Labarai

WA YA HALICCI HALITTU? WA YA


 HALICCE NI ? KUMA SABODA ME ?





 Kwamitin ilimi a jagorancin harkokin addini a


 Masallacin Harami da Masallacin Annabi





 WA YA HALICCI HALITTU? WA YA


HALICCE NI ? KUMA SABODA ME ?





 Kwamitin ilimi a jagorancin harkokin addini a


Masallacin Harami da Masallacin Annabi





WA YA HALICCI HALITTU? WA YA


HALICCE NI ? KUMA SABODA ME ?


Shin Ina kan hanya ta daidai ?


Wa ya halicci sammai da kasa da abinda ke tsakanin


su na halittu masu girma wadanda ba’a iya gane


yawansu?


Wa ya kera wannan gwanannan tsarin a sama ko a


kasa ?


Wa ya halicci mutum ya kuma ba shi ji da gani da


hankali? Ya sanya shi mai iko akan tsururutar wasu


ilimai da gane hakikanin abubuwa ?


Wa ya kagi wannan gwananniyar  kira a gabban


jikinka, ya kuma surantaka sai ya kyautata halittar ta


ka?


Ka yi la’akari da halittar halittu rayayyu a banbancin


Nau’ukan su, wa ya kage su a wannan kyawun da ba


shi da iayaka?


Ta yaya wannan kasantacce mai girma yake


tsaruwa kuma yake tabbatuwa tare da ka’idojin sa,


wadanda suke kiyaye shi, kiyaye wa ta kwarewa


tsawon wadannan shekaru?


Wa ya sanya wadannan tsare-tsare wadanda suke


tafiyar da wannan halittar (rayuwa da mutuwa,


bibikon rayuwa, dare da yini, canjin lokuta …


2


Shin wannan halittar ita ta yi kanta ? Koko ta samu


ne daga rashi? Ko kuma kwatsam aka same shi ?


Allah madaukakin sarki yana cewa:





 {Shin, an halitta su ne bã daga kõme ba, kõ kuwa


sũ ne mãsu yin halitta(35)


Shin, sun halitta sammai da ƙasa ne? Ã'a ba su dai


yi ĩmãnin yaƙĩni ba.


Suratut Tur, aya ta: 35-36.


Idan ba mu halicci kammu ba, kuma ba zai taba


kasancewa a ce mun zo ne daga babu ko kwatsam, to


dole abinda yake gaskiya da ba kokonto a cikinta:


Wannan halittar dole ne tana da malicci mai girma mai


iko, domin ba zai yiwu wannan duniyar ta halicci kanta


ba, ko ta zo daga babu ko kuma kwatsam.


Saboda me mutum yake yin imani da abubuwan da


ba ya ganisu, kamar: (Tunani hankali, rai, ji a jika, da


so.) ashe ba saboda yana ganin alomominsu ba ne? To


tayaya mutum zai yi mu sun samuwar Mahaliccin


wadannan abubuwa masu girma, alhali yana ganin


alamomi na halittarsa da aikinsa da kuma rahamarsa?


Babu mutumin da zai yarda a ce da shi: Ai wannan


gidan kawai ya samu ne ba tare da wani ne ya gina shi


ba. Ko a ce da shi: Ai babu ita ce ta samar da wannan


gidan!. To, ta yaya wasu daga cikin mutane suke


3


gasgata wanda yake cewa: wannan duniyar mai girma


ta zo ne ba tare da Mahalicci ba ?. Ta yaya mai hankali


zai yarda ace da shi: wannan ginin (na sama da kasa)


wanda ke cike da kwarewa ya samu ne haka kawai?


Duk wannan yana kaimu ne zuwa ga sakamako


guda daya cewa: Wannan duniyar (halittar) tana da


Ubangiji mai girma mai iko da yake kula da su, kuma


shi ne kadai ya cancanci bauta, kuma duk abinda ake


bautawa komabayan shi to bautar batacciya ce kuma


shi bai cancanci a bauta masa ba.


Ubangiji Mahalicci Mai girma.


