Labarai




da sunan allah mai rahama mai jin kai


Kafin mu shiga cikin bayani game da rayuwar shugaban mu


Annabi Isah amincin Allah ya tabbata a gare shi a cikin


alkur’ani ya kamata ne mu dan yi shinfida ga wannan maudu’in


da wata iyar gabatarwa wacce zamu bayyana farkon halitta a


cikinta da kuma tushen dan adam da kuma hikimar halittar su


da kuma matsananciyar bukatuwar su ga abincin ruhi wanda


yake tabbatar musu da natsuwa da kuma kwanciyar hankali,


wanda yake rikiduwa cikin aqidar tsara al’amuran su da kuma


na al’ummar su da kuma inda tunanin su ke fuskanta da


ababaen da suka fatan su samu na ingantaccen inda suka


fuskanta, hakan kuwa na cikin ababen da aka shar’anta wanda


ke tabbatar musu kiyaye hakkoki da tsare rayuka da kuma kare


mutunci da dukiya, kuma wadannan shari’u basa zuwa sai ta


hanyar wasu mutane wanda suke isar da sako daga Allah sune


Annabawa da Manzanni tsira da amincin Allah ya tabbata a


gare su.


Dukda cewa Alkur’ani mai girma shima daya ne daga cikin


littattafan da suka sauko daga sama, hakika Allah ya saukar da


shi ga Annabi Muhammad (S.A.W) cikamakin manzanni dan


ya zama shi ne littafi na karshe wanda ya sauko daga sama,


saboda haka ne ya zama littafi na duk duniya baki daya wanda


ya dace da kowane zamani da kuma lokaci kuma ya tattaro


4


dukkan dukkan abunda murtane ke bukata dan tabbatar da jin


dadin su a nan duniya da kuma lahira.


Daga cikin abunda Alkur’ani yayi bayanin sa a kwai jerin


labarin faruwar halitta da kuma samuwar wannan duniyar da


kuma ci gaban da aka samu a cikin ta, ta hanyar uslubi na gaske


wanda hankali lafiyayye ke karba da kuma fidira tatacciya da


mandiki ingantacce wanda aka tace shi daga kwaikwayo,


hakika Alkur’ani mai girma ya maida halittan wannan duniyar


da abunda ke cikin ta zuwa ga Allah shi kadai bashi da abokin


taraiyya.


Kuma hakika manzan musulunci Muhammad (S.A.W) me isar


da sako daga Allah yayi bayanin yadda aka fara halitta a cikin


hadisin Imran binil Husain inda yace: “ wasu mutane daga cikin


mutanen yaman sun zo wurin manzan Allah (S.A.W) sai suka


ce: ya manzan Allah munzo wurinka ne dan ka fahimtar da mu


addini kuma mu tambaye ka game da farkon wannan al-amari


(farkon halitta)? Sai Annabi (S.A.W) yace:” Allah ya kasance


tun farko babu komai a tare da shi kuma al’arshin sa ya kasance


akan ruwa sai ya rubuta komai a cikin lauhil mahfuzi sa’nnan


sai ya halicci sammai da kasa” “sahihu ibn Hibban”.


Sai Annabi (S.A.W) ya baiyana musu abunda yafi


mahimmancin abunda suka tambaya shi ne tabbatar da cewa


Allah na nan tuntuni shi kadai, sai yace: “Allah ya kasance


yana nan tun tuni kuma babu komai sai shi” wato ma’na Allah


ya kasance tun farkon lamari yana nan kuma babu kowa tare da


shi, sai ya fa’idantar da su cewa dadantaka ta kai tsaya ta Allah


ce shi kadai, kuma lallai wanda babu farkon samuwar sa shi ne


Allah tsarkakakke madaukaki kawai, babu wanda ke taraiyya


5


da shi cikin wannan siffan tashi cikin halittu, domin Allahn


taka bata inganta tare da tabbatar da wani abu tare da Allah


cikin samuwar sa tun farko, kuma hakika Allah ya tabbatar a


cikin Alkur’ani mai girma cewa shi samamme ne tuntuni shi


kadai da ma’ana ta bai daya wacce ta tattaro dukkan ma’anoni


dan ya baiyana ma halittun sa cewa wannan duniyar dukkanta


halitta ce, an halicce ta daga babu zuwa samuwa, sai Allah


madaukaki yace: “ abunda ke cikin sammmai da kasa suna


tasbihi ga Allah kuma shi ne mabuwayi mai hikima (1)


mulkin abunda ke cikin sammai da kasa nashi ne yana


rayawa kuma yana kashewa kuma shi mai iko ne akan


dukkan komai (2) shi ne na farko da karshe kuma na


baiyane da boye kuma shi masani ne akan dukkan komai


(3)” suratul Hadeed, aya ta: 1-3.


Allah shi ne na farko tun tuni wanda babu farkon samuwar shi,


ya kasance shi kadai ne tun farko kuma babu wata halitta tare


da shi cikin halittu, yana da dukkan siffofi na kamala da kuma


kyau wanda babu wani wanda ke kama da shi a cikin su kuma


babu wanda yake daidai da shi a cikin su cikin halittu kamar


yadda Allah ya baiyana haka cikin fadar sa madaukaki: “


mahaliccin sammai da kasa ya sanya muku mata daga gare


ku kuma ya sanya dabbobi jinsi biyu dan ya yawaita ku ta


hanyar su babu wani abu wanda yayi kama da shi kuma shi


mai ji ne mai gani (11) mabudan sammai da kasa nashi ne


yana shimfida arziki ga wanda yaga dama kuma ya


kaddara lallai shi masani ne ga dukkan komai (12)”


suratush shurah, aya ta: 11-12.


Kamar yadda Allah ya baiyana rashin yiwuwar iya siffanta shi


dari bisa dri da kuma kewawa wurin sanin sa da girman


6


wannan abun bautan ya baiyyana ga bawa wanda yake bauta


masa sai tsoransa da firgicin sa su auko a cikin zuciyar sa sai ya


kankan da kai a gare shi kuma sai ya tabbatar da rububiyyar sa


da Allahn takakar sa, Allah madaukaki ya fada yana mai bayani


akan gaskiyar wannan lamarin: “ yana sanin abunda ke gaban


sau da bayan su kuma su baza su iya kewaye shi ba da


sanin su (110) kuma fuskoki sun kaskanta ga rayaiyye


madawwami kuma duk wanda ya dauko zalunci to hakika


ya tabe (111) kuma duk wanda ya aikata aiki na kwarai


alhali shi mumini ne to baya tsoran zalunci ko kuma


tawaya (112)” suratu Daha, aya ta: 110-112.


Duk wanda ba Allah ba to fararre ne kuma halitta ne Allah ya


halicce shi da ikon sa sai ya fito da shi daga rashi zuwa


samuwa, kamar yadda Allah ya baiyyana haka cikin fadar sa: “


wannan shi ne Allah ubangijin ku mahaliccin dukkan


komai babu abun bauta da gaskiya sai shi to ta yaya ake


juyadda ku daga bin gaskiya (62) haka nan ake juyad da


wadanda suka kasance da ayoyin Allah suke karyatawa


(63) shi ne wanda ya sanya muku kasa tabbatatta da sama


ginanna kuma ya suranta ku sai ya kyautata suran


halittarku kuma ya azurta ku daga kayan marmari wannan


shi ne Allah ubangijin ku Allah yayi albarka ubangijin


talikai (64) shi ne rayaiyye babu abun bauta da gaskiya sai


shi to ku bauta masa kuna masu tsarkakae addini a gare shi


godiya ta tabbata ga Allah ubangijin talikai (65) kace lallai


ni am hane ni daga bautar abunda kuke bauta ma koma


bayan Allah lokacin da hujjoji suka zo mini daga ubangiji


na kuma an umarce ni da in mika wuya ga ubangijin talikai


(66)” suratu Gafir, aya ta: 62-66.


7


Kuma daga cikin tabbatacciyar aqidar musulmai akwai cewa


lallai Allah yana halittan abunda yaga dama kuma yana aikata


abunda yake so babu mai mayadda hukuncin sa kuma babu mai


gyara ga lamarin sa abunda ya so mai aukuwa ne kuma


umarnin sa mai kasancewa ne, kamar yadda Allah ya baiyana


haka da fadar sa: “ kuma ubangijinka yana halitta abunda


yaga dama kuma ya zabazabi ba a wurin su yake ba tsarki


ya tabbata a gare shi kuma ya daukaka daga abunda suke


shirka da shi (68) kuma ubangijin ka yana sanin abunda


zukatan su ke boyewa da kuma abunda suke baiyanawa


(69) kuma shi ne Allah babu abun bauta da gaskiya sai shi


godiya a gare shi take farko da karshe kuma hukunci nashi


ne kuma zuwa gare shi zaku koma (70)” suratul Kasas, aya


ta: 68-70.


Allah baya halitta dan wasa kuma baya barin halittun sa kara


zube, ba’a halicci wata halitta ba a wannan duniyar sai dan


wata hikima kuma ba’a halicce su ba sai dan suyi wani aiki,


kuma wannan hikimar zata iya zama mun santa kuma zata iya


zama bamu santa ba, hakika ilimin zamani ya baiyanar a


wannan zamanin irin shakuwar da halittu masu rai sukeyi da


junan su cikin abunda ake kira jerin gwanan hanyar abinc1 da


kuma shakuwar halittu da wasu wanda ba suba cikin sauran


halittu daskararu, kamar tasirin haske da duhu da kuma rana da


wata da kuma dare da yini a gare su, wannan shi ne abunda aka


sanar da mu kuma nan gaba za’a zo da sababben bincike, Allah


yayi albarka mafi kyautata halitta wanda yace: “ lallai mu mun





1


- hanyar abinci.


8


halicci kowane abu da kaddara (49)” suratul Kamar, aya ta:


49


www.islamland.com


info@islamland.com


9


Alkur’ani wanda yake maganar Allah ne yayi bayani cewa


lallai farkon duniya an halicce ta ne ba daga wani abu ba kawai


da kaddarawar Allah da kuma ikonsa ya halicce ta da kuma


umarnin sa kamar yadda Allah ya baiyana haka da fadar sa:


“wanda ya kirkiro halittan sammai da kasa kuma idan ya


hukunta faruwar wani abu to kawai yana ce masa ne


kasance sai ya kasance (117)” suratul bakara, aya ta: 117.


Kuma Annabi Muhammad (S.A.W) yayi bayani cewa lallai


ruwa shi ne farkon abunda aka halittun da Allah ya samar kuma


shi ne tushen komai cikin halittu, Allah ya halicce shi da ikon


sa ba tare da wani tushe ba kuma ya sanya shi tushe na halittar


duniya baki daya, sai yace: “ an halicci komai daga ruwa”


sahihu ibn Hibban.


Allah ya bada labari a cikin Alkur’ani cewa ya halicci sammai


guda bakwai da kassai guda bakwai a cikin kwanaki shida ba


tare da gajiya ba, sai yace: “kuma hakika mun halicci


sammai da kassai da abunda ke tsakanin su a cikin


kwanaki shida kuma babu abunda ya same mu na gajiya


(38)” suratu Qaaf, aya ta: 38.


Duk dacewa yana da iko madaukaki akan halittar su cikin


kiftawar ido ko kuma abunda yafi kusa da haka, kamar yadda


ya baiyana haka cikin fadar sa: “kuma umarnin mu bai


10


kasance ba face sai daya kamar kiftawar ido (50)” suratul


Kamar, aya ta: 50.


In aka ce: to dan me bai halicce su ba cikin sakan daya matukar


yana da iko yace musu kasane sai su kasance?


Ibn jauzy ya fada game da baiyana wasu daga cikin hikimar


hakan:


Na farko: lallai Shi yayi nufin samar da wani abu a kowace


rana wanda mala’iku zasu dinga girmama hakan da kuma


dukkan wanda yake kallon sa.


Na biyu: lallai hakan tabbaci ne na shimfida ga abunda za’a


halitta ga Annabi Adam da zuriyar sa tun kafin a halicce shi,


hakan zai fi girma wurjen girmama shi a wurin mala’iku.


Na uku: lallai gaggawa yafi karfi ta bangaren iko, shi kuma


tabbata yafi tasiri ta bangaren hikima, sai yayi nufin baiyana


hikimar sa a cikin haka, kamar yadda yake baiyana ikon sa


cikin fadar sa: “kasance sai ya kasance”.


Na hudu: lallai shi ya koyarda bayin sa tabbatatuwa, duk


abunda ya tabbata bazai gushe ba, abunda yake gushewa shi ne


yafi kamata da tabbatuwa.


Na biyar: lallai wannan jinkirin wurin halittar wani abu bayan


wani abu, yafi nisantuwa wurin tunanin cewa hakan ya auku ne


da dabi’a ko kuma da yarjejeniya.


Da kuma wata hikimar wacce Kurdaby Allah yayi masa rahama


ya ambata- a cikin tafsirin sa “ Aljam”i li Ahkamil Kur’an” sai


yace: Allah ya halicce su ne cikin kwanaki shida, saboda komai


nada lokaci a wurin sa, da wannan sai ya baiyana rashin


11


gaggawa wajan yin ukuba ga masu sabo, saboda komai yana da


lokaci n sa.


Kuma bayani filla-filla ya zo a cikin Alkur’ani game da halittar


sammai da kasa cikin fadar Allah madaukaki: kace shin yanzu


ku za ku dinga kafurce ma wanda ya halicci kasa a cikin


kwana biyu kuma ku dinga sanya masa kishiyoyi wannan


shi ne ubangijin talikai (9) kuma sai dora mata duwatsu a


samanta kuma ya sanya albarka a cikin ta kuma ya kadda


abincin ta a cikin ta a cikin kwanaki hudu dai dai ne ga


masu tambaya (10) sa’nnan sai ya daidaita a sama alhali


lokacin ita hayaki ce sai yace mata da kasa ku taho kuna


masu biyaiya ko kuma rashi biyaiya sai suka ce mun zo


muna masu biyaiya (11) sai ya kaddara su sammai bakwai


a cikin kwana biyu kuma yayi ahayi a ckin kowace sama da


al’amuranta kuma muka kawata saman duniya da fitilu da


kuma tsaro wannan kaddarawa ne na mabuwaye masani


(12)” suratu Fussilat, aya ta: 9-12.


Sayyid qutub yana cewa a cikin littafin sa “ Fi zilalil kur’an”


.....wadannan kwanaki biyu wanda Allah ya halicci kasa a cikin


su, da kuma kwanaki biyu wanda ya halicci duwatsu a cikin su


kuma ya kaddara abinci kuma ya saukar da albarka a cikin su


sai suka cika daidai cikin kwanaki hudu.....lallai su babu


kokwantu kwanaki ne cikin kwanukan Allah wanda shi ne


yasan irin su, su ba irin kwanukan mu bane na duniya.....kuma


kwanakin da aka halicci kasa a cikin su da farko, sa’annan sai


aka samar da duwatsu a cikin su, kuma aka kaddara abinci a


cikin su, su wasu kwanuka ne na daban wanda ake kiyasta su


da wani ma’auni na daban wanda basu san hi ba, sai dai mu


mun san cewa sunfi kwanakin duniya da muka sani tsawo sosai


12


kuma mafi kusan abunda zamu sawwara da shi daidai da abun


da ilimin mu ya kai na iyan adam cewa lallai su wasu lokuta ne


wamda suka gabata a ban kasa zamani bayan zamani, har ta


tabbata kuma bayan ta yayi kauri, kuma ta zama dai dai da


hadda za’a iya rayuwa a cikin ta wadda muka sani.


13


A nan ne tambaya ta hankali ke zuwa cewa: me dalilin halittar


mutane wanda Allah ya yi musu irin wannan karramawar ta


hanyar hore musu dukkan abun da ke cikin wannan duniyar?


Kuma miye dalilin halittar su?


Hakika Alkur’ani mai girma ya baiyana hikimar halittan


mutane a fili ta yadda kar ya bar fage dan lalube da hange na


kwakwale da tunane-tunane, sai Alkur’ani yayi bayani cewa


lallai su an halicce su ne dan wani abu mai girma kuma babba


saboda shi ne Allah ya halicci sammai da kasa kuma saboda shi


ne aka halicci aljannah da wuta, wannan kuwa ba komai bane


face bautar Allah shi kadai bashi da abokin taraiyya kamar


yadda Allah ya baiyana hak da fadar sa: “ kuma ban halicci


aljanu da mutane ba sai dan su bauta mini (56) bana nufin


wani arziki daga wurin su kuma bana nufin su ciyar da ni


(57) lallai Allah shi ne mai azurtawa ma’abocin karfi mai


tsanani (58)” suratuz Zariyat, aya ta: 56-58.


Rayuwar ba kamar yadda i’yan gurguzu da mulhidai suke


tunani bace cewa babu tashi bayan mutuwa kuma babu hisabi


kuma babu ukuba kawai rayuwa ce da karewa, kamar yadda


Allah ya bada labarin su da fadar sa: ´kuma suka cea ba wani


abu bane face rayuwar mu ata duniya muna mutuwa kuma


muna rayuwa kuma babu abunda ke halaka mu face


zamani kuma su basu da wani ilimi akan haka kawai su


suna zato ne (24)” suratul Jasiya, aya ta: 24.


Babu abunda yafi wahala irin ace mutum ya rayu da wannan t


tunanin kuma babu ran da tai tozarta feye da ran da ta kudurce


wannan , saboda mutum kamar yada yake da bukatuwa ta


14


kosarda burin sa na jiki a cikin a bunda yake bukata haka nan


ma bukatun sa na ruhi, kuma wannan bai yiwuwa sai ta hanyar


sanin Allah shi kuma wannan bai yuwuwa sai ta hanyar bin


abunda manzanni suka zo da shi, kuma ita kadiyyar ilhadi da


kuma inkarin tada mutane bayan mutuwa zance ne wanda ba


wannan zamanin aka fara shi ba, a a zance ne da yake ta yawo


tsakanin mutane tun da wanda suke mulhidai ne suna koyar da


ita daga wasu a’umma zuwa wasu wadanda ke bayan su dan


wanda Allah ya tayshe basirar sa daga gaskiya ya rungume ta


saboda kauda kai da yayi daga manhajin Allah da kuma


hukuntar da hankali da yayi a inda ba’a hukuntar da hankali a


cikin sa, Allah madaukaki yana cewa: “ sai muka aika da


manzo daga cikin su zuwa gare su cewa ku bauta wa Allah


baku da wani abun bauta koma bayan sa shin baza ku ji


tsoran Allah ba (32) sai manya suka ce daga cikin mutanen


sa cikin wadanda suka kafurta kuma suka karyata da


haduwar lahira kuma muka jiyar da su dadi a rayuwar


duniya wannan ba komawai bane face wani mutum daga


cikin ku yana cin irin abunda kuke ci na abinci kuma yana


shan irin abunda kuke sha (33) kuma idan har kuka yi


biyayya ga wani mutum irin ku to lallai ku hasararru ne


(34) yanzu zai dinga muku alkawari cewa lallai ku in kun


mutu kuma kuka kasance turbaya da kasusuwa wai lallai


za’a fitar da ku (35) har abada abunda yake muku alkawari


bazai faru ba (36) kawai ba wane abu bane face rauwar mu


ta duniya muna mutuwa kuma muna rayuwa kuma mu


baza’a tashe mu ba (37)” suratul muminuun, aya ta: 32-37.


Hakika mutane sun kasance a farkon halitta al’umma ne guda


daya kansu a hade ba a rarrabe ba saboda suna zaune ne a wuri


15


daya iyakantacce kuma basu da yawa sai dai bayan da yaran


Adam sukayi yawa kuma inda suke zaune yayi musu kadan sai


hakan ya tilasta ma wasun su tashi daga inda suke zuwa wasu


bangarori na ban kasa da kuma yaduwa cikin ta dan bincike da


neman arziki, kuma hakika Alkur’ani ya baiyyana wannan


hakikar zancen inda Allah madaukaki ya fada: “ kuma mutane


basu kasance ba a da face al’umma guda daya sai suka


rarrabu badan wata kalma wadda ta gabata daga ubangijin


ka ba da anyi hukunci tsakanin su cikin abunda suka


kasance suna sabani a cikin sa (19)” suratu Yunus, aya ta: 19.


Sai wannan warwatsuwar a bayan kasa ta haifar da sabanin ta


bangaren yaruka da al’au haka nan ma da kuma nisanta daga


tushen addini na farko, yana daga cikin adalcin na Allah wanda


baya zalunci da mugunta shi ne cewa baya yin azaba sai bayan


yayi gargadi ta hanyar wanda yake aikowa cikin Manzannin sa


dan suyi wa mutane bayanin ingantacciyar hanya ta gaskiya


wacce take kaiwa zuwa gare shi, sai rahamar Allah ga mutane


ta hukunta cewa bazai yi musu ukuba ba har sai ya aiko musu


da manzanni wadan da suke nuna musu hanyar shiriya, kuma


suna tsawatar da su daga bin hanyar bata, kamar yadda mukayi


bayani a baya, saboda haka ne ma babu wata al’umma da ba’a


aika mata da manzo ba da kuma sako cikin koane amani, kamar


yadda Allah madaukaki ya baiyyana haka cikin fadar sa: “


lallai mu mun aiko ka da gaskiya kana mai bushara da


kuma gargadi kuma babu wata al’umma face sai mai


gargadi ya je mata (24)” suratu Fadir, aya ta: 24.


Allah madaukaki ya kasance yana aikawa da manzanni da


Annabawa tsakanin wani lokaci zuwa wani lokaci dan su maida


mutane zuwa ga kadaita ubangijin su da kuma bauta masa


16


bayan sun kauce wa a kidar su kuma manhajin su ya samu


matsala, dukkan su tsira da amincin Allah ya tabbata a gare su


tun daga na farkon su har zuwa na karshen su da’awar su iri


daya ce wacce ta hadu akan tauhidi wanda shi ne kadaita Allah


da bauta wurin kudurcewa da zantuttuka da kuma aiyyuka da


kuma kafurce ma dukkan abunda ake bauta mawa koma bayan


sa saboda fadar Allah madaukaki: “ kuma hakika mun aika


da manzao a cikin kowace al’umma cewa ku bauta ma


Allah kuma ku nisanci dagutu daga cikin su akwai


wadanda Allah ya shiryar kuma daga cikin su akwai


wadanda bata ta tabbata a kan su kuyi tafiya a ban kasa sai


kuyi dubi kuga yaya karshen masu karyatawa take


kasancewa (36)” suratun Nahl, aya ta: 36.


Kuma wadannan manzanni Allah madaukaki yana aiko su ne


saboda kada ya zamo an samu wata hujja akan Allah ga mutane


bayan manzanni, kamar yadda Allah madaukaki ya bada labari


da fadar sa: “ manzanni ne masu bushara da kuma gargadi


saboda kada a samu wata hujja akan Allah bayan aiko da


manzanni kuma Allah mabuwayi ne mai hikima (165)”


suratun Nisa’i, aya ta: 165.


Dukda sanin cewa dukkan manzanni da annabawa sun kasance


mutane ne su kuma basuda wani abu na siffan Allahn taka,babu


wani bambanci tsakanin su da wasun su cikin mutane sai da


abunda Allah ya kebance su da shi kawai na ma’asumanci cikin


abunda suke isarwa daga gare shi da kuma abunda ya kebance


su da shi na mu’ujiza wacce take gudana ta hannayen su dan ta


zama aya ga mutanen su dan suyi imani kuma su tabbatar da


gaskiyar manzancin su da Annabtakan su, Allah madaukaki


yana cewa: “ kuma bamu aiko ba gabanin ka cikin


17


manzanni face su suna cin abunci kuma suna zuwa kasuwa


kuma muka sanya sashinku fitina ne ga sashi ko zaku iya


hakuri kuma ubangijin ka ya kasance mai hakuri (20)”


suratul Furkan, aya ta: 20.


Kuma Allah ya baiyyana mutuntakan su da kuma irin abunda


suke da shi na fidira hakika sun kasance suna da mata da kuma


zurriyya saboda kada wani yayi tunanin cewa su da ban ne da


mutane, Allah madaukaki yana cewa: “ kuma hakika mun


aika da manzanni tun gabanin ka kuma muka sanya musu


mata da kuma zuriyya kuma baya kamata ga wani manzo


yazo da wata aya sai da izinin Allah kowane abu yana da


lokaci rubutacce (38)” suratul Ra’ad, aya ta: 38.


Kuma Allah madaukaki yana cewa: “ hakika wadanda sukace


lallai Allah shi ne masihu dan Maryam sun kafurta kuma


masihu yace yaku bani isra’ila ku bautawa Allah ubamgiji


na kuma ubangijin ku lallai duk wanda yayi shirka da


Allah to hakika Allah ya haramta masa shiga aljannah


kuma makomar sa wuta kuma azzalumai basuda


mataimaka (72) hakika sun kafurta wadanda sukace lallai


Allah dayan uku ne kuma babu wani abun bauta sai dai


abun bauta guda daya kuma idan basu hanu ba daga


abunda suke cewa to lallai azaba mai radadi zata shafi


wadanda suka kafurta daga cikin su (73) shin baza su tuba


ba zuwa ga Allah kuma su nemi gafarar sa kuma Allah mai


yawan gafara ne mai jin kai (74) masihu dan Maryama ba


kowa bane face manzo wanda manzannin sun shude


gabanin sa kuma mahaifiyarsa ta kasance mai gaskiya


dukkan su biyun sun kasance suna cin abinci ka duba


yadda muke musu bayanin ayaoyi sa’annan kuma ka duba


18


yadda ake juya su (75) kace shin yanzu zaku dinga bauta


ma wani abu daban koma bayan Allah wanda baya


mallakar cutarwa ko amfanarwa gare ku kuma Allah shi ne


mai ji masani (76) kace ya ku ma’abota littafi kada ku wuce


gona da iri cikin addinin ku da abunda ba gaskiya ba kuma


kada ku dinga bin san ran wasu mutane wadanda sun bace


tun gabanin haka kuma sun batarda mutane da yawa kuma


sun bata daga hanya madaidaiciya (77)” suratul Ma’idah,


aya ta: 72-77.


Kuma basu da wani abu da ya shafi al’amuran ubangiji da


bauta, basuda ikon yin tasarrufi cikin duniya kuma basa


mallakawa kansu ko wanin su cutarwa ko amfanarwa kuma


basa mallakar mutuwa ko rayuwa ko kuma tashi daga kabari,


Allah madaukaki yana cewa yana bada labari gameda manzan


sa Annabi Muhammad (S.A.W) wanda shi ne mafi falalar


mutane kuma mafi tsarkin su: “ kace bana mallakar


amfanarwa ko cutarwa ga kaina sai abunda Allah ya so


kuma da ace nasan gaibu da na yawaita aikin alheri kuma


da ba wani abu da zai same ni na cutarwa ni ba kowa bane


face mai gargadi da bushara ga mutanen da sukayi imani


(188)” suratul A’araf, aya ta: 188.


19


Hikimar Allah da nufin sa sun zartu akan cewa zai sanya halifa


a ban kasa wanda zai raya ta kuma za’a samu yaduwa cikin


zurriyyar sa wadanda hakan da izinin Allah zai tabbatar da


abunda hikimar sa ta hukunta na raya kasa, kuma dan ta zama


gidan jarabawa da fitina a gare su, dan mai biyaiyya a cikin su


gare shi ya baiyyana cikin bayin sa kuma waye mai sabawa


kuma waye mumini sannan kuma waye zai kafurta, Allah


madaukaki yana cewa: “ kuma lokacin da ubangijin ka yace


wa mala’iku lallai ni zan sanya halifa a ban kasa sai suka ce


yanzu zaka saka a cikinta wadanda zasu yi barna a cikin ta


kuma su zubarda jini kuma alhali mu muna tasbihi a gare


ka kuma muna tsarkake ka sai yace lallai ni na san abun da


baku sani ba (30)” suratul Bakara, aya ta: 30.


Sai wannan halifan ya zama shi ne Annabi Adam amincin


Allah ya tabbata a gare shi uban mutane na karshe cikin


nau’o’in abunda Allah madaukaki ya halitta, kuma an halicce


shi ne ranar juma’a kamar yadda manzan Allah (S.A.W) ya


baiyana haka cikin fadar sa: “ mafi alherin yini da rana ta


bullo a cikin sa shi ne ranar juma’a, a cikinta ne aka halicci


Adam, kuma a cikin ta ne aka shigar da shi aljannah, kuma


a ciki ta ne aka fitar da shi daga cikin ta, kuma alkiyama


baza ta tsayu ba sai ranar juma’a” sahi hu muslim.


Saboda haka ne Allah madaukaki ya zabe ta dan ta zama ranar


idi ga musulmai a duk sati, kuma saboda darajar Adam da


matsayin sa a wurin Allah sai ya umarci mala’ikun sa da suyi


masa sujada dan matsayin sa da darajta shi da kuma karamci a


wurin halittar sa kuma ya yi busa a cikin sa daga ruhin sa sai


20


dukkan mala’iku suka yi biyaiyya ga umarnin Allah sai dai


Iblis wanda ya saba wa Allah kuma yaki yin sujada dan hassada


da kuma girman kai daga kansa ga wannan abun halittan wanda


Allah ya fifita shi a kan sa, kamar yadda Allah ya bada labarin


haka da fadar sa:” lokacin da ubangijin ka yace wa mala’iku


lallai ni zan halicci wani mutum daga turbaya (71) idan na


daidaita shi kuma na busa masa daga rai na to ku fadi a


gare shi kuna masu sujada (72) sai mala’iku dukkan su


sukayi sujada (73) sai dai ibilis ne yayi girman kai kuma ya


kasance cikin kafirai (74) sai yace ya kai ibiis meye ya


hanaka yin sujada ga abunda na halitta da hannaye na biyu


shin kayi girman kai ne ko kuma ka kasance ne cikin


madaukaka (75) sai yaceni na fi shi alhri ka halicce ni daga


wuta shi kuma ka halicce shi daga turbaya (76) sai yace to


ka fita daga cikin ta domin lallai kai tsinanne ne (77) kuma


lallai akwai la’anta ta akan ka har zuwa ranar sakamako


(78) sai yace ya ubangiji to ka jinkir ta mun har zuwaranar


da za’a tada su (79) sai yace lallai kai kana cikin wadanda


za’a yi musu jinkiri (80) har zuwa ranar da aka sa lokaci


sananne (81) sai yace to saboda buwayarka lallai ni sai na


batar da su baki dayan su (82) sai dai bayin ka a cikin su


wadan da aka tsiratar (83) sai yace magana ta gaskiya


kuma wallahi gaskiya nake fada (84) wallahi lallai sai na


cika wutar jahannama da kai da kuma wadanda suka bi ka


cikin su baki daya (85)” suratu Saad, aya ta: 71-85.


Sai halittan sammai da kasa ya zama shinfida ne na halittar


Adsam amincin Allah ya tabbata a gare shi wanda hikimar


Allah ta hukunta yaduwar mutane zata fara ne daga gare shi da


kuma matar sa Hauwa’u, sai Allah madaukaki yayi bayani


21


cewa wannan duniyar da dukkan abbunda ke cikin ta an yi su


ne dan dan Adaman halicce su ne dan ya amfana da abunda


Allah ya sanya a cikin ta na alheri kuma dan ya zama fili e mai


fadi a gare shi wanda ta hanyar sa ne zai iya gano abunda zai


tabbatar masa da rayuwa ta karamci, inda Allah madaukaki


yace: “ ashe baku gani ba cewa lallai Allah ya hore muku


abunda ke cikin sammai da kasa kuma ya cika muku


ni’imar sa a gare ku ta baiyyane da boye kuma daga cikin


mutane akwai wadanda suke jayaiyya game da Allah ba


tare da wani ililimi ba ko kuma shiriya ko kuma wani littafi


mai haskakawa (20)” suratul Luqman, aya ta: 20.


Kuma dan ya zama wuri mai fadi dan tunani da kuma lura


wadanda suke kaiwa zuwa ga sanin wannan mahaliccin mai


girma wanda ya cancanta da bauta kamar yadda Allah ya


baiyyana haka da fadar sa: “ lallai a cikin halittar sammai da


kasa da kuma sabawar dare da rana akwai ayoyi ga masu


hankali (190) wadanda suke ambatan Allah a tsaye da


zaune da kuma kan gefen jikin su kuma suna tunani cikin


halittar sammai da kasa suna cewa ya ubangijin mu baka


halicci wannan dan wasa ba tsarki ya tabbata a gare kato


ka kare mu daga azabar wuta (191) ya ubangijin mu lallai


kai duk wanda ka shigar da shi wuta to hakika ka tabar da


shi kuma azzalumai basu da mataimaka (192) ya


ubangijinmu lallai u munji wani mai kira yana kira zuwa


ga imani cewa kuyi imani da ubangijin ku sai mukayi imani


ya ubangijinmu to ka gafarta mana zunuban mukuma ka


kankare mana kurakuran mu kuma ka kashe mu tare da


masu biyiaiyya (193) ya ubangijinmu kuma ka bamu


abunda kayi mana alkawari da shi ta hanyar manzannnin


22


ka kuma kada ka tozarta mu ranar alkiyama lallai kai baka


saba alkawari (194)” suratu Ali imran, aya ta:190-194.


23


Bayan shaidan ya sabawa ubangijin sa yaki yin sujada ga Adam


sai Allah ya rubuta masa tabewa da kuma fitarwa daga


aljannah, sai shaidan yayi alkawarin batar da iyan adam da


kuma kautar da su daga hanya ingantacciya saboda hassadar da


ke ransa kamar yadda yayi hassada ga babansu Annabi Adam


kamafin haka, kamar yadda Allah ya bada labarin haka da fadar


sa: “ lokacin da ubangijin ka yace wa mala’iku lallai ni zan


halicci wani mutum daga busashshen tabo mai canzawa


(28) to idan na daidaita shi kuma na busa masa daga ruhi


na to ku fadi a gare shi kuna masu sujada (29) sai mala’iku


dukkan su sukayi sujada baki daya (30) sai dai iblis shi yaki


ya zama tare da masu sujada (31) sai yace ya kai iblis me ya


same ka baka tare da masu sujada (32) sai yace ban zama


mai sujada ba ga wani mutum wanda ka halicce shi daga


tabo baki busashshe mai caccanzawa (33) sai yace to ka fita


daga cikinta domin lallai kai korarre ne (34) kuma kai lallai


akwai tsinuwa akan ka har zuwa ranar sakamako (35) sai


ya ce ya ubangiji to ka mun jinkiri har zuwa ranar da za’a


tada su (36) sai yace lallai kai kana cikin wadanda za’ayi


wa jinkiri (37) har zuwa ranar da aka sa lokai sananne (38)


sai yace ya ubangiji saboda batar dani da kayi sai na


kawata musu duniya kuma wallahi lallai sai na batar dasu


baki daya (39) sai dai bayinka a cikin su wadan da ka


kubutar (40) sai yace wannan itace hanya ta madaidaiciya


(41) lallai bayina baka da wani iko akan su sai dai wadanda


suka bika cikin batattu (42) kuma lallai wutar jahannama


24


itace inda akayi musu alkawari dukkan su (43)” suratul Hijr,


aya ta: 28-43.


Kuma hakika farkon gabar da iblis yake yiwa Adam ta fara ne


cikin a gidan aljannah tun farkon fara halittar shi, sai ya fara


dakun sa yana kulla masa makirci kuma yana rudar shi da yaci


daga wannan bishiyar da Allah ya hane shi ci daga gare ta dan


ya samu ya fitar da shi da matar sa daga cikin ta da kuma irin


ni’imar da suke cikin ta, sai shaidan ya samu damar batar da


Adam amincin Allah ya tabbata a gareshi har sai da Adam yaci


wannan bishiyar sai daga baya yayi nadama akan wannan


sabon da yayi kuma ya tabbatar da kuskuran sa sai ya tuba


kuma ya nemi gafarar Allah sai Allah ya karbi tubar sa, to


sakamakon wannan laifin sai aka fitar da shi daga aljannah da


matar shi kuma aka saukar da su zuwa kasa kamar yadda Allah


ya baiyyana haka da fadar sa: “ kuma lokacin da mukace wa


mala’iku kuyi sujada ga Adam sai sukayi sujada sai dai


Iblis ne yaki yin sujada (116) sai mukace ya Adam lallai


wannan makiyin ka ne da matar ka to kada ku yadda ya


fitar da ku daga aljannah sai ku tabe (117) lallai kai baza


ka ji yunwa ba a cikinta kuma baza kayi tsiraici ba (118)


kuma lallai kai baza ka ji kishi ba a cikinta kuma baza ka


yi walha ba (119) sai shaidan ya samai wasiwasi sai yace ya


kai Adam shin bazan nuna maka wata bishiya ba ta


dawwama da kuma wani irin mulki da baya yanke wa (120)


sai suka ci daga gare ta sai al’aurar su ta baiyana a gare su


sai suka fara boye ta da ganye na aljannah kuma sai Adam


ya saba wa ubangijin sa sai ya bace (121) sa’annan sai


ubangijin sa ya zabe shi sai ya karbi tubarsa kuma ya


shirya shi (122) sai yace ku fita daga cikin ta dukkan ku


25


sashinku yana makiyi ga sahi to idan shiriya tazo muku


daga gare ni to duk wanda yabi shiriya ta to bazai bata ba


kuma bazai tabe ba (123) kuma duk wanda ya kauda kai


daga ambato na to lallai shi yana da wata irin rayuwa ta


kunci kuma zamu tada shi ranar alkiyama makaho (124)


sai yace ya ubangiji dan me ka tada ni makaho alhali da na


kasance ina gani (125) sai yace hakannan ayoyin mu suka


zo maka sai ka manta da su to haka nan kaima yau za’a


manta da kai (126) kuma haka nan muke sakawa duk


wanda ya ketare iyaka kuma bai yi imani da ayoyin


ubangijin sa ba kuma lallai azabar lahira tafi tsanani kuma


tafi dauwama (127)” suratu Daha, aya ta: 116-127.


Bayan karni goma daga sauko da Iblis daga aljannah zuwa ban


kasa saboda sabawa umarnin Allah madaukaki da yayi na kin


yin sujada ga Adam kuma shima Adam aka sauko da shi daga


aljannah saboda sabawa umarnin Allah da yayi na cin bishiyar


da aka hana shi ci daga gare ta, sai sabani da shirka da kuma


ninsanta daga manhajin Allah da ya tsara wa Adam da zuriyyar


sa suka auku, wanda ke tabbatar musu da jin dadi a gidaje biyu


na duniya da lahira, saboda farkon manzanni bayan Adam shi


ne Nuhu amincin Allah ya tabbata a garesu wanda a cikin


mutanen sa ne shirka ta fara baiyana sai aka aike shi zuwa gare


su dan ya maida su zuwa manhajin Allah, Allah madaukaki


yana cewa yana mai hikaito da’awar Annabi Nuhu ga mutanen


sa: “ sai Nuhu yace ya ubangiji lallai su sun saba mini kuma


sun bi wanda bazai kara musu komai ba a cikin dukiyar su


da yaran su sai dai hasara (21) kuma sunyi makirci makirci


mai girma (22) kuma suka ce kada ku bar ababen bautar


ku kuma kada ku bar Wuddu da Suwa’a da Yagusa da


26


Ya’uka da Nasra (23) kuma hakika sun batar da mutane da


yawa kuma kada ka karawa azzalumai sai dai bata (24)


saboda sabun da sukeyi ne aka nutsar da su a cikin ruwa


sannan za’a sa su a cikin wuta kuma baza su samu wasu


masu taimaka musu ba koma bayan Allah (25) kuma


Annabi Nuhu yace ya ubangiji kada ka bar wani gida na


kafiri a ban kasa (26) domin lallai kai in ka kyale su to zasu


batar da bayin ka kuma baza su dinga haihuwa ba sai


fajirai kafurai (27) ya ubangiji ka gafarta mini da iyayena


da duk wanda ya shiga gidana yana mumini da muminai


maza da mata kuma kada ka kara wa kafurai sai dai


halaka (28)” suratun Nuh, aya ta: 21-28.


27


Mutane suna da bukatar manzanni da kuma karantar war su irin


yadda suke da bukata ga abinci da abin sha, su suna da


bukatuwar su dan su san mahaliccin su ta hanyar su kuma dan


karantarwar su ta zama hanya ta gyaran rayuwar su da kuma


haskaka zukatan su da kuma shiryar da kwakwalen su, kuma


dan su san inda zasu dosa a cikin rayuwa ta sanadiyyar su da


kuma alakar su da rayuwa da abunda ke cikin ta, ta yadda baza


su kauce ba su auka cikin alfasha da zunubai kuma dan su san


hakkin su da kuma abunda ya wajaba a kan su ta fuskar


mahaliccin su da kawunan su da kuma mutanen da ke kewaye


da su.


Ibn alkayyim yana cewa yana mai baiyyana wannan lamari:


kuma daga nan ne zaka san irin matsananciyar bukatar bawa


zuwa ga sanin manzannin cewa ta wuce kowace bukata, da


kuma abunda yazo da shi, da gaskata shi cikin abunda ya bada


labarin shi, da yi masa biyayya cikin abunda ya bada umarni,


domin kuwa lallai babu wata hanya ta jin dadi da rabauta a


duniya da kuma lahira sai ta hanyar manzanni, kuma babu wata


hanya ta sanin kyawawa daga munana filla-filla sai ta bangaren


su, kuma ba’a samun yaddar Allah ko kadan sai ta hannun su,


abu mai kyau na aiyuka da zantuttuka da halaye ba komai bane


face shiryarwar su da kuma abny da suka zo da shi, su ne


ma’auni mai rinjaye, wanda da aiyukan su da zantuttakan su da


halayen su ne ake auna halaye da aiyuka, kuma da bin su ne


shiryaiyyu suke banbanta da batattu, bukata zuwa gare su tafi


bukatuwar gangan jiki zuwa ga ruhin sa, da bukatauwar ido


28


zuwa ga hasken sa, da bukatuwar ruhi zuwa ga rayuwar sa, duk


wata irin bukatuwa da matsantuwa da za’a kwatanta to


bukatuwar bawa zuwa ga manzanni tafi tsanani sosai, meye


tunanin ka da wanda idan shiriyar sa ta kubce maka da kuma


abunda ya zo da shi ko da da kiftawar ido ne zuciyar ka zata


baci, kuma ta zama kamar kifi idan ya bar cikin ruwa aka jefa


shi cikin kaskon suya, to halin da bawa zai samu kansa idan


zuciyar sa ta rabu da abunda manzanni suka zo da shi kamar


irin wannan halin ne kai yama fi haka tsanani sai dai babu mai


jin hakan sai dai zuciya rayaiyya.


29


Lallai manzanci da Annabci kyauta ce ta ubangiji da kuma zabi


na Allah kuma tagomashi ne daga ubangiji Allah yana yin


kyautar sa ga wanda yaga dama cikin bayin sa bata da alaka da


dangantaka ko alfarma ko daraja, Allah masani ne mai hikima a


inda yake sanya manzancin sa, inda Allah madaukaki yake


cewa: “ ya ku mutane an buga wani misali sai ku saurare


shi lallai wadanda kuke kira kuna bauta musu koma bayan


Allah baza su iya halittan kuda ba koda sun tarun masa ne


kuwa kuma idan kuda ya fisgi wani abu a wurin su baza su


iya kwato shi daga wurin shi ba me nema da wanda ake


nema duk masu rauni ne (73) basu girmama Allah ba


yadda ya kamata su girmama shi ba lallai Allah mai karfi


ne mabuwayi (74) Allah yana zaban manzanni daga cikin


mutane da mala’iku lallai Allah mai ji ne mai gani (75)”


suratul hajj, aya ta: 73-75.


Shi yasa bai kamata ba ayi wa Annabi Muhammad (S.A.W)


hassada ba kamar yadda akayi wa Annabi Isah hassada kafun


haka ta bangaren bani isra’ila, domin ita kamar yadda mukayi


bayani ne kyauta ce daga Allah yana yin ta ga wanda ya ga


dama, Allah madaukaki yana cewa: “ shin ko suna yi wa


mutane hassada ne akan abunda Allah ya basu na falalar sa


to hakika mun baiwa mutanen gidan Annabi Ibrahim littafi


da hikima kuma mun basu mulki mai girma (54)” suratun


Nisa’i, aya ta: 54.


Kuma manzannin Allah amincin Allah ya tabbata a gare su


matsayin su da darajarsu sun banbanta su ba daidai suke ba ta


30


wurin falala kuma hakan falala ne daga Allah yana bada shi ga


wanda ya so cikin bayin sa, Allah madaukaki yana cewa: “


wadannan manzanni ne mun fifita sashin su akan sashe


daga cikin su akwai wanda Allah yayi wa magana kuma ya


daga darajar wasun su kuma mun baiwa Isa dan Maryama


ayoyi baiyanannu kuma mun karfafa shi da ruhi mai tsarki


inda Allah ya ga dama da wadanda suke bayan su basuyi


kashe-kashe ba bayan hujjoji sun zo musu sai dai su sunyi


sabani daga cikin su akwai wadanda sukayi imani kuma


daga cikin su akwai wadanda suka kafurce kuma da Allah


ya ga dama da basyi yake-yake ba sai dai Allah yana aikata


abunda yake so ne (253)” suratul bakara, aya ta “ 253.


31


Shi ne na farkon manzanni, Allah ya aiko shi bayan mutanen


shi sunyi shirka kuma halin su ya baci, kuma suka manta da


tushen shari’ar Allah wacce ya saukar wa Annabi Adam, sai


suka koma bautan gumaka, kamar yadda Allah ya baiyana


hakan da fadar sa: “lallai mu mun aika da Nuhu zuwa ga


mutanen sa cewa ka yi gargadi ga mutanen ka tun kafin


wata azaba mai radadi ta zo musu (1) sai yace ya ku


mutane na lallai ni mai gargadi ne a gare ku mabiyyani (2)


ku bauta wa Allah kuma kuji tsoran sa kuma kuyi mun


biyaiya (3) zai gafarta muku zunuban ku kuma zai muku


jinkiri har zuwa wani lokaci na musamman da aka aje lallai


lokacin da Allah yasa in yazo to ba’a jinkirta shi da kun


kasance kuna da sani (4)” suratu Nuh, aya ta: 1-4.


Sun riki gumaka guda biyar na su, sun kasance suna nufin su da


bauta kuma suna bauta musu koma bayan Allah: (Wudu –


Suwa’u – Yagusu – Ya’uqu – Nasra), Allah yayi bayanin su a


cikin Alkur’ani da fadar sa: “kuma suka ce kada kubar


ababen bautar ku kuma kada ku sake ku bar Wuddu da


Suwa’u da Yagusu da Ya’uqu da Nasra (23)” suratun Nuh,


aya ta:23.


Kuma shi Annabi Nuhu amincin Allah ya tabbata a gare shi ya


kasance mai tsoran Allah ne mai gaskiya, ya kira mutanen sa da


da hakuri da kuma tabbatuwa, kuma yabi hanyoyi daban daban


wurin kiran mutanen sa wadanda sukayi masa isgili kuma suka


karyata shi,kamar yadda Allah ya baiyana haka da fadar sa: “


32


sai yace ya ubangiji lallai ni na kira mutane na dare da


rana (5) amma kiran da nake musu bai kara musu komai


ba sai dai guduwa (6) kuma lallai ni a duk lokacin da nake


kiran su dan ka gafarta musu sai su sanya yatsun su a cikin


kunnuwan su kuma su nannada tufafin su kuma su kangare


kuma suyi girman kai girman kai (7) sa’annan lallai ni na


kira su a baiyane (8) sannan lalli ni na baiyana musu kuma


na musu a sirrance sirrantawa (9) sai nace musu ku nemi


gafarar ubangijin ku domin lallai shi ya kasance mai yawan


gafara ne (10)” suratu Nuh, aya ta: 5-10.


Ammma duk da haka ya ci gaba da kiran su tsira da amincin


Allah ya tabbata a gare shi kuma duk lokacin da ya kara


dagewa wajan kiran su da tunasar da su sai su kara kaimi wajen


kauda kai da dogewa akan barna, sai ya cigaba da yin hakuri a


kan su kuma ya ci gaba da kiran su zuwa ga addinin Allah sai a


ka samu mutane kadan suka bi shi, su kuma kafurai sai suka ci


gaba cikin kangarewar su sai Allah ya hana musu ruwan sama


sai Annabi Nuhu ya kira su zuwa ga yin imani dan Allah ya


dauke musu wannan azabar sai sukayi imani sai Allah ya dage


musu wannan azabar sai dai su daga baya sun koma cikin


kafurcin su, kuma yaci gaba da kiran su har tsawan shekaru dari


tara da hamsin sai daga baya Annabi Nuhu ya kai koke zuwa ga


ubangijin sa cewa mutanen sa sun saba masa kuma sun bi


batattu daga cikin su, sai ya roki ubangijin sa kuma yace:


“kuma Annabi Nuhu yace ya ubangiji kada ka bar wani


gida na kafiri a ban kasa (26) domin lallai kai in ka kyale su


to zasu batar da bayin ka kuma baza su dinga haihuwa ba


sai fajirai kafurai (27) ya ubangiji ka gafarta mini da


iyayena da duk wanda ya shiga gidana yana mumini da


33


muminai maza da mata kuma kada ka kara wa kafurai sai


dai halaka (28)” suratun Nuh, aya ta: 26-28.


Sai Allah ya karba addu’ar sa sai Allah ya umarce shi da gina


jirgin ruwa- kuma dama shi kwararre ne a bangaran kafintanciwannan farkon shiri ne na tsiratar da shi shi da wadanda suke


tare da shi cikin mutanen sa daga ruwan dufana wanda zai


wanke kasa daga kafurci, kuma aka ce ya dauki jinsi biyu na


kowane nau’in abu, sai ruwan dufana ya zo hakan kuwa ya


auku ne ta yadda Allah yayi umarni ga sama da tayi ruwa ita


kuma kasa ta fitar da idanun ruwa sai Allah ya nitsar da su baki


dayan su, kamar yadda Allah ya baiyana haka da fadar sa: “


mutanen Nuhu sun karyata gabanin su sai suka karyata


bawan mu kuma sukace mahaukaci ne kuma suka yi mai


tsawa (9) sai ya roki ubangijin sa yace lallai ni an rinjaye ni


to ka kawo mun agaji (10) sai muka bude kofofin sama da


wani rirn ruwa mai bubbugowa mai yawa (11) kuma muka


bude kasa da idanu ruwa sai ruwan ya hadu akan wani


lamari wanda an riga an kaddara shi (12) kuma muka


dauke shi akan jirgin ruwa ma’abociya katakai da kusoshi


(13) tana gudana kan kulawar mu wannan sakamako ne ga


wanda suka kasance sun kafurce (14) kuma hakika mun


barta aya ce shin ko akwai mai tunani (15)” suratul Kamar,


aya ta: 9-15.


Kuma Annabi anuhu tsira da amincin Allah ya tabbata a gare


shi ya kasance daga gare shi ne da yaran sa guda uku wadanda


suke tare da shi sauran mutane suka yadu, su ne: Saam (baban


larabawa da farisawa da rumawa), Haam: (baban bakake da


ifranjawa da kibtawa da indiyawa da sindawa), Yafis: (baban


turkawa da chinisawa da sakalibawa da ya’juju da ma’juju).


34


Maji dadin Allah baban Annabawa an haifa masa Isma’il da


Ishaq bayan ya tsofa amincin Allah ya tabbata a gare su, su ne


wadanda aka samu mafi yawancin Annabawa daga cikin


zurriyar su, kamar yadda Allah ya baiyyana haka da fadar sa: “


godiya ta tabbata ga Allah wanda ya bani Isma’il da Ishaq


bayan na manyanta lallai ubangiji na mai karbar addu’a ne


(39) ya ubangiji ka sanya ni mai tsaida sallah da kuma


zurriya ta ya ubangiji ka karbi addu’a ta (40)” suratu


Ibrahim, aya ta: 39-40.


Allah ya zabe shi da manzancin sa kuma ya fifita shi akan da


yawa daga cikin halittun sa, kuma Annabi Ibrahim amincin


Allah ya tabbata a gare shi ya kasance yana rayuwa a tsakanin


wasu mutane da ke shirka da Allah kuma suke bauta wa taurari,


kamar yadda Allah ya bada labarin haka da fadar sa: “ kuma


lokacin da Ibrahim yace wa mahaifin sa Azara shin yanzu


zaka riki gumaka a matsin ababen bauta lallai ni ina ganin


ka da mutanen ka kuna cikin wata irin bata baiyananna


(74) kuma haka nan muka nuna wa Ibrahim mulkin


sammai da kasa dan ya zama cikin masu yakini da tabbaci


(75) lokacin da dare ya shigo masa sai yaga wani tauraro


sai yace wannan shi ne ubangiji na lokacin da ya gushe sai


yace ni bana san masu gushewa (76) lokacin da yaga wata


ya fito a fili sai yace wannan shi ne ubangiji na lokacin da


ya gushe sai yace in dai har ubangiji na bai shiryar da ni ba


to lallai ni zan kasance cikin mutane batattu (77) lokacin da


yaga rana ta fita a fili sai yace wannan shi ne ubangiji na



Posts na kwanan nan

FALALAR AZUMIN KWANA ...

FALALAR AZUMIN KWANA SHIDA SHAWAL

TAKAITACCEN BAYANI MA ...

TAKAITACCEN BAYANI MAI ANFANI GA SABON SHIGA MUSULUNC

ZIKIRAI WADANDA AKE Y ...

ZIKIRAI WADANDA AKE YIN SU DA SAFE DA KUMA YAMMA

BIDI’AR ‘YAN SHI’A A ...

BIDI’AR ‘YAN SHI’A A RANAR ASHURA