injila a


cikin ta akwai shiriya da haske kuma yana gaskata abunda


ya gabace shi na Attaura kuam shiriya ne da tunatarwa ga


masu takawa (46)” suratul Ma’idah, aya ta: 46.


Annabi Isah amincin Allah ya tabbata a gare shi ya tsayu da


kiran mutanen bani isra’ila zuwa ga bautar Allah da kuma isar


musu da sakon sa da kuma yin aiki da abun da ya zo a cikin


Injila na hukunce-hukunce mafi alherin tsayuwa, Allah ya bada


labarin haka da fadar sa: “ lokacin da Isah ya zo da hujjoji


baiyyanannu sai yace hakika nazo muku da hikima kuma


zan baiyyana muku sashin abunda kuke sabani a cikin sa to


kuji tsoran Allah kuma kuyi ini biyaiyya (63) lallai Allah


shi ne ubangiji na kuma ubangijin ku to ku bauta masa


wannan itace hanya madaidaiciya (64)” suratuz Zukruf, aya


ta: 63-64.


Lokacin da Annabi Isah ya ga irin yadda suke karyata shi da


kuma kafurcewar su ga da’awar sa sai yayi kira a cikin


mutanen sa yana cewa waye zai taimake ni kuma yayi hakuri


akan abunda zai same shi saboda yada addinin Allah? sai


hawariyawa sukayi imani da shi kuma adadin su mutum goma


sha biyu ne suka kulla alkawi da shi akan zasu yda addinin


Allah da kuma kira zuwa gare shi a cikin mutanen su da kuma


hakuri akan abunda zai same su akan wannan hanyar kamar


yadda Allah ya bada labarin haka da fadar sa: “ lokacin da


Isah ya ga kafurci daga garesu sai yace waye zai taimake ne


69


saboda Allah sai hawariyawa suka ce mu ne mataimaka


Allah munyi imani da Allah kuma ka shaida cewa lallai mu


musulmai ne (52)” suratu Ali imran, aya ta: 52-53.


70


Hakika Alkur’ani ya siffata Annabi Isah amincin Allah ya


tabbata a gare shi da wasu irin siffofi da suke nuni akan darajar


wannan manzan mai karamci a wurin Allah madaukaki kuma


hakika shi ya tattaru siffa ta kamala ta dan dam wanda ke nuni


akan wannan darajar mai girma, kamar yadda Alllah ya


baiyyana haka da fadar sa: “ kuma sai biyo da Annabi Isah


dan Maryam a bayan su yana mai gaskata abunda ya


gabace shi na Attaura kuma mun bashi Injila a cikin ta


akwai shiriya da haske kuma yana gaskata abunda ya


gabace shi na Attaura kuam shiriya ne da tunatarwa ga


masu takawa (46)” suratul Ma’idah, aya ta: 46.


Kuma Alkur’ani mai karamci ya bada labari cewa lallai wannan


manzan abun karfafawa ne daga Allah madaukaki kuma abun


tsarewa ne da tsaran sa, Allah madaukaki yace: “ kuma hakika


mun baiya Musa littafi kuma muka biyo da Annabawa a


bayan sa kuma muka baiya Isah dan Maryam hujjoji


baiyyanannu kuma muka karfafa shi da mala’ika Jibrilu to


yanzu duk lokacin da wani manzo yazo muku da abunda


ranku basa so sai kuyi girman kai wasun su ku kashe su


wasun su kuma ku karyata (87)” suratul Bakara, aya ta: 87.


Kuma manzan Allah (S.A.W) ya siffanta shi da cewa shi abun


koyi ne mai kyau kuam misali ne lafiyayye wurin imani da


ibada da iklasi ga Allah madaukaki, kuma lallai saukar sa a


karshen zamani alama ne me girma cikin alamun tashin


alkiyama kamar yadda Allah ya baiyyana haka da fadar sa: “



Posts na kwanan nan

SAKO DAGA MUSULMI MAI ...

SAKO DAGA MUSULMI MAI WA'AZI ZUWA GA MUTUM KIRISTOCI

FALALAR AZUMIN KWANA ...

FALALAR AZUMIN KWANA SHIDA SHAWAL

TAKAITACCEN BAYANI MA ...

TAKAITACCEN BAYANI MAI ANFANI GA SABON SHIGA MUSULUNC

ZIKIRAI WADANDA AKE Y ...

ZIKIRAI WADANDA AKE YIN SU DA SAFE DA KUMA YAMMA