Labarai

1


Jerin Littafan Shi’a Na 7


Zuwan


Shi’a


Nijeria


Umar Labxo


2


بسم الله الرحمن الرحيم


Asalin yaxuwar Shi’a a Nijeria ya fara a tsakanin matasa, yawanci ‘yan


makaranta, masu aikin yaxa addinin Musulunci waxanda aka san su da sunan ‘Yan


Uwa Musulmi. Wannan suna fassara ce kai tsaye ta sunan wata Qungiya,


Al’ikhwanul Muslimun, wacce Imam Hassan Albanna ya kafa a qasar Masar a


cikin shekarun 1930. Babbar manufar qungiyar shi ne mayar da Musulmi zuwa ga


hukunce – hukuncen Musulunci a kafatanin fagagen rayuwarsu wanda ya haxa da


fagen siyasa, tattalin arziqi, tarbiya da zamantakewa da kuma dangantakarsu da


waxanda ba Musulmi ba. Qungiyar ta yaxu a yawancin qasashen Musulmi ciki har


da Nijeriya.


Tare da qungiyar ‘Yan Uwa Musulmi akwai qungiyar Xalibai Musulmi ta


Nijeriya, watau M.S.S. wacce aka kafa ta shekaru 50 da suka wuce. Waxan nan


qungiyoyi biyu sashen su ya haxe da sashe kuma suna yin nashaxinsu a jami’o’i da


manyan makarantun qasar nan. A wani yayi nashaxinsu yana shafar ‘yan


makarantun sakandare ta hanyar tarukan horaswa da suke shiryawa xaliban


qananan makarantu a lokacin hutu. Masu shagala da aikin da’awa a qarqashin


inuwar waxan nan qungiyoyi yawancinsu matasa ne maza da mata masu karatun


fannonin ilmi dabam – daban, kamar Kimiya da Likitanci da Tattalin Arziki, amma


kaxan ne daga cikinsu suke karanta Musuluncin kansa. Wannan ya sa, koda yake


suna da son Musulunci ga kuma gafin quruciya, amma suna da qarancin ilmin


addini. Saboda haka a lokacin da Shi’a ta shigo qasar nan, a kan doron juyin juya


hali na Musulunci (!) na qasar Iran da kirarinsa mai xaukar hankali na kafa


jumhuriyar Islama da zartar da hukunci da Shari’a, sai yawancin waxannan samari


3


suka hau jirgin Shi’a da tikitin juyin Islama. Daga cikin waxan nan samari akwai


Malam Ibrahim Ya’aqub Alzakzaki.


Alzakzaki da Yaxuwar Shi’a


Sunan Zakzaki ya fara fitowa a farkon shekarun 1980 lokacin da, bayan


kammala karatunsa a fannin Tattalin Arziqi daga Jami’ar Ahmadu Bello ta Zaria,


ya qi ya je aikin bautar qasa, watau N.Y.S.C. saboda, kamar yadda ya ce, shi ba ya


bautawa qasa; Allah kaxai yake bautawa. Duk da raunin wannan magana da rashin


fahimtar addini da take nunawa a fili, wannan mataki da Zakzaki ya xauka ya ba


shi farin jini kuma ya mayar da shi tamkar wani gwarzo a idanun matasa waxanda


wutar son addini take ci a zukatansu amma qwaqwalensu sun yi duhu duxum


saboda jahilci. Zakzaki ya wayi gari ana lasafta shi daga cikin shugabannin xalibai


da matasa masu sha’awar addini.


Ba’a daxe da haka ba, sai mahukuntan qasar Iran masu bin tafarkin Shi’anci,


a cikin qoqarinsu na neman goyon bayan Musulmin duniya musamman a kan


yaqinsu na shekaru takwas da qasar Iraqi, suka riqa gayyatar malamai da matasa


masu sha’awar addini daga ko wane vangare na duniyar Musulmi domin su halarci


bikin shekara – shekara da suke yi don tunawa da nasarar juyin juya halinsu.


Zakzaki na daga cikin waxanda aka gayyata daga Nijeriya.


Mahukuntan Iran waxanda suke xaukar nauyin baqinsu zuwa da komowa,


suna nunawa baqin karamci, suna girmama su ainun kuma ga alama suna ba su xan


goro a matsayin sallama. Banda wannan, suna qoqarin cusa wa baqin nasu aqidar


Shi’anci ta hanyar laccoci, muhalarori, tarukan qarawa juna sani da kuma kyautar


littafai masu yawa. Ga alama ta wannan hanya sun yi nasarar ribace wasu da


shigar da su tafarkinsu kamar Zakzaki, wasu kuwa sun gane makircinsu sai suka


4


raba gari da su. Daga cikin waxanda aka gayyata daga Nijeriya kuma amma ba’a


yi nasarar janye su zuwa Shi’anci ba akwai Malam Abubakar Tureta daga Kaduna


da Malam Abubakar Jibril daga Sakkwato wanda ya zama a sahun gaba wajen


yaqar Shi’anci a Nijeriya.


Alaqar Zakzaki da Iran ta ci gaba da yin qarfi a hannu guda, a xaya hannun


kuma shahararsa ta bunqasa, kuma magoya bayansa suka qara yawa, a yayin da ya


buxe ressa a yawancin jihohin arewacin qasar nan, yana kira da sunan


gwagwarmayar kafa hukuncin Musulunci da yaqar waxanda ya kira xagutai.


Mabiyan Zakzaki sun yi ban gaskiya da shi ainun, sun yarda da


shugabancinsa har suna ganin wanda duk bai xauke shi a matsayin shugaba ba


kamar shi ba Musulmi ba ne, suna cewa wanda ya mutu bai yi masa mubaya’a ba


to ya mutu mutuwar Jahiliya. Shi kuwa ya yi amfani da amince masa da suka yi,


ya riqa gabatar musu da koyarwar Shi’a da aqidojinsu sannu a hankali kuma koda


yaushe aka tsorata su da kusancin shugabansu da Iran, sai ya ba su tabbacin cewa


shi babu abinda ya haxa shi da Iran sai gwagwarmaya da yaqar Amurkawa da


Yahudawa da xagutai. Amma kuma a hannu guda, Zakzaki ya ci gaba da shigo da


alamu da bukukuwan Rafilawa kamar babbaqun rawuna, bikin Ashura, da


sauransu.


Haka nan gogan naka ya ci gaba da taqiya, yana yaudarar almajiransa da


magoya bayansa har ranar da dubunsa ta cika. Wata mujalla daga cikin irin


mujallun da ake bugawa a qasar Iran ana aikowa da su Nijeriya ta buga wata


maqala wacce a cikinta aka ci zarafin Sahabin Annabi (SAW) mai shuhura watau


Abu Huraira (R.A). Wannan ya tayar da hankalin wasu daga cikin mabiyan


Zakzaki inda suka nemi ya fito fili ya la’anci wannan maqala amma ya qiya.


Wannan shi ya buxe idanun da yawa daga cikin mabiyansa, waxanda a da jahilci


5


da bin son zuciya ya rufe idanun nasu. Daga nan aka samu wani reshe a cikin


mabiyan Zakzaki wanda ya yi ta matsawa malamin lamba a kan ya fito fili ya


bayyana matsayinsa dangane da ko Shi’a yake yi ko a’a. Zakzaki ya ci gaba da


noqewa har dai daga bisani tusa ta qurewa bodari kuma gaskiya ta yi halinta. A


cikin shekarar 1995 aka yi uwar watsi bayan wani taron qure qarya da aka yi wa


Zakzaki a hedkwatarsa a Zaria. Mabiyansa da yawa, ciki har da manyan


almajiransa, suka valle, suka yi shelar barrantarsu da Zakzaki da tafarkinsa na


Rafilanci kuma suka kafa tasu qungiya ta yunqurin jaddada Musulunci a kan


tafarkin Ahlus Sunna, Jama’atu Tajdidil Islam (J.T.I.), a qarqashin shugabancin


Malam Abubakar Mujahid. A yanzu asirin Zakzaki ya tonu kuma taqiya ta qare,


amma kash! Biri ya riga ya yi varna.


Dalilan Yaxuwar Shi’a a Nijeriya


Akwai dalilai masu yawa da suka taimaka wajen yaxuwar tafarkin Rafilanci


a nan qasar. Za mu duba muhimmai daga cikinsu.


Dalili Na Farko: Gazawar Malamai


Dalili na xaya kuma mafi muhimmanci, shi ne gazawar malamai a


shugabancin jama’a da shiryar da su, da yi musu jagora da katangance su daga


vata. Domin famintar wannan dalili za mu kasa malamai gida uku.


1. Malaman zaure, ko kuma malaman buzu kamar yadda ake kiran su a wasu


wurare. Wannan kashi a cikin malamai su ne mafi girma, mafi alqadari kuma


mafi qima a idanun mutane. Amma duk da girma da qimarsu da muke gani, za mu


rufe ido mu faxi gaskiya game da su domin gaskiya ta fi ko wane mai qima qima.


Matsala ta farko da malaman zaure, yawancin su, shi ne imma dai suna da


qarancin sani ko kuma ilminsu ya sava Sunna. Xauki ilmin Tauhidi ga misali,


6


wanda shi ne mafi muhimmanci kuma mafi xaukakar dukkan ilman Musulunci.


Har yanzu malamanmu na buzu ba su rungumi tafarkin Sunna ba a babin Tauhidi;


Tauhidinsu imma Ash’ariya ne ko kuma Tauhidin masu Ilmul Kalam wanda yake


da tushensa a wajen Mu’utazilawa ko Falasifawa.


A fannin Fiqihu, wanda shi ne fannin da malaman zaure suka yi fice,


yawancinsu a Fiqihun Malikiya kawai suka tsaya. Idan mutum ya duba cewa


banda sauran mazhabobi uku fitattu, watau Hanafiya, Shafi’iya da Hanbaliya,


akwai mazhabobin Zahiriya da Zaidiya, banda mazhabobin xaixekun malamai


waxanda ba su samu yaxuwa ba kamar mazhabar Imam Thauri da Imam Auza’i da


sauransu, sai mutum ya ga cewa babu shakka malamanmu kaxan suka xebo a


Fiqihun Musulunci. Ba’a maganar fannin Usulul Fiqhi. Kuma ko a Malikiya ma,


wasu littafai ne qididdigaggu suke laqema, wasu manyan littafan mazhabar


yawancinsu ba su karanta su, kamar Tafsirin Qurxubi da Tafsirin Abubakar Ibnul


Arabi, da Altamhid na Ibnu Abdilbarri da Bidayatul Mujtahid na Ibnu Rushd, da


sauransu. A nan ba kuxin goro muke yi wa malaman ba; amma muna bayyana


halin yawancinsu ne.


A fannin Tafsiri kuwa, ya ishe ka manuniya cewa a qasar Hausa duka idan


mutum ya ce, “Na tafi wajen jalalaini,” to wajen karatun tafsiri yake nufi saboda


tafsiri shi ne jalalaini kuma jalalaini shi ni tafsiri. Wannan yana nuna yadda


malamanmu suka tsaya a kan littafin Tafsirul Jalalaini na Jalaluddinil Mahalli da


Jalaluddinis Suyuxi kawai a koyo da koyarwarsu na fannin Tafsiri. Idan aka duba


cewa wannan littafi bai kai matsayin moxa guda ba a cikin kogi dangane da abinda


aka rubuta a fannin Tafsiri, sai a ga cewa tabbas abinda malamanmu suka rasa ya fi


abinda suka samu a cikin wannan fanni. Bari batun ilmin Usulul Tafsir. A nan


ma, ba kuxin goro muke yi wa malaman ba; amma hukunci a kan mafi yawa ake


yin sa, mafi qaranci togewa ne.


7


Matsalar Luga a wajen malaman buzu makomarta ita ce ga matsalar manhaja


da tsarin koyarwa. Koyon Luga yana da rukunai uku: karatu da rubutu da furuci.


Ga alama malaman zaure karatu kaxai suke yi saboda a tsarin karatun zaure babu


zancen a bayar da aiki a rubuto, watau abinda ake cewa da Larabci “tamrinat” ko


“tamarin”, ko kuma da Turanci “exercises”. Wannan ya sa koda yake malaman


zaure yawanci suna da babbar taska ta xaixekun kalmoni, “vocabulary”, amma


magana da Larabci tana yi musu wuya, haka nan rubutawa. Kuma koda yake ana


iya lura cewa malaman buzu gwanayen rubutun waqa ne da Larabci, makomar


wannan, wata qila, shi ne cewa ita waqa ‘yar kyaikwayo ce.


Haka nan a fannonin Hadisi da Tarihi da Sira da Firaq; malaman buzu, in ka


xauke su gaba xaya, suna da qarancin rabo a cikin waxan nan ilmai. Rashin ilmin


Firaq, watau ilmin qungiyoyin bidi’a da aqidojinsu, shi ya sa malaman zaure suka


rasa ta yi a gaban kogin Shi’anci yayin da ya yi ambaliya domin ya tafi da matasan


Musulmi. Manyan littafan da aka rubuta a ilmin Firaq kamar Almilal wal Nihal na


Shahrastani da Maqalatul Islamiyina wa Ikhtilaful Musallina na Imam Abul


Hassan Al’ash’ari da Alfarqu bainal Firaq na Shaihul Islami Abdulqahir Albagdadi


da Alfisal fil Milal wal Ahwa’i wal Nihal na Ibnu Hazm Al’andalusi da sauransu,


yawancinsu ko sunayensu ba su tava ji ba.


Wannan ya sa suka xauka cewa wai Shi’anci wani wasan yara ne wanda za


su bari in sun girma! Idan aka ce su bincika abinda yake faruwa a tsakanin


Rafilawa sai su ce, haba wannan hayaniyar quruciya ce suke yi, za su bari ne. Sai


ga shi waxan nan malamai waxanda suka tashi zaune tsaye a saboda wasu ‘yan


qungiyoyi da suka ce wai suna zagin waliyai, sai ga shi ana zagin Sahabban


Annabi (SAW), ana kafirta su, amma sun yi shuru. Saboda haka malaman suka


kyautata alwala amma suka gaza sallah!


8


Abinda ya gabata dangane da ilminsu ne; amma idan muka duba ayyukansu


sai mu ga abin mamakin. Mun gabatar da bayani cewa a cikin malaman Musulunci


a nan qasar, malaman zaure su ne mafi yawa, mafi alqadari kuma mafi qima a


idanun mutane. Abinda ya sa suka zama haka shi ne cewa su magadan Jihadin


Shaihu Danfodiyo ne. Amma a yau, ayyukansu da halayensu sun sava da na


malaman Jihadi. Malaman Jihadi sun yi ilmi mai zurfi, kuma littafan da suka bari


suna shaidawa da haka, amma malamanmu na yau abin ba haka yake ba. Shaihu


Usmanu ya rubuta kimanin littafai 90, Shaihu Abdullahi kimanin 70; Muhammad


Bello xan Shaihu kimanin 80; Nana Asma’u kimanin 55; amma malamanmu na


yau, saboda gafala rubutun ma laifi suka xauke shi. Idan ka ce su rubuta littafi sai


su ce wai ba su gama da waxanda aka riga aka rubuta ba; idan kuma kai ka rubuta


sai su ce ka yi karambani. Alhali Shaihu Usmanu, a cikin littafinsa Najmul


Ikhwani, yana kira ga Musulmi da su riqa karanta littafan malaman zamaninsu,


saboda malaman ko wane zamani su suka fi sanin matsalolin wannan zamanin,


kuma wajibinsu ne su nemawa matsalolin magani.


Malaman jihadi sun yi wa’azi, malaman buzu ba sa yin wa’azi sai kaxan.


Malaman jihadi sun yaqi bidi’a, malaman zaure su bidi’ar suke yaxawa kuma duk


wanda yake yaqi da bidi’a to su shi ne abokin gabarsu. Malaman jihadi sun


nesanci sarakai da masu mulki, na yanzu kuwa shige musu suke yi. Malaman


jihadi sun yi jihadi kuma sun jaddada addini, malamanmu na yau ba su san ko inda


za’a kama bakin zaren ba. Malaman Jihadi sun tsaya tsaiwar daka, sun yi


gwagwarmayar tabbatar da gaskiya da tsai da adalci, malamanmu na yau cewa


suke yi yanzu zamanin yin shiru ne da lazimtar cikin gida, kamar yadda wani


babban malamin zaure ya faxa wa Shaihu Abubakar Mahmud Gumi.1 Malaman


jihadi sun gina al’umma, malaman buzu sai aikin gina gidajensu na gado. Ko


1 Duba Where I Stand na Abubakar Mahmud Gumi, bugun Spectrum Books, Ibadan-Nijeriya, 1992, shafi na


51.


9


wane malami ya qasaita sai ka ji ya naxa khalifa, wai xan da zai gaje shi. Ko waye


ya ce musu ilmi gado ne? Malaman jihadi sun ce a yi sana’a (duba Ahkamul


Makasib na Muhammad Bello) su kuwa yawanci ba sa sana’ar, balle su ce wani ya


yi, sai cin abinda suke kira albarkacin makaranta!! Wani malamin ma har faxa


yake yi don me za’a ce Musulmi su daina bara!! Kuma qarya yake yi; shi


‘ya’yansa ba sa bara.


Kai a yau ta kai cewa malaman buzu da yawansu, ba wai kawai sun raba gari


da tafarkin Shaihu Xanfodiyo ba da tarihinsa da koyarwarsa, a’a yaqar sa ma suke


yi! Sun qaurace wa littafansa da ilminsa da koyarwarsa. Mutum zai yi shekara


guda cur bai ji sunan Xanfodiyo ya gudana a bakin xayansu ba a wajen karatu ko


wa’azi. Maimakon haka, sun rungumi koyarwar wasu jahilan malamai waxanda


bas u zo qasar nan da kome ba sai diwanin waqe-waqe.


Wannan shi ne halin yawancin malaman azure, kuma shi ne tushen kusan


dukkanin matsalolin da muke fama da su a yau. Don haka babu mamaki idan ba su


taka rawa ta ku-zo- ku-gani ba wajen hana yaxuwar Shi’anci a qasar nan.


2. Kashi na biyu na malaman shi ne wanda za mu kira da sunan Ustazai.


Wannan kashi ya haxa da dukkan waxanda suka yi karatun addini amma a


zamanance, kamar waxanda suka halarci makarantun Haya Muslim kuma suka yi


karatun diflomomi ko digiri na fannin nazarin addinin Musulunci ko Shari’a a


manyan makarantu da jami’o’in qasar nan. Kuma ya haxa da waxanda suka yi


karatu a jami’o’in qasashen Larabawa da sauran qasashen Musulmi. Waxan nan


yawanci suna da kyakkyawar manhaja ta koyon karatu kuma ilminsu yana da faxi


da zurfi koda yake wasunsu, kamar waxanda suka fita daga jami’o’in qasarnan,


ilmin nasu faxi gareshi kawai amma ba zurfi. Sai dai duk da haka suna samun


kyakkyawan harsashi wanda yake ba da dama ga duk wanda yake so cikinsu da ya


10


zurfafa. Suna tsakuro wani abu kusan daga ko wane fanni muhimmi na addinin


Musulunci kamar Alqur’ani da Hadisi (waxan nan ba su da qarfi a manhajojin


jami’o’in Nijeriya); Fiqihu da Usulul Fiqihi, Falsafa da Tauhidi (a makarantun


Nijeriya yawanci Tauhidin Ash’ariya ake koyarwa); Tarihi da Sira; da kuma


fannonin Luga dabam – daban irin su Adab, Nahawu, Sarfu, Balaga da ressanta


uku, Aruli, da sauransu. Samun qaqqarfan harsashe na Luga yana zama tamkar


wani mabuxi ga Ustazai wanda suke buxe taskokin ilmi da shi.


Kamar yadda Ustazai suka sha bamban a wajen ilminsu, da mai zurfin ilmi


da mai cikin cokali, haka nan suka sha bamban wajen ayyukansu da halayensu da


sadaukar da kansu ga addini. Akwai masu aqidar Salaf, masu bin Sunna da yaqar


bidi’a, kamar yadda akwai ‘yan gargajiya wajen aqidarsu da fahimtarsu da


rungumar bidi’a. Daga cikin waxan nan na biyun akwai waxanda suka fito daga


gidajen malaman zaure, waxanda suka fito daga gidajen sarautar gargajiya da masu


karkata ga xariqun Sufaye. A cikin Ustazai akwai masu yin wa’azi da waxanda ba


sa yi, da masu yaqar bidi’a da ‘yan ba-ruwanmu da waxanda suka sadaukar da


kawunansu domin koyar da mutane da aikin da’awa da waxanda ba sa koyarwa


sai dai a aji inda ake biyan albashi.


Yawanci waxanda suka wayar da kan Musulmi dangane da tafarkin


Rafilanci, suka bayyana vacinsa da sharrinsa da vatansa, suka yi fama don dakatar


da yaxuwar Shi’anci a tsakanin Musulmi daga cikin wannan kashi suke. Daga


cikinsu akwai waxanda suka yi amfani da koyarwa da wa’azi wajen yaqar Shi’a


kamar Shaihu Abubakar Mahmud Gumi, wasu sun yi amfani da huxuba kamar


Shaihu Abubakar Jibril Sakkwato, wasu sun yi amfani da alqalumansu kamar


Shaihu Aminuddini Abubakar Kano wanda ya fassara littafin Alkhuxuxul Arida


na Muhibbud Dini Alkhaxib zuwa harshen Hausa wanda a karon farko ya fallasa


asirin Shi’a ga jamhurun Musulmi waxanda ba sa karatun Larabci ko Turanci.


11


3 Saboda rashin kalmar da ta fi, za mu kira kashi na uku na malaman da sunan


Burazozi wanda wannan hausancewa ne na kalmar “brothers” ta Turanci wace take


nufin ‘yan uwa. Abinda nake nufi da burazozi, ko kuma ‘Yan Buraza kamar yadda


aka fi sanin su, su ne mutane, yawanci matasa, waxanda suke da son Musulunci a


zuci amma kuma galibi suke da qarancin saninsa. Yawanci suna sanin Musulunci


ta hanyar sauraron laccoci a wurin taruka, karanta qasidu da maqalu a cikin jaridu


na yau da kullum da kuma mujallu masu kulawa da al’amuran Musulmi.


Yawancinsu xalibai ne masu karatun fannoni dabam-daban a manyan makarantu


da jami’o’i kamar fannonin kimiya, fasaha, tattalin arziki, likita, lauya da sauransu.


Kaxan ne daga cikinsu suka karanta Musulunci kuma a mataki na qasa ainun,


imma I.R.K. a makarantun sakandare ko kuma qaramar faifa ta aro a jami’a.


Kamar yadda na faxi a baya, yawancin waxannan matasa ne masu tsananin son


addini da kishin sa amma kuma babu wadatar ilminsa. Idan ka haxa qarancin sani


da tsananin kishi da gafin quruciya, sai ka samu wani kwaxo mai haxari. Kuma da


yake yawanci suna jin Turanci, harshen da shi ne ake yin amfani, kuma ake burga,


da shi a makarantu, wannan sai ya ba su damar shaqe wuyan makirfon da faxi a


saurare su, koda abinda za su faxi xin ba shi da nauyi ainun. Wani babban abinda


yake qara tauye su shi ne rashin jin Larabci kuma kamar yadda aka sani duk wanda


bai jin Larabci to ba ya shan kunun Musulunci sai dai ya sha farau – farau.


Wannan kashi na “malamai” daga cikinsu ne yawancin ‘yan Shi’a suka fito, ciki


har da madugunsu Malam Zakzaki.


Wannan bayani duka ba yana nufin cewa wannan kashi na malamai bai yi


wa Musulunci kome ba; a’a. A haqiqa ‘Yan Buraza sun toshe wata babbar kafa


a makarantunmu wacce, musamman a shekarun 1970 da 1980, ba mai iya toshe


ta sai su. Sun taimaka ainun wajen tsayar da ibadoji, kamar sallah da azumi, a


makarantu, sun tari qalubalen qungiyoyin Kirista kuma sun taimaka wajen


12


yaqar malamai da xalibai masu karkata ga tafarkin Gurguzu a jami’o’inmu a


lokacin da Kwaminisanci yake yaqar addinai da al’adu a qasashe masu tasowa.


Sai dai wannan kashi na malamai, da yawa daga cikinsu, bayan sun


manyanta kuma sun taka matakin shugabanci da tasiri a cikin al’umma, har yau


abin takaici suna nan suna yaxa Shi’a, wasu a kan rashin sani wasu kuma a bisa


ganganci. Daga cikinsu, ga misali, akwai wani xan jarida mai qima a idanun


makaranta, wanda ya yi rubutu a wata jarida wacce ake mata kallon ta Musulmi


ce, yana cewa wai qiyayyar da Larabawa suke nuna wa mutanen Iran qiyayya


ce da aka gina ta a kan qabilanci, yana nufin saboda su ‘yan Iran Farisawa ne ba


Larabawa ba, kuma wai savanin dake tskaninsu ba na aqida ba ne. Babu shakka


wannan xan jaridar imma dai ya shiga fagen da ba shi da sani a kai, abinda bai


dace da xan jarida mai mutunci da amana ba, ko kuma yana yaudarar


makarantansa ne da gangan.1


Akwai wani Farfesan Tarihi (amma ba Tarihin Musulunci ba) wanda ya ba


da lacca a munasabar bikin Ashura na ‘yan Shi’a na shekarar 1432/2011 a Kano,


inda ya ce wai ranar da Hussaini(RA) ya yi shahada ita ce rana mafi muhimmanci a


tarihin Musulunci.


Abin mamaki! Ba ranar da Annabi(SAW) ya yi hijira zuwa Madina ba


(wacce Sahabbai suka zave ta, don muhimmancinta, ta zama rana ta farko a


kalandar Musulunci); ba ranar yaqin Badar ba (wacce Allah ya kira ta a cikin


Alqur’ani: Yaumal Furqani: Ranar rabewa tsakanin qarya da gaskiya); ba ranar


Sulhun Hudaibiyya ba (sulhun da Allah ya kira shi a cikin Alqur’ani: Fatahan


Mubina: Buxi mabayyani); ba ranar Fatahu Makkata ba (ranar da aka kawo


qarshen bautar gumaka a qasar Larabawa); a’a, ranar da Hussaini ya yi shahada ita


ce mafi muhimmanci a tarihin Musulunci! Ban sani ba wannan jahilci ne daga


vangaren Farfesan ko kuwa ya sha farfesun Iran ne, shi ya sa yake faxin haka da


gan-gan don ya vatar da mutane?


1 Domin tabbatar da haka, duba littafinmu Matsayin Musulmi a wajen ‘Yan shi’a.


13


Kuma wasu jaridu da ake wa kallon cewa su na Musulmi ne sun xauko


wannan bankaura ta Farfesan, sun buga ta, suna yaxa ta a tsakanin al’umma. Shin


rashin sani ne wannan ko kuwa wata qullalliya ce? Ta yaya ‘yan jaridarmu za su


jahilci addininmu? Ko ta qaqa mutanen da aikinsu ne ilmantar da jama’a da


faxakar da su da wayar da su, za su komo suna yi musu rufa-ido?


Na karanta wata maqala a cikin jaridar Daily Trust fitowar Alhamis, 23 ga


watan Fabrairu, 2012 shafi na 52, inda wata ma’aikaciyar jaridar mai suna Hajiya


Wance ta ruwaito wani malamin Shi’a yana zargin Sayyidina Abubakar da


Sayyidina Umar, Allah ya qara musu yarda, da cewa wai sun yi mubaya’a ga Ali


binu Abi Xalib(RA) a kan khilafa a gaban Annabi(SAW) amma bayan rasuwar


Annabi xin sai suka warware wannan mubaya’ar.


Sai na yi mamaki yadda jaridar za ta tallata wannan zargi na Shi’a tare da


cewa zargin ya sava da tarihi ingantacce, kuma tare da cewa zargin yana tattare da


vatanci ga waxannan manyan Sahabbai. Na ce a raina da wani xan Majalisar


Dattijai ne ko Majalisar Wakilai aka yi wa wannan zargi da wata qila jaridar sai ta


tuntuve shi, ko ta tuntuvi wani mataimakinsa, kafin ta buga zargin don ya kare


kansa ko ya qaryata, kamar yadda jaridu masu mutunci suke yi. (Wani da ba na


tuhuma da qarya ya tabbatar mun da cewa sun aike da martani daga baya, amma


jaridar ba ta buga ba.)


Ita wannan musakar Hajiyar da ta rubuta maqalar da Editanta jahili, ko


munafuki, da ya buga ta ba su sani ba cewa warware mubaya’a babban laifi ne a


Musulunci wanda bai kamata a dangana shi ga gama-garin Musulmi ba, balle


Sahabi, balle shugabannin Sahabbai irin su Abubakar da Umar, musamman kuma


da yake wannan mubaya’ar an yi ta da umarnin Annabi(SAW) kuma a gabansa.


Dangana musu wannan laifi zargin su ne da aikata FASIQANCI.


Imam Muslim ya fitar da hadisi daga Abu Sa’id Alkhuduri(RA) ya ce:


Manzon Allah(SAW) ya ce, “Idan aka yi mubaya’a ga khalifofi biyu to ku kashe


na baya daga cikinsu.”1 Da yake sharhin hadisin, Imam Nawawi ya ce, “Ma’anar


hadisin: Idan aka yi mubaya’a ga wani khalifa bayan an riga an yi ga wani, to


mubaya’ar na farko ita ce ingantacciya kuma wajibi ne a cika ta. Sa’an nan


1 Sahih Muslim.


14


mubaya’ar na biyun vatacciya ce kuma haramun ne a cika ta. Haka nan haram ne


gare shi (khalifan na biyu) ya neme ta (mubaya’ar tasa).”1


Mai karatu yana iya gani a fili cewa waxannan talukai biyu, ina nufin


Hajiya musaka da jahilin Edita, sun taimaka wajen tallata wannan zargi na qarya


kuma sun dangana wa Abubakar da Umar, Allah ya qara musu yarda, munanan


abubuwa guda biyu: barin wajibi da aikata haram. Wannan da harshen Shari’a shi


ake cewa fasiqanci. Wata qila muna iya qarawa da wani abu na uku wanda ya fi


biyun muni: savawa umarnin Annabi(SAW) da gangan, abinda yana iya zama


kafirci, wanda kuma shi ‘yan Shi’a suke nufi da wannan zargin tunda su a wajensu


waxannan Sahabban kafirai ne masu ridda. Wal iyazu billah!


Muna fata wannan zai zama gargaxi ga masu karambani a cikin ilmin


Musulunci da su sama wa kansu lafiya, su qyale masu qwarewa da fagensu.


Dalili na Biyu: Jahilci


A yayin da malamai suka gaza sai jahilci ya samu filin baje koli. Juyin juya


hali na qasar Iran ya faranta ran al’ummar Musulmi ganin yadda tutar


Musulunci ta xaukaka da yadda daular kafirci mafi girma, Amurka, ta kunyata.


Wannan ya sa Musulmi da yawa suka sha’afa da aqidar mutanen Iran a lokacin


da suka riqa duban su a matsayin wani abin koyi da ya kamata kowa ya yi koyi


da su. Da yawa daga Musulmi sun zaci cewa bajintar mutanen Iran da nasarar


da suka samu ta ‘yantar da kansu daga zaluncin Amurkawa da danniyar


Turawan yammacin duniya baki xaya, sanadinta shi ne aqidar Rafilanci da suka


qudure. Wasu jahilai kuma suka riqa zaton cewa munafunci da suke gani a


wurin wasu sarakai da shugabannin qasashen Musulmi masu bin tafarkin Sunna


tushensa shi ne aqidarsu ta Sunna wace babu bore, ba gwagwarmaya, kuma


babu qundumbala a cikinta. Wannan sai ya sa Musulmi da yawa, musamman


matasa, masu tsananin son Musulunci da qin kafirci da jin takaicin halin


1 Duba Sharhu Sahih Muslim na Imam Muhyiddin binu Sharaf Annawawi, bugun Darul Fikir, Bairut, 1401,


mujalladi na 12 shafi na 231.


15


qasqanci da koma baya da al’umma suke ciki, suka riqa ganin sun sami mafita


a cikin koyi da mutanen Iran.


Wani abu da ya qara wa mutanen Iran farin jini da haiba a idanun Musulumi


waxanda zukatansu suke cike da son Musulunci amma qwaqwalensu wayam,


shi ne wasu kalmomi masu qyalli da qyal-qyali da suka riqa amfani da su


kamar gwagwarmaya, barranta daga xagutai, gogayya da kafircin duniya, yaqi


da waxanda suka kangarewa Allah Ta’ala, fatattaqar Yahudawa da ‘yanto


masallacin Baitul Maqdis, kafa jumhuriyar Islama, yin shahada wajen xaukaka


addinin Allah, da irin waxan nan kalmomin take da kirari waxanda Rafilawa


suka yi ta burgewa da su.


Ga alama irin waxan nan kalmomi su suka burge Zakzaki da maqarrabansa


inda suka yi ta maimaita su kamar yadda akun kuturu take kyaikwayon abinda


aka gaya mata ba tare da ta san ma’anarsa ba. Da waxan nan kalmomi su ma


suka ja gayya, inda komai na Iran ya zama abin yayi, kama daga babbaqun


rawunansu zuwa manyan alkebbunsu, kai har da sunayensu da laqabansu, da


tafiyarsu da maganarsu. Hotunansu da jaridunsu da mujallunsu da uwa uba


littafansu suka cika ko ina. A cikin wannan ruxu, mugunyar aqidarsu ta yi saraf


ta shige qwaqwalen dake haihai. Da haka ne Shi’a ta yaxu a Nijeriya a


qarqashin inuwar gazawar malamai da gafalarsu.


Dalili na Uku: Talauci


Talauci shu’umin abu ne. Yana zama haxari ga lafiyar mutum da tunaninsa; ga


halayensa da xabi’unsa; ga zamantakewar iyali da zaman lafiyar al’umma; kuma


abinda ya fi kome haxari, talauci yana iya mayar da Musulmi kafirai. Wannan ya


sa Manzon Allah (SAW) a koda yaushe yake addu’a yana neman tsari daga talauci,


kamar yadda aka ruwaito yana cewa, “Ya Ubangiji, ina neman tsarinka daga


16


talauci da qaranci da qasqanci.” (Abu Dawuda da Nasa’i). Kuma yana cewa, “Ya


Ubangiji, ina neman tsarinka daga kafirci da talauci.” (Abu Dawuda). Duba ka gani


yadda ya gama tsakanin kafirci da talauci za ka fahimci cewa haxarin talauci yana


da girma.1


Talauci ya taka mugunyar rawa ta fuska biyu wajen yaxuwar tafarkin Shi’anci a


tsakanin matasa Musulmi a Nijeriya. Fuska ta xaya ita ce kasancewar matasa da


iyayensu yawanci suna fama da talauci da rashin abin yi, don haka Rafilanci wanda


yake cike da hayaniya da zanga-zanga da sauransu, sai ya zama wata mafita ce ga


matasa da za su fita daga zaman banza da suke fama da shi kuma su sami abin yi


wanda zai shagaltar da su daga matsalolin rayuwa waxanda suka dabaibaye su.


Fuska ta biyu ita ce kasancewar da’awar ‘yan Shi’a da harakarsu ta xauki salon


zuga talakawa a kan masu mulki da attajirai ta yadda koda yaushe suke maimaita


magana a kan xagutai da azzalumai wanda ya sa talakawan Musulmi, waxanda a


haqiqa an zalunce su xin, suka rufawa ‘yan Shi’a baya domin huce fushi da fatan


rama gayya a qarqashin daular Shi’awa wacce suke fatan kafawa.


Yana da wuya a yi bayani filla-filla yadda gwamnatin qasar Iran ta yi amfani da


kuxi wajen yaxa tafarkin Rafilanci a Nijeriya, amma kowa ya san da walaki wai


goro a miya. A lokacin da yake kan ganiyarsa, kafin Shi’ancinsa ya fito fili rabin


mabiyansa su valle masa, Malam Zakzaki tare da gwamnoninsa na jihohi, watau


amir-amir da ya kafa a jihohi, duka suna rayuwa maya-maya, irin rayuwar attajirai


masu hannu da shuni. Banda katafaren gidan da ya gina a garinsu Zaria, malamin


kuma yana more kayan alatu kamar zunduma-zunduman motoci, kayan sadarwa na


zamani, karikicen lantarki da sauransu. Wannan kuma shi ne halin manyan


maqarrabansa waxanda suke a hedkwatarsa a Zaria da kuma waxanda suke a


1 Domin ganin hadarin talauci da muninsa, sai a duba Mushkilatul Faqar wa Kaifa Alajahal Islam na Yusuf


Alqaradawi, bugun Maktabatu Wahaba, Alqahira, 1415/1995, shafi na 12-25.


17


jihohi. Saboda haka muke ganin cewa mutanen, kasancewar ba sa yin aikin


gwamnati ko kamfani tunda wannan a ganinsu aikin xagutu ne, ba za su rasa


samun xan hasafi ba daga wasu kafafe da vangarori wanda da shi ne suke tafiyar


da harkokin qungiyarsu kuma su samu tsabar da suke watsa wa ‘yan tsaki. Kuma


idan muka dubi talaucin da mutanen qasar nan suke fama da shi, musamman


Musulmi, tun daga farkon shekarun 1980, lallai tsaba na iya kai ‘yan tsaki ko ina,


in ya so ta baro su.


Sai dai a yanzu an samu canji a tunanin ‘yan Shi’a da ayyukansu. Tuni suka


daina qin aikin xagutu, tun da a yanzu ana samun su a cikin ayyukan gwamnati da


na kamfani, bugu da qari a kan sana’o’I dabam-daban da suke yi. Hakan ya bas u


dammar kafa tsari na tattara kuxaxe daga mabiyansu waxanda suke amfani das u


wajen jawo mutane da shigar da su tafarkinsu ta hanyar agaji da taimakon


mabukata da sauransu.


Dalili na Huxu: Tavarvarewar Zamantakewa


Wani dalili da ya taimaka wajen yaxuwar Rafilanci shi ne tavarvarewar yanayin


zamantakewa a tsakanin jama’a sakamakon sauye-sauye da suka faru a rayuwar


al’ummarmu. Waxan nan sauye-sauye sun haxa da qaura daga rayuwar karkara


zuwa rayuwar maraya, tasirin rayuwar wasu al’ummai a kanmu, raunin


dangantaka tsakanin rukunan al’umma: tsakanin iyaye da ‘ya’ya, manya da yara,


shugabanni da talakawa, malamai da mabiya, da sauransu.


A yanzu kulawar iyaye ga yaransu ta yi qaranci ta yadda uba bai sanin inda


xansa yake yin harkokinsa, ko da su wa yake hulxa. Don haka bai san abinda ya


koyo, ko ra’ayin da ya xauko ba. Ikon da manya ke da shi a kan yara a yanzu ya yi


rauni. A da ana cewa yaro na kowa ne, kuma babban mutum ko dattijo yana iya


tsawatawa yara koda bai san su ba kuma dole su saurare shi. Amma a yanzu ana


18


ganin yara suna cin karensu ba babbaka, babu mai ce musu ku ci kanku. A yau,


talakawa sun daina mutunta shugabanni waxanda suka rasa kwarjininsu saboda


qarya da sata (‘yan siyasa), jahilci da kwaxayi (sarakan gargajiya). Mawadata sun


rasa ban girman matalauta waxanda suke ganin son abin duniyarsu ya yi yawa,


kuma sun hana su haqqinsu na zakka. Malamai su ma girmansu ya faxi a lokacin


da mutane suka lura cewa suna gudu bayan abin duniya kuma sun miqa wuya ga


masu mulki da mawadata, sa’an nan sun bar matsayinsu na magadan annabawa.


Wannan sakwarkwacewa a cikin alaqar rukunan al’umma junansu da juna ta


bar matasa da gama-garin mutane a sake ba kariya, kuma wannan hali ya bai wa


baraden Dujal, kamar shugabannin Shi’a, damar su baje kolinsu kuma su ci


karensu ba babbaka. A sakamakon haka, magoya bayansu sai qara yawa suke yi


koda yake abinda suke kira zuwa gare shi halaka ne da vata.


Dalili na Biyar: Gazawar Masu Mulki


Tsare Addini, hifzud dini, yana cikin manyan manufofin Shari’ar Musulunci,


Maqasidul Shari’a, kuma tabbatar da shi aikin hukuma ne. Daga cikin hanyoyin


tsare addini akwai kiyaye shi daga dukkan abinda zai iya gurvata shi, ko ya vata


kyawunsa kamar bidi’o’i da camfe-camfe da tsurface-tsurface da duk wani abu da


ya sava wa Alqur’ani da Sunna.


Abin takaici ne cewa, tsarin siyasar da muke bi a yau tsari ne wanda babu


ruwansa da addini. Saboda haka masu mulki suke ko-in-kula da abinda ya shafi


addini sai fa idan ya zama zai amfani manufofinsu da maslahohinsu na siyasa. A


sakamakon haka, Musulunci ya zama ba shi da gata, ko wane jahili, ko wani


mugun malami Dujal sai ya shiga harkar addini ya yi abinda ya ga dama. Wani


abin mamaki kuma shi ne, ko a jihohin da suke amfani da Shari’a a yanzu, abin bai


canja ba. Koda yake an kafa ma’aikatun kula da harkokin addini a waxan nan


jihohi, amma ga alama waxan nan ma’aikatu ba su xauki yaqi da bidi’o’i a


matsayin xaya daga cikin manyan ayyukansu ba. Wannan kuwa ba abinda yake


19


nunawa sai rashin fahimtar aikinsu, ko rashin sanin makamar aikin. Idan


Ma’aikatar Kula da Harkokin Addinin Musulunci ba ta yaqi bidi’a da masu yaxa


bidi’a ba, to mene ne amfaninta?


Ya kamata gwamnatocin jihohin Musulmi, kai har ma da gwamnatin tarayya, su


fahimci haqiqanin Rafilanci da xabi’arsa. Yaxuwar Shi’anci MATSALA CE TA


TSARO, ba wai kurum matsala ce ta addini ko ta zamantakewa ba. Babu inda za’a


samu Shi’a ta yaxu a tsakanin Musulmi ba tare da sun kawo fitina da tashin hankali


da zubar da jini ba. Wannan shi ne abinda tarihi yake shaida da shi kuma shi ne


abinda muke gani a yau a dukkan qasashen da suke da ‘yan Shi’a masu yawa


kamar qasar Siriya da Pakistan da Iraqi da Lebanon, da sauransu. Saboda haka zai


zama tamkar wani kyakkyawan riga kafi ne idan Musulmin Nijeriya suka yiwa


kansu qiyamallaili, suka tsayar da yaxuwar Shi’a tun al’amarinta bai faskara ba.


Kuma abin farin ciki shi ne, har yau ba’a makara ba; amma an yi kusa!


Gudunmawar Sufaye ga Yaxuwar Shi’a


Wani abu da zai iya shiga cikin dalilan yaxuwar Shi’a a Nijeriya shi ne


taimako da malamai da mabiyan xariqun Sufaye suka bayar wajen hakan. Da ma


dai akwai alaqa mai qarfi a tsakanin Shi’a da Sufanci ta wajen kafuwarsu da


aqidojinsu. Malamai da yawa sun yi magana a kan wannan alaqa, amma za mu ba


da misali da maganar wani malami wanda babu mai zargin sa da cewa shi “mai


tsananin ra’ayin Sunna ne,” ko almajirin Ibnu Taimiyya ne, ko xan Wahhabiyya


ne. Wannan malami shi ne Ibnu Khaldun. Ga abinda yake faxi dangane da


dangantakar Rafilawa da ‘yan Xariqa:


“Sa’an nan ‘yan baya daga Sufaye suka fara magana a kan kashafi da


al’amuran gaibu, kuma aqidojin Hululu da Xayantakar Samuwa suka bayyana a


20


tsakaninsu.1 Sai suka yi tarayya da Imamiyya (Shi’a ‘yan dozin) da Rafilawa


waxanda suka qudure allantakar Imamai da Hululu. Kuma magana a kan Quxubi


da Abdalu ta bayyana a tsakaninsu, kamar suna kwaikwayon aqidar Rafilawa


dangane da Imamai da Nuqaba’u. Kuma suka aro aqidojin Shi’awa.”2


Har yau, Ibnu Khaldun yana faxi a wani wurin dabam, “Sa’an nan waxan


nan Sufaye ‘yan baya, masu maganar kashafi da al’amuran gaibu, suka zurfafa…


Kuma magabatansu sun kasance suna gauraya da Isma’iliyya Rafilawa masu


quduri da Hululu da allantakar Imamai, tafarkin da ba’a san shi ba a wajen na


farkonsu. Sai ko wanne (daga qungiyoyin biyu) ya xarsa daga tafarkin xan


uwansa.”3


To amma duk da wanan dangantaka da alaqa mai qarfi a tushe da aqidu,


qungiyoyin biyu suna da bambance-bambance masu yawa. Ga wasu daga ciki:


Da farko, ‘yan Shi’a suna kafirta Sahabban Annabi(SAW) baki xayansu in


banda guda bakwai kawai, su kuwa ‘yan xariqa ba sa kafirta ko xaya daga cikin


Sahabbai.


‘Yan Shi’a suna zagin Sahabbai, suna yi musu qazafi, suna zagin Uwayen


Muminai matan Manzon Allah(SAW) suna yi musu qazafi, su kuwa ‘yan xariqa ba


sa zagin su, ba sa yi musu qazafi, maimakon haka suna girmama su, suna qaunar


su.


‘Yan Shi’a ba su yarda da khalifancin Khulafa’ur Rashiduna ba, Abubakar


da Umar da Usmanu, sai Ali kawai, su kuwa ‘yan xariqa sun yi imani da


khalifancin guda huxun baki xaya.


1 Dangane da ma’anar Hululu da Dayantakar Samuwa, sai a duba littafinmu Sufanci da Aqidun Sufaye.


2 A duba Muqaddimatu Ibni Khaldun na Abdurrahman binu Khaldun, bugun Darul Kutubil Ilmiyya, Bairut,


1424/2003, shafi na 254.


3 Muqaddimatu Ibni Khaldun, shafi na 386.


21


‘Yan Shi’a sun yi imani da khalifanci (ko imamancin) Imamai goma sha


biyu: Ali, Hassan, Hussaini, Ali Zainul Abidin, Muhammad Baqir, Ja’afar Sadiq,


Musa Kazim, Ali Rida, Muhammad Taqiy, Ali Naqiy, Hassan Askari da na sha


biyunsu Mahadi wanda suka ce wai an haife shi amma ya vuya yana xan shekara


huxu, kuma zai komo a qarshen zamani ya kafa daular Shi’awa. Su kuwa Sufaye,


koda yake suna qaunar waxan nan Imamai a matsayinsu na jikokin Manzon


Allah(SAW), to amma ba sa xaukar su a matsayin khalifofi (tunda ba wanda aka


tava naxawa khalifa a cikinsu sai Ali kawai) kuma babu shakka ba sa xaukar su a


matsayin Imamai da irin ma’anar da ‘yan Shi’a suke nufi da wannan kalmar.1


‘Yan Shi’a suna quduri da cewa waxan nan Imaman sun fi dukkan


Annabawa da Manzanni da Mala’iku makusanta ga Ubangiji, su kuwa ‘yan xariqa


ba sa ban gaskiya da haka.


‘Yan Shi’a suna quduri da cewa Imaman sun san gaibu, sun san abinda ya


faru tun farkon halitta da abinda zai faru har bayan abada, kuma sun san abinda


yake qunshe cikin zukatan bayi, su kuwa Sufaye ba sa quduri da haka.


‘Yan Shi’a suna quduri da cewa Alqu’ani da yake hannun al’umma a yau,


wanda kuma Musulmi ke tilawarsa a safe da yammaci, ba dai-dai yake ba, an yi


qari da ragi a cikinsa, kuma wai Sahabbai ne suka yi wannan qari da ragin, su


kuwa ‘yan xariqa ba sa ban gaskiya da haka.


‘Yan Shi’a suna imani da cewa garin Karbala ta fi Makka da Madina falala,


su kuwa ‘yan xariqa ba su yarda da wannan almarar ba.


‘Yan Shi’a sun yarda da auren mutu’a kuma suna yin sa, su kuwa ‘yan


xariqa a wajensu wannan irin auren zina ce kawai.


1 Domin ganin bambanci tsakanin yadda ‘yan Shi’a da Ahalus Sunna suke duban Imaman Shi’a, sai a nemi


littafinmu Ahalul Baiti a mahangar Ahalus Sunna da ‘Yan Shi’a.


22


Amma duk da waxan nan bambance-bambance masu yawa, ‘yan xariqa,


musamman xariqar Qadiriyya, sun taimaka wajen yaxuwar Shi’a a Nijeriya. Ya


aka yi haka ta faru?


Ga alama, akwai dalilai guda biyu. Na farko: jahilcin yawancin ‘yan xariqa


dab a su san haqiqanin Shi’a bad a miyagun aqidojinsu. Na biyu: munafuncin ‘yan


Shi’a da yaudararsu, inda suka I amfani da taqiyya, suka shige wa ‘yan xariqa suna


nuna cewa sun yarda a aqidunsu da ayyukansu a lokacin da, a haqiqa, suna xaukar


su a matsayin kafirai. ‘Yan Shi’a, waxanda aqidarsu ta taqiyya ta ba su dama su yi


kome ba kome,1 sun shiga cikin ‘yan xariqa suna yin Maulidi tare da su, suna


sallah bayan su, suna halartar tarukansu na zikiri da wa’azi, da sauransu. Wannan


sai ya yaudari ‘yan xariqa, a yayin da suka xauka cewa ‘yan Shi’a ‘yan uwa ne


abokan tafiya. Amma a haqiqa abin ba haka yake ba.


Su ‘yan Shi’a suna sane da cewa alaqar su da ‘yan xariqa alaqa c eta


yaudara, amma su Sufaye bayin Allah mutanen kirki bas u sani ba. Malaman Shi’a


suna lasafta Sufaye ‘yan xariqa a sahun nasibawa maqiya Ahalul Baiti, kuma suna


kafirta su baki xaya, kamar yadda suke kafirta sauran Ahalus Sunna tun daga kan


Sahabbai, Allah ya qara musu yarda, har ya zuwa yau.


Babban shaihinsu mai suna Alhurrul Aamili, yana cewa: “Ka sani (ya kai


mai karatu) cewa wannan suna, watau Sufanci, ya kasance ana amfani da shi ga


wasu falasifawa vatattu ga barin hanya. Sa’an nan, daga baya, sai aka riqa kiran


wasu zindiqai da shi, da wasu masu sava mana, maqiyan Ahalul Baiti, irin su


Hasanul Basari da Thauri da sauransu. Sa’an nan, wasu suka zo waxanda suka bi


tafarkinsu, irin su Gazali shugaban maqiya Ahalul Baiti… Suka riqa ganin cewa


nasibawa da zindiqai a kan gaskiya suke, sai suka bar lamarin Shari’a.”


1 Domin ganin aqidar Taqiyya da yadda ta halasta wa ‘yan Shi’a su aikata abinda suke ganin haramun ne a wajen


su, sai a duba littafinmu Aqidar Taqiyya a wajen ‘Yan Shi’a.


23


Ya ci gaba da cewa, “Shaihinmu mai girma, Shaihu Baha’uddin Muhammad


Al’aamili, ya ruwaito a cikin littafin Kishkul cewa Annabi(SAW) ya ce, ‘Alqiyama


ba za ta tashi ba sai wasu mutane daga al’ummata sun bayyana, sunansu Sufaye, ba


sa daga gare ni. Kuma lallai su ne Yahudawan al’ummata, kuma sun fi kafirai vata,


kuma su ‘yan wuta ne.’”1


Za mu kula cewa a cikin wannan nassi, malamin ya kafirta manya-manyan


shaihunnan Sufaye da malamansu, ciki har da Hujjatul Islam Algazali, wanda ya


kira shi shugaban nasibawa, da Hasanul Basari wanda yawancin Sufaye suke


xaukar sa a matsayin tushen tafarkinsu. To ina kuma ga sauran shaihunnai da


waliyyai?


Haka nan, malamin Shi’awa xan hayaqi, Ni’imatullahi Aljaza’iri, ya qulla


babi musamman a cikin littafinsa, inda ya yi bayanin aqidar malaman Shi’a ta


kafirta dukkan ‘yan xariqa da shaihunnansu da waliyyansu saboda sun yarda da


khalifancin Abubakar da Umar da Usmanu, kuma ya sifanta su da mafi munin


siffofi.2


Wannan yana tabbatar da abinda muka faxi cewa, kusanta ‘yan xariqa da


‘yan Shi’a suke yi ba wani abu ba ne face yaudara, don su samu magoya baya daga


almajiransu. Abin takaici shi ne har yau malaman xaiqu da mabiyansu bas u gane


ba. Sai yaushe za su farka?


Yanayin Yaxuwar Shi’a a Yau


1 A duba Risalatul Ithnai Ashariyya fil Raddi alal Sufiyya na Alhurrul Aamili, shafi na 13-16.


2 A duba Al’anwarul Nu’umaniyya, babin Zulumatun fi Ahawalis Sufiyyati wal Nawasib, bugun Madba’atu


Baab, Tibriz-Iran, ba tarihi, mujalladi na 2 shafi na 305.


24


Tun zuwan Shi’a Nijeriya, qungiyar ta taka matakai uku na yaxuwa kamar


haka:


Na xaya, matakin yaxuwa a lokacin taqiya da munafinci da yaudara. Wannan


shi ne lokacin da shugabannin Shi’a suka yi ta kira da sunan gwagwarmaya da


sabunta addini da kafa hukuncin Musulunci. A wannan yayi, qungiyar ta yaxu


yaxuwa mai yawa a lokaci qanqani sakamakon qishirwar matasa ta sauyi da kuma


rashin sanin haqiqanin abinda da’awar ta qunsa a wannan mataki.


Mataki na biyu, shi ne lokacin da Malam Zakzaki ya fito fili ya bayyana cewa


lallai Shi’a yake yi bayan taqiya ta tsawon shekara goma sha biyar ko sama da


haka. A wannan lokaci qungiyar ta rabe biyu kusan a tsakiya, inda a shekarar 1995


aka samu vullar qungiyar Jama’atu Tajdidil Islam wacce ta yi shelar barrantarta


daga tafarkin Rafilanci kuma ta yi wa shugabancin Zakzaki tutsu. Qoqarin matasa


dake vangaren J.T.I. da qungiyar Izala da kuma malamai da almajirai masu bin


tafarkin Salafiya, qoqarin waxan nan gaba xaya wajen tona asirin Shi’a ya kawo


tsaiko ga yaxuwarta, musamman a birane inda a da a nan ne ta fi yawan mabiya.


Ga alama a yanzu, Shi’a tana shiga mataki na uku na yaxuwa, inda masu aikin


yaxa ta suka mayar da hankali zuwa qauyuka da yankunan karkara. A cikin ‘yan


shekarun nan, biyu zuwa biyar, Rafilanci yana yaxuwa kamar wutar daji a qauyuka


saboda qarancin ilmi da wayewa ta addini da kuma cewa yawancin masu wa’azi


suna tattara qarfinsu a birane, sai kaxan ke fita dawa. Wannan ci gaba, ko kuma ci


baya za mu ce, da aka samu yana da haxarin gaske. Dalili shi ne, dama Shi’anci


jahilci ne, kamar yadda mai karatu ya riga ya gani, to idan aka haxa shi da jahilcin


dake akwai a karkara, to an samu itace jiqe jagab da kananzir, babu abinda ya rage


sai qyastun wuta! Idan haka ta faru, Allah ya tsare, za mu wayi gari a wani yanayi


wanda varnar Maitatsine da ta’addancin Kiristoci za su zama tamkar wasan yara.


Allah ya kiyashe mu fargar jaji.


25


Rufewa


A cikin wannan taqaitaccen littafi mun ga yadda Shi’a ta shigo Nijeriya


kuma mun ga dalilai da suka taimaka wajen yaxuwar ta. Kuma sharrin wanan


mugunyar qungiya ga addini da rayuwar duniya a yau ba sai an faxi ba; tun da abu


ne wanda kowa yake iya gani da idanunsa.


Don haka ya zama wajibi ga dukkan Musulmi, xaixeku da qungiyoyi da


hukumomi, su taimaka wajen yaqar wannan qungiya, domin ceto waxanda suka


riga suka faxa cikin ta da tsayar da yaxuwar ta. Bai kamata wani vangare na


al’umma ya yi kamar babu ruwansa ba a wannan harka; saboda yaxuwar Shi’a


matsala ce wacce ta shafi kowa da kowa.


Kuma dole ne waxanda suka taimaka a baya wajen yaxuwar wannan


qungiya, su yi KAFFARA a yanzu ta hanyar taimakawa wajen yaqar ta. Saboda


haka, malaman xariqu da almajiransu, da ‘yan Boko waxanda a da suka yi Buraza,


da kuma ‘yan qungiyar Jama’atu Tajdidil Islam, waxanda suka tuba daga yin Shi’a


amma suka koma gefe suka zama ‘yan kallo, suna da nauyi na musamman wajen


yaqar wanan mugunyar qungiya da ganin bayan ta.


Kuma koda yake havakar qungiyar da yawan hayaniya da barazanar ta suna


ba wasu mutane tsoro, amma mu da muka san xabi’arta muna iya tabbatar wa da


mutane cewa yaqar ta da kawar da ita daga doron qasar Nijeriya abu ne mai sauqi,


in Allah ya yarda. Shuru na mutane shi ke sa ta yaxuwa ba wani abu ba. Don haka


lokaci ya yi da kowa zai ba da tasa gudunmawa.


Allah ya yi mana taimako. Shi ne abin dogaron mu.


26



Posts na kwanan nan

QISSAR ANNABI ISA -AM ...

QISSAR ANNABI ISA -AMINCIN ALLAH A GARE SHI- DAGA CIKIN AL-QUR'ANI MAI GIRMA

SAKO DAGA MUSULMI MAI ...

SAKO DAGA MUSULMI MAI WA'AZI ZUWA GA MUTUM KIRISTOCI

FALALAR AZUMIN KWANA ...

FALALAR AZUMIN KWANA SHIDA SHAWAL

TAKAITACCEN BAYANI MA ...

TAKAITACCEN BAYANI MAI ANFANI GA SABON SHIGA MUSULUNC