Akwai wani Ubangiji Mahalicci guda daya, shi ne


Mamallaki mai jujjuya lamura mai azurtawa, wanda


yake rayawa yake kashewa. Shi ne wanda ya halllici


kasa. ya kuma sawwaketa, ya sanyata daidai da


halittunsa. Shi ne wanda ya halicci sama da abinda


yake cikinta na halittu masu girma. Ya sanya wa rana


da wata da dare da yini wannan nagartaccan tsarin ,


wanda yake nuni a bisa girman Ubangijinsa.


Shi ne wanda Ya hore mana iska, wacce babu


rayuwa a garemu idan babu ita, Shi ne wanda Yake


saukar mana da ruwa, kuma Ya hore mana tekuna da


ƙoramu. Shi ne wanda Yake ciyar da mu, Yake karemu


alhali mu muna tayi a cikin mahaifammu, ba tare da


muna da wani ƙarfi ba, Shi ne wanda Yake tafiyar da


jini a cikin jijiyoyin mu, tun daga haihuwar mu har


zuwa mutuwarmu.


4


Wannan Ubangijin Mahalicci Mai azirtawa,


Shi ne Allah - tsarki da ɗaukaka sun tabbatar


masa -.


Allah - Madaukakin sarki - Ya ce:





 {Lalle ne Ubangijinku Allah ne, wanda Ya halitta


sammai da ƙasa a cikin kwãnaki shida, sa'an nan kuma


Ya daidaita a kan Al'arshi, Yanã sanya dare ya rufa yini,


yanã nẽman sa da gaggawa, kuma rãnã da watã da


taurãri hõrarru ne da umurninSa. To, Shĩ ne da halittar


kuma da umurnin. Albarkar Allah Ubangijin halittu tã


bayyana!}


[al-A'araf: 54].


Allah ! Shi ne Ubangiji Mahalicci ga dukkan abinda


ke cikin duniyar nan wanda muke gani da wanda ba


ma gani, duk abinda ba Shi ba to halitta ne daga


halittun Sa. Shi ne wanda Ya cancanci a bauta maSa


Shi kaɗai, kuma kada a bautawa wani tare da Shi, ba


Shi da abonkin tarayya a mulkinSa ko halittarSa ko


jujjuya lamura ko bauta maSa.


Da zamu ƙaddara cewa akwai wasu ababan bauta


tare da Ubangiji - Maɗaukakin sarki - da halittu sun


lalace; domin ba zai yiwu ba a ce alloli biyu ne suke


5


jujjuya al’amarin halitta a lokaci guda, Allah -


Maɗaukakin sarki - Ya ce:





 {Da ya kasance acikinsu (sama da ƙasa) akwai wasu


allolin banda Allahu to da sun ɓaci}


[al-Anbiya'a: 22].


SIFFOFIN UBANGIJI MAHALICCI.


Ubangiji - tsarki ya tabbata a gare Shi - Yana da


sunaye masu kyau waɗanda ba a iya ƙididdige su, Yana


kuma da siffofi maɗaukaka masu yawa masu girma


waɗanda suke nuni akan cikarSa.


Daga cikin sunayan na Sa:


Mahalicci, Allah. Ma’anar sa: Abin bauta wanda Ya


cancanci bautar Shi kaɗai, ba Shi da abokin tarayya.


Rayayye, Tsayayye, Mai jin ƙai, Mai azirtawa, Mai


karamci,


Allah - Maɗaukakin sarki - a ckin AlKur'ani mai


girma Ya ce:





 {Allah, bãbu wani Ubangiji fãce Shi, Rãyayye, Mai


tsayuwa da kõme, gyangyaɗi bã ya kãma Shi, kuma


barci bã ya kãma Shi, Shi ne da abin da yake a cikin


6


sammai da abin da yake a cikin ƙasa. Wane ne wanda


yake yin cẽto a wurinSa, fãce da izninSa? Yana sanin


abin da yake a gaba gare su da abin da yake a bãyansu.


Kuma bã su kẽwayẽwa da kõme daga ilminSa, fãce da


abin da Ya so. KursiyyunSa ya yalwaci sammai da ƙasa.


Kuma tsare su bã ya nauyayarSa. Kuma Shi ne


Maɗaukaki, Mai girma}


[Suratul Baƙarah: 255].


Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce:





 Ka ce: "Shi ne Allah Makaɗaĩci (1)


Allah shi ne abin nufi da Buƙata (2)


Bai haifa ba, kuma ba a haife Shi ba (3)


Kuma babu ɗaya da ya kasance kini a gare Shi)


[al-Ikhlas: 1-4].


Ubangiji abin bauta wanda ya siffantu da


siffofin cika





 Daga cikin siffofinSa Shi ne abin bauta, wanda ba


Shi ba to abin halitta ne, kuma an ɗora masa hukunce-


hukunce kuma abin umarta ne kuma abin rinjaya.


Daga cikin siffofinSa Shi Rayayye ne kuma Tsayayye


ne, to duk wani samamme a wannan halittar Allah ne


Ya rayar da shi, kuma Ya samar da shi daga babu, Allah


ne ke kula da shi ta samar da shi da arziƙin shi, da kula


da shi. Ubangiji Rayayye ne ba Ya mutuwa kuma


7


ƙarewa ta koru gare shi, Tsayayye ne ba ya bacci, a’a


gyangyaɗi ko bacci basa kama Shi.


Daga siffofinSa shi Masani ne, wanda babu wani


abu da yake ɓoyuwa a gare Shi a ƙasa ko a sama.


Daga cikin siffofinsa cewa Shi Mai ji ne kuma Mai


gani ne, wanda Yake jin kowanne abu, Yake ganin


kowanne abin halitta, Yana sane da abinda


zukatammu suke saƙawa da kuma abinda suke


ɓoyewa, babu wani abu da yake boyuwa a gare Shi,


tsarki ya tabbata a gare Shi a sama ko a ƙasa.


Daga cikin siffofinSa Shi Mai iko ne, babu wani abu


da yake gagarar Allah, kuma babu abinda zai mayar da


nufinSa, Yana aikata abinda Ya so, Yana kuma hana


abinda Ya so, Yana ƙaddamarwa Yana kuma


jinkirtarwa, Yana da cikakkiyar hikima.


Daga cikin siffofinSa Shine Mahalicci, Mai


azurtawa, Mai juya lamura, wanda Ya halicci halittu Ya


kuma juya su, halittu suna cikin damƙarSa, kuma


ƙarƙashin rinjayenSa.


Daga cikin siffofinSa Shine Yake amsawa mai


tsanain buƙata, Yana agazawa wanda yake cikin


tsanani, Yana yaye baƙin ciki, duk wani abin halitta, to


idan ya shiga damuwa da kunci, yana komawa ne


gareShi don neman taimako.


Ita


bauta ba ta kasancewa sai ga Allah -


Maɗaukakin sarki -, Shi ne cikakke wanda Ya cancanci


a bauta maSa Shi kaɗai banda wanda ba Shi ba, duk


8


abinda aka bautawa da ba Shi ba to abin bautar


ɓatacce ne kuma tawayayye ne, mai mutuwane mai


ƙarewa ne.


Allah - tsarki ya tabbatar maSa - Ya azurta mu da


hankulan da suke riskar wani abu na girmanSa, Ya


kuma dasa mana ɗabi'ar da take son alheri, kuma take


ƙin sharri, kuma  take natsuwa idan ka fake ga Allah


Ubangijin talikai, wannan ɗabi'ar tana nuni akan


cikarSa kuma cewa bazaiyiwu a siffantaShi da tawaya


ba - tsarki ya tabbatar maSa -.


Bai kamata ga mai hankali ya bautawa wani ba sai


cikakke, to tayaya zai bautawa wanda aka halitta mai


tawaya irinsa ko ma wanda bai kai shi ba!


Bazai yuwu ba abin bautawa ya kasance mutum, ko


gunki ko bishiya ko dabba!


Ubangiji Yana saman sammanSa, Ya daidaitu a kan


Al’arshinSa  nesa da halittarSa, babu wani abu a


zatinSa na halittarSa, haka kuma babu a cikin


halittarSa wani abu na zatinSa, ba ya shiga ko ya narke


a cikin halittarSa.


Ubangiji babu wani abu da ya yi kama da Shi, Shi


Mai ji ne Mai gani ne, ba Shi da wani kini, Shi


Mawadaci ne ga barin halittarSa, ba Ya bacci baYa cin


abin ci, shi Mai girma ne, bazaiyiwu a ce Yana da mata


ko ɗa ba; Malicci Yana da siffofin girma wanda ba zaiyi


wu ba har abada ace Ya siffantu da buƙata ko tawaya.


Allah - Madaukakin sarki - Ya ce:





 {Ya ku mutãne! An buga wani misãli, sai ku saurãra


zuwa gare shi. Lalle ne waɗanda kuke kira baicin Allah,


bã zã su halitta ƙudã ba, kõ da sun tãru gare shi, kuma


idan ƙudãn ya ƙwãce musu wani abu, bã zã su kuɓutar


da shi ba daga gare shi. Mai nẽma da wanda ake


nẽman gare shi sun raunana} (73)


Ba su ƙaddara wa Allah haƙƙin girmanSa ba. Lalle


ne Allah, haƙĩƙa, Mai ƙarfi ne, Mabuwãyi}


[al-Hajj: 73-74].


To saboda me wannan Mahalicci Mai girma


Ya haliccemu? Kuma me Yake so daga


garemu?


Shin zai yuwu a hankalce ace Allah Ya halicci duk


waɗannan halittu, ba tare da wata manufa ba, shin Ya


haliccesu ne don wasa alhali Shine Gwani Masani?


Shin zai yuwu a hankalce cewa wanda Ya halicce


mu da wannan kyautataccen tsari, Ya kuma hore


mana abinda ke cikin sammai da ƙasa ace Ya halicce


mu ba tare da wata manufa ba, ko Ya barmu ba tare


da amsa mafi mahimmancin tambayoyi ba waɗanda


zasu ja hankalin mu, misali: Saboda me muke a nan?


10


Menene zai kasnce bayan mutuwa? Menene manufar


halittar mu?


Shin zai yiwu a hankalce cewa babu wata uƙuba ga


azzalimi da kuma sakayya ga mai kyautatawa?


Allah - tsarki ya tabbatar maSa - Ya ce:





 {Shin, to, kun yi zaton cẽwa Mun halitta ku ne da


wãsa kuma lalle ku, zuwa gare Mu, bã zã ku kõmo ba}


[al-Mua'Minun: 115].


A’a, Allah Ya aiko Manzanni domin musan abinda


ya sa aka samar da mu, kuma Ya nuna mana yadda


zamu bauta maSa, kuma mu nemi kusanci gare Shi,


kuma me Yake so daga garemu, ta yaya zamu sami


yardar Sa, Ya kuma bamu labarin makomar mu bayan


mutuwa.?


Allah Ya aiko Manzanni domin su bamu labarin


cewa Shi kaɗai Yake wanda Ya cancanci a bauta maSa,


domin kuma musan ya zamu bauta maSa, domin su


isar mana da umarninSa da kuma haninSa, kuma su


sanar da mu kyawawan ɗabi’un da idan muka yi riƙo


da su to rayuwar mu zata zama kyakkyawa, alhairai za


su gameta da kuma albarkatai.


Haƙiƙa Allah Ya aiko Manzanni masu yawa misalin:


(Annabi Nuhu, Ibrahim, Musa, da Isa), Ya ƙarfafe su da


ayoyi da Mu’ujizojin da suke nuni akan gaskiyarsu,


kuma cewa su Manzanni ne daga wurinSa - tsarki ya


tabbatar maSa -, kuma na ƙarshansu ya kasance


11


(Annabi) Muhammad ne - tsira da amincin Allah su


tabbata a gare shi -.


Kuma haƙiƙa Manzanni sun bamu labari a bayyane


cewa wannan rayuwar jarrabawa ce, kuma lalle


rayuwa ta haƙiƙa zata  kasance ne bayan mutuwa


Kuma cewa a can (lahira) akwai aljanna ga muminai


waɗanda suka bautawa Allah Shi kaɗai baShi da


abokin tarayya, kuma suka yi imani da dukkanin


manzanni, hakanan kuma a can (lahira) akwai wuta


wacce Allah Ya tanadeta ga kafirai waɗanda suka


bautawa wasu allolin tare da Allah, ko suka kafirce da


kowane manzo daga cikin manzannin Allah.


Allah - Madaukakin sarki - Ya ce:





 {Yã ɗiyan Ãdam! Ko dai wasu manzanni, daga


cikinku, su jẽ muku, sunã gaya muku ayõyiNa to,


wanda ya yi taƙawa, kuma ya gyara aikinsa, to, bãbu


tsoro a kansu, kuma bã su yin baƙin ciki (35)


Kuma waɗanda suka ƙaryatã game da ãyõyinMu,


kuma suka yi girman kai daga gare su, waɗannan sũ ne


abõkan wuta, sũ, a cikinta madawwama ne}


[al-A'araf: 35-36].


Allah - Madaukakin sarki - Ya ce:





 {Yã ku mutãne! Ku bauta wa Ubangjinku, Wanda


Ya halicce ku, kũ da waɗanda suke daga gabãninku,


tsammãninku ku kãre kanku (21)


Wanda Ya sanya muku ƙasa shimfiɗa, kuma sama


gini, kuma Ya saukar da ruwa daga sama, sa'an nan Ya


fitar da abinci daga 'ya'yan itãce game da shi, sabõda


ku. Sabõda haka kada ku sanya wa Allah wasu


kĩshiyõyi, alhãli kuwa kuna sane (22)


Idan kun kasance a cikin kokwanto daga abinda


muka saukar a bisa bawanmu, to kuzo da wata sura


irinsa (alkur'ani) kuma ku kira shedunku wanda ba


Allah ba, in kun kasance masu gaskya ne (23)


To, idan ba ku aikata (kãwo sura) ba, to, bã zã ku


aikataba, sabõda haka, ku ji tsoron wuta, wadda


makãmashinta mutãne da duwãtsu ne, an yi tattalinta


dõmin kãfurai (24)


Kuma ka bãyar da bishãra ga waɗanda suka yi


ĩmãni. kuma suka aikata ayyuka na ƙwarai, cẽwa


13


lallene, suna da gidãjen Aljanna, ƙõramu na gudãna


daga ƙarƙashinsu. Ko da yaushe aka azurta su da


abinci daga wasu 'ya'yan itãce daga gare su, sai su ce:


"Wannan shi ne aka azurta mu da shi daga gabãnin


haka," Kuma a je musu da shi yana mai kama da juna,


Kuma sunã da, a cikin su, mãtan aure mãsu tsarki,


kuma su, cikin su madawwama ne}


[Suratul Baƙarah, 21-25].


ME YASA MANZANNI SUKE DA YAWA ?


Tabbas Allah Ya aiko ManzanninSa zuwa ga


al’ummatai, babu wata al’umma face sai da Allah Ya


aika musu da Manzo, domin ya kira su zuwa ga


bautawa Ubangijin su, kuma ya isar musu da


umarninSa da kuma haninSa, kuma manufar kiran na


su ya kasance ne gaba ɗaya itace: Bautawa Allah Shi


kaɗai - Mai girma da ɗaukaka -. To a duk lokacin da


wata al’umma ta fara bari ko ta rikitar da abinda


Manzon ya zo da shi na kaɗaita Allah, sai Allah Ya sake


aiko da wani Manzon domin ya gyara tafiyar, kuma ya


kuma dawo da mutane kan tafarki na daidai, na


kaɗaita Allah da kuma yi maSa biyayya.


Har sai da Allah Ya kammala aiko Manzanni da


(Annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su


tabbata a gare shi -, wanda yazo da Addini cikakke da


kuma shari’a tabbatacciya gamammiya ga dukkanin


mutane har ranar alƙiyama, wacce ta cika kuma ta


goge wacce ta gaba ce ta na shari’o’i, kuma Allah -


14


Maɗaukakin sarki - Ya lamunci wanzar da wannan


Addinin da kuma tabbatuwarsa har zuwa ranar


alƙiyama.


Mutum ba zai kasance mumini ba har sai ya


yi imani da dukkanin manzanni.


Allah Shine wanda Ya aiko manzanni, kuma Ya


umarci dukkanin halittarSa da yi musu biyayya, wanda


ya kafirce da sakon ɗaya daga cikinsu to haƙiƙa ya


kafircewa dukkannin su, babu wani zunubi mafi girma


fiye da mutum ya juyarwa da Allah wahayinSa, babu


makawa yin imani da dukkanin manzanni domin shiga


aljanna.


Abinda yake wajibi akan kowanne mutum a


wannan lokacin shine yayi imani da Allah da kuma


dukkanin Manzannin Allah, kuma yayi imani da ranar


ƙarshe, hakan kuma bazai kasance ba sai idan yayi


imani kuma yabi na ƙarshensu kuma cikamakinsu


(Annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su


tabbata a gare shi -, wanda aka ƙarfafeshi da mu’ujiza


madawwamiya ita ce Alƙur’ani mai girma, wanda  


Allah Ya lamunce kiyaye shi har sai ya gaje ƙasa da


waɗanda ke kanta.


Allah Ya ambata a cikin AlKur’ani cewa duk wanda


yaƙiyin imani da kowanne manzo daga cikin


manzaninSa to shi ya kafircewa Allah, kuma ya ƙaryata


wahayinSa, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce:





 {Lalle ne, waɗanda uke kãfirta da Allah da


ManzonSa kuma sunã nufin su rarrabe a tsakãnin


Allah da manzanninSa, kuma sunã cẽwa: "Munã ĩmãni


da sãshe, kuma munã kãfirta da sãshe." Kuma sunã


nufin su riƙi hanya a tsakãnin wannan (150)


Waɗannan sũ ne kãfirai sõsai, kuma Mun yi tattali,


dõmin kãfirai, azãba mai walãkantarwa}


[Surat al-Nisa'i: 150-151].


Saboda haka mu musulmai muke imani da Allah da


ranar lahira - kamar yadda Allah Yayi umarni -, kuma


muna imani da dukkanin Manzanni da littattafan da


suka gabata, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce:





 {Manzon Allah yã yi ĩmãni da abin da aka saukar


zuwa gare shi daga Ubangijinsa, da mũminai.


Kõwanensu yã yi ĩmãni da Allah, da mala'ikunSa, da


littattafanSa, da manzanninSa. Bã mu rarrabẽwa a


tsakãnin daya daga manzanninSa. Kuma (mũminai)


suka ce: "Mun ji kuma mun yi dã'a; (Muna nẽman)


16


gãfararKa, yã Ubangijinmu, kuma zuwa a gare Ka


makõma take }


[Surat al-Baƙara: 285].


MENENE ALƘUR'ANI MAI GIRMA?


Alƙur’ani mai girma shine zancan Allah -


Maɗaukakin sarki - kuma wahayinSa da Ya saukar da


shi ga ƙarshan Manzanni (Annabi) Muhammad, shine


ƙololuwar mu’ujizar da take nuni akan gaskiyar


Annabtarsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare


shi -, Alƙur'ani mai girma shine gaskiya a cikin


hukunce- hukuncensa, kuma gaskiya a cikin labaransa.


Tabbas Allah Ya ƙalubanci masu ƙaryatawa akan


suzo ko da da sure ce guda ɗaya kwatankwacinsa sai


suka kasa hakan; saboda girman abinda ya ƙunsa, da


kuma gamewar abubuwan da ya tattaro na dukkan


abinda yake da alaƙa da mutum a rayuwar duniya da


lahiya, kuma ya ƙunshi dukkanin tabbatattun


abubuwa na imani waɗanda ya wajaba ga mutum yayi


imani da su.


Kamar yadda ya ƙunshi umarni da hani waɗanda


suke wajaba mutum ya tafi akansu a tsakaninsa da


Ubangijinsa, ko tsakanin sa da kansa ko kuma tsakanin


sa da sauran halittu, dukkanin hakan a tsari na


ƙololuwar balaga da kuma bayani.


Haƙiƙa (Alƙur’ani) ya ƙunshi da yawa daga dalilai na


hankali da tabbatattun ilimi masu zurfi waɗanda suke