Labarai




Introduction to Islam in Hausa Language


DA SUNAN ALLAH MAI MATUKAR RAHAMA DA


MATUKAR JIN KAI


TAKAITACCEN BAYANI GAME DA MUSULUNCI


Dukkanin godiya ta tabbata ga Allah; Ubangijin talikai, sannan salati da taslimi ga shugaban


manzanni; Annabinmu MUHAMMADU, hada da gabadayan alayensa da sahabbansa. Bayan


haka.


Shi dai MUSULUNCI, shi ne sakon Allah na karshe - daga jerin sakwanninSa - zuwa


gabadayan al’umma, wanda Ya saukar da shi ga cikamakon annabawanSa; MUHAMMADU


DAN ABDULLAHI, tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi.


MUSULUNCI shi ne addinin gaskiya wanda Allah ba Ya karbar wani addini daga wani mahaluki


in ba shi ba. Kuma, hakika Allah Ya sanya shi addini sassauka da ba wata wahala a cikinsa;


don bai wajabtawa mabiyansa abin da ba za su iya ba, bai kuma dora masu abin da ya fi


karfinsu ba.


Hakanan, MUSULUNCI addini ne da kadaita Allah ne tushensa, rahama ruhinsa, gaskiya


takensa; ya tsaya a kanta tsayin-daka, kamar yadda ya ke cike makil da adalci, zuwa gareshi


yake kira, kuma a kansa yake kaiwa yake komowa.


Harwalau, MUSULUNCI shi ne addinin nan mai girma wanda yake fuskantar da bayin Allah


zuwa ga duk wani abu mai amfani a garesu a addininsu da duniyarsu, yake kuma gargadinsu


daga duk wani abin da yake mai cutarwa ne a garesu a addininsu da rayuwarsu.


Haka zalika, MUSULUNCI shi ne addinin da Allah Ya gyara akidu, da halaye, da rayuwar


duniya da ta lahira da shi. Da kuma shi ne ya gyara tsakanin soye-soyen ran da suke a


rarrabe, da zukatan da suke nesa da juna. Ta haka ne ya tseratar da su daga duffan bata


zuwa hasken shiriya, ya kuma yi masu ja-gaba zuwa hanya madaidaiciya.


Sannan - bayan dukkanin abubuwan da suka gabata - MUSULUNCI shi ne tsayayyen addini,


wanda aka kyautata shi matuka gaya cikin kafatanin labarurrukansa, da daukacin hukuncehukuncensa.


Babu wani labari da ya bayar sai da gaskiya, kuma ba bu wani hukunci da ya yi


sai da alheri da adalci, daga ingantattun akidu, da kyawawan ayyuka, da halaye mafifita da


ladubba madaukaka.


MANUFAR SAKON MUSULUNCI


Manufar sakon musulunci ita ce tabbatar da wadannan abubuwa:


(1) Sanar da mutane Ubangijinsu (mahaliccinsu) ta hanyar ilmantar da su sunayenSa


wadanda suke iyaka ne wajen kyau, da sifofinSa wadanda suke sun kai kololuwa wajen


daukaka, da ayyukanSa cikakku.


(2) Kiran bayin Allah zuwa bautar Allah Shi kadai, ba shi da abokin tarayya (wato su aikata


abubuwan da ya wajabta masu su kuma bar wadanda ya hane su). Kuma wannan bauta ce


kadai za ta gyara masu duniyarsu da lahirarsu.


2


(3) Tunatar da su halinsu, da makomarsu bayan mutuwarsu, da kuma abubuwan da za su


gamu da su a kaburburansu, da kuma lokacin tashinsu daga cikinsu ranar kiyama suna


rayayyu, hada da lokacin yi masu hisabi, da kuma tuna masu makomarsu cewa dayan biyu


ce: ko dai aljanna ko wuta.


GINSHIKAN MUSULUNCI


Ginshikan musulunci da suka fi muhimmanci a takaice su ne:


GINSHIKI NA FARKO: AKIDA


Wato imani da jiga-jigan imani guda shida:


JIGO NA FARKO: IMANI DA ALLAH


Wannan kuma ya kunshi abubuwa masu zuwa:


(1) IMANI DA RUBUBIYYAR ALLAH


Wato imani da cewar ba wani ubangiji, mahalicci, mamallaki, mai gudanarwa da sarrafa


al’amuran bayinsa sai shi.


(2) IMANI DA ULUHIYYAR ALLAH


Wato imani da cewa Shi kadai ne abin bauta na gaskiya; duk wani abin bauta ba shi ba,


karya ne.


(3) IMANI DA SUNAYEN ALLAH DA SIFOFINSA


Wato imani da cewa tabbas Allah Yana da sunaye masu matukar kyau, da cikakkun sifofi


masu matukar daukaka, a tabbatar masa da su kamar yadda suka zo a Al-Kur’aninSa da


sunnar manzonSar.


JIGO NA BIYU: IMANI DA MALA’IKUN ALLAH


Mala’iku manyan bayi ne da Allah Madaukakin Sarki Ya halicce su, Ya kuma dora masu


ayyuka daban-daban, su kuma suka mika wuya gareshi, suna masu yi masa biyayya, kamar


yadda suke bauta masa ba-dare-ba-rana.


Daga cikin wadannan Mala’iku akwai:


1- JIBRILU, wanda aka wakilta wajen sauko da wahayi, yana sauko da shi daga Allah zuwa


wanda Allah din Ya so na daga AnnabawanSa da ManzanninSa.


2- MIKA’ILU; wanda a ka wakilta wajen ruwa da tsirrai.


3- ISRA’FILU; wanda a ka wakilta wajen busa kaho lokacin da komai da kowa zai mutu, da


lokacin tashinsu daga kaburburansu ranar kiyama.


4. MALAKUL MAUTI (MALA’IKAN MUTUWA); wanda a ka wakilta wajen karbar ran duk wanda


zai mutu.


JIGO NA UKU: IMANI DA LITTATTAFAN ALLAH


3


Ba shakka Allah Mai matukar daukaka da buwaya Ya saukar da littattafai ga manzanninSa.


Duk wata shiriya, da alheri, da gyara suna cikinsu.


Wadanda muka sani daga cikin wadannan littattafai su ne:


1. ATTAURAT; Saukakken littafin Allah zuwa Annabi MUSA r kuma shi ne littafin Bani Israa’ila


mafi girma.


2. AL-INJIL; Saukakken littafin Allah zuwa Annabi ISA r


3. AZZABUR; Wanda Allah Ya bai wa Annabi DAWUD r


4. SUHUFU IBRAHIM; Na Annabi IBRAHIM r


5. ALKUR’ANI MAI GIRMA; Littafin da Allah Madaukakin sarki Ya saukar da shi zuwa


Annabinmu MUHAMMADU r, karshen annabawan Allah, sai Allah Ya shafe daukacin littattafan


da suka gabata da wannan Al-Kur’ani, kamar yadda Ya yi alkawarin kare shi; don kuwa zai


wanzu hujja a kan gabadayan halitta har zuwa ranar kiyama


JIGO NA HUDU: IMANI DA MANZANNI


Ba shakka Allah Madaukakin Sarki Ya aika manzanni zuwa bayinSa. Na farkonsu dai shi ne


Annabi NUHU r, na karshensu kuma Annabi MUHAMMADU r.


Gabadayan manzannin Allah mutane ne, ‘yan Adam; halittarsu aka yi; ba su da wani abu


daga cikin abubuwan da Allah Ya kebanta da su (kamar yin arzuki, ko ruwa, rayawa ko


matarwa ... d.ss) domin su bayi ne daga bayin Allah, Allah Ta’ala Ya girmama su da aiko su


da Ya yi da sakonSa.


Allah Madaukakin Sarki Ya rufe aiko da sakwanninSa da sakon da Ya aiko MUHAMMADU r da


shi, Ya kuma aiko shi zuwa daukacin mutane. Babu wani annabi bayansa.


JIGO NA BIYAR: IMANI DA RANAR LAHIRA


Ranar lahira ita ce ranar kiyama da ba wata rana bayanta. Ranar da Allah zai tashi mutane


daga kaburburansu suna rayayyu, don wasu su wanzu a gidan ni’ima (ALJANNA) wasu kuma


a gidan azaba mai matukar radadi (WUTA).


Imani da ranar lahira shi ne: Imani da duk abubuwan da za su kasance bayan mutuwa, daga


tambayar kabari, da ni’imarsa da azabarsa, da kuma duk wani abu da zai kasance bayan


wannan hali, kamar raya matattu da tashinsu daga kaburburansu, da hisabi, har dai a kai ga


shiga Aljanna ko Wuta.


JIGO NA SHIDA: IMANI DA KADDARA


Imani da kaddara shi ne mutum ya yi imani da cewa hakika Allah Ya kaddara duk wasu


abubuwa da za su kasance tun kafin kasancewarsu, ya kuma samar da daukacin halittu


kamar yadda ya rigaya a iliminSa, kuma yake kunshe a cikin hikimarSa.


Dukkanin abubuwa sanannu ne kuma rubutattu a wurin Allah Ta’ala, shi Ya so samuwarsu,


kuma shi Ya samar da su.


GINSHIKI NA BIYU: JIGAJIGAN MUSULUNCI


4


Shi dai musulunci ginannen addini ne daga wasu jigajigai guda biyar, mutum ba zai zama


musulmin gaskiya ba sai ya yi imani da su gabadaya da zuciyarsa, yana mai aikata su da


gabbansa.


WADANNAN JIGAJIGAI SU NE


JIGO NA FARKO: KALMAR SHAHADA


Wato:


شهادة ألا إله إلا الله وأن محمداً رسول الله


“SHAHADATU AN LA ILAHA ILLA ALLAH, WA ANNA MUHAMMADAN RASULULLAH”. Shahada


ita ce mabudin musulunci, kuma tushensa da a ka a za harsashinsa a kanta.


Abin da a ke nufi da الإله shi ne abin da a ke bautawa.


MA’ANAR: شهادة ألا إله إلا ا لله “LA ILAHA ILLA ALLAH” Babu wanda ya cancanci a bauta masa


sai Allah Shi kadai, Shi ne abin bautawa na gaskiya, kuma duk wani abin bautawa ba shi ba,


karya ne, kuma shirme ne.


MA’ANAR: شهادة أن محمدا رسول ا لله “SHAHADATU ANNA MUHAMMADAN RASULULLAH” Ita


ce: Gaskata MUHAMMADU MANZON ALLAH r cikin duk abin da ya fada, da aikata duk abin da


ya ce a yi, da barin duk abin da ya ce a bari, kar kuma a kuskura a bautawa Allah sai da abin


da ya shar’anta.


JIGO NA BIYU: SALLOLI


Salloli ne guda biyar, kowa ce da lokacinta. Allah Ya yi horo da su don bayi su ba shi


hakkinSa, su kuma gode ni’imominSa. Kamar yadda ta ke wata kullalliyar alaka ce tsakanin


musulmi da ubangijinsa, da ya ke kiransa a cikinta, ya ke kuma ganawa da shi.


Hakanan, Allah Ya shar’anta su don su hana musulmi aikata alfasha da miyagun ayyuka.


Bayan haka, alherin addini da gyaran imani, da ladan Allah na duniya da lahira duk Allah Ya


rataya su da wadannan salloli. Ka ga musulmi ya samu abin da zai ba shi jin dadin duniya da


na lahira; mutane su na cikin damuwa a zukatansu da jikkunansu, shi kuwa garau ba abin da


ya dame shi, kullum ya na cikin walwala da annashuwa.


JIGO NA UKU: ZAKKA


Zakka ita ce sadakar da wanda ta wajaba a kansa ya ke bayar da ita duk shekara ga


wadanda suka cancance ta kamar fakirai da shauran wadanda ya halatta a ba su.


Zakka ba ta wajaba a kan fakiri tun da bai mallaki gwargwadon abin da shari’a ta kayyade za


a fitar masa da zakka ba (wato NISABI). Don haka tana wajaba ne a kan mawadata.


Allah Ya wajabta masu ita don kammala masu musuluncinsu da kyautata yanayi da


halayensu, da kiyaye su, su da dukiyoyinsu daga masifu da bala’ai, da kuma tsarkake su daga


zunubai. Hakannan, don share hawayen fakirai da mabukata, da kula da manyan


masalahohinsu, wadanda rashinsu ya ke ci wa kowannensu tuwo a kwarya.


Tare da duk wadancan abubuwan da a ka ambata za ka ga abin da a ka ce mawadatan su


bayar, bai fi cikin cokali ba in ka kwatanta da dukiya da arzukin da Allah Ya yi masu.


5


JIGO NA HUDU: AZUMI


Wato azumtar watan Ramalana mai albarka; watan tara a jerin watannin shekarar hijira.


A cikinsa musulmi su na haduwa kwansu da kwarkwatarsu, su bar manyan sha’awowinsu da


rana; ba ci, ba sha, ba saduwa da iyali (tun daga ketowar alfijir har zuwa faduwar rana).


Kuma Allah Madaukakin Sarki, Yana musanya masu wadancan abubuwa da suka bari daga


falalarSa, da ihsaninSa; wato Ya cika masu addininsu, da imaninsu, Ya kuma kankare masu


zunubansu, Ya kuma daga darajojinsu, da dai shauransu na daga manyan alheran duniya da


na lahira da Ya rataya su da azumi.


JIGO NA BIYAR: HAJI


Haji shi ne zuwa dakin Allah Mai girma (da ke Maka), a wani lokaci takamaimai don gudanar


da wasu ayyukan ibadu na musamman. Allah Madaukakin Sarki Ya farlanta haji ga mai iko


sau daya kacal a rayuwarsa gabadaya.


A lokacin aikin haji ne daukacin musulmi su ke yin tururuwa su hadu - daga duk fadin duniya


- a fiyayyaun wurare a bayan kasa, suna masu bautawa ubangiji daya, suna sanye da kaya iri


daya, ba bu bambanci tsakanin shugaba da talaka, babu bambanci tsakanin mawadaci da


mabukaci, babu bambanci tsakanin fari da baki.


Haka, za su yi dafifi gabadaya don gabatar da wasu iyakantattun ibadu, alal misali tsayuwar


arfa, dawafi (wato zagaya Ka’aba madaukakiya alkiblar musulmi), sa’ayi (wato kai-kawo


tsakanin dutsen Safa da dutsen Marwa). Wasu ke nan daga cikin ibadu mafiya girma da a ke


gabatarwa a wadannan wurare masu albarka.


Hakika Allah ne kadai Ya san dumbin alfanu na addini da na duniya da aikin haji ya tattaro;


don ba za su kirgu ba.


GINSHIKI NA UKU


Sannan hakika musulunci ya tsara rayuwar mabiyansa daidaikunsu da jama’unsu da abin da


zai tabbatar masu jin dadin duniya da na lahira.


DON KUWA ya halatta masu aure ya kuma kwadaitar da su yinsa, ya kuma haramta masu


zina da luwadi, da duk sauran ayyukan assha.


SANNAN ya wajabta masu sada zumunta, da tausayin fakirai da musakai da kula da su. Ya


wajabta, ya kuma kwadaitar da su da siffatuwa da duk wani kyakkyawan hali ya kuma


haramta hada da kada akalarsu daga duk wani mummunan hali.


Sannan ya halatta masu neman na-kansu, su nemi halaliyarsu, ta hanyar kasuwanci, ko


kodago, da makamantansu. Ya kuma haramta masu riba, da duk wani haramtaccen ciniki,


kazalika duk wani abin da akwai algus ko garari a ciki.


Hakanan ya kula da bambancin mutane wajen kiyaye tsare-tsare da dokokinsa, da kiyaye


hakkokin wasu, haka ce ma ta sa ya shar’anta wasu ukubobi masu tsawatarwa (wanda duk a


ka zartarwa da daya daga ciki ya bar sha’awar kuma aikata laifin da ya janyo masa ita, kai!


waninsa ma ba zai yi tunanin aikatawa ba).


Wasu ukubobin sun shafi keta hakkokin Allah Madaukaki kamar ridda (yin abin da zai fitar da


mutum daga musulunci), da zina, da shan giya. Wasu kuma sun shafi daukacin nau’oin


ta’adda ga hakkokin mutane, kamar kisan-kai ko sata ko kazafi (zargin kamamme ko


kamammiya da zina ba tare da shedu ba), ko yin ta’adda da duka, ko duk wata cutarwa.


6


Hakika, duk wanda ya yi duba da idon basira zai ga kowace ukuba ta dace da laifin da a ka


shar’antata dominsa, don zai ga hukunci ne tsaka-tsaki (ba sako-sako, ba kuma shige-gonada-


iri).


Bugu-da-kari, musulunci ya tsara ya kuma tantance alakar da ke akwai tsakanin


shuwagabanni da talakawansu, haka ce ma ta sa ya wajabtawa talakawa bin


shuwagabaninsu cikin duk abin da ba sabon Allah ba ne, ya kuma haramta masu tawaye da


fito-na-fito da su, saboda kanana da manyan barnace-barnacen da hakan ke haifarwa.


A karshe, zai yiwu mu ce ba wani shakku ko tababa kan cewar musulunci ya kunshi gini da


samar da sahihiyar alaka hada da ingantaccen aiki tsakanin bawa da ubangijinsa, da tsakanin


mutum da ragowar mutanen da suke kewaye da shi a cikin dukanin al’amura na yau da


kullum. Ba wani alheri na daga halaye da mu’amaloli sai ya nuna wa al’umma ya kuma


kwadaitar da su don su aikata. Hakanan babu wani sharri a cikin halaye da mu’amaloli sai ya


gargadi al’umma ya kuma hana su aikata shi. Hakika wannan yana bayyana mana kuru-kuru


cikar wannan addini da kyawunsa ta kowace fuska.


DUKKANIN GODIYA TA TABBATA GA ALLAH UBANGIJIN TALIKAI


FASSARAR : MUHAMMAD NURA ABDULLAHI



Posts na kwanan nan

TAKAITACCEN BAYANI MA ...

TAKAITACCEN BAYANI MAI ANFANI GA SABON SHIGA MUSULUNC

ZIKIRAI WADANDA AKE Y ...

ZIKIRAI WADANDA AKE YIN SU DA SAFE DA KUMA YAMMA

BIDI’AR ‘YAN SHI’A A ...

BIDI’AR ‘YAN SHI’A A RANAR ASHURA

ANNABI ISAH AMINCIN A ...

ANNABI ISAH AMINCIN ALLAH YA TABBATA A GARESHI A CIKIN ALKUR’ANI 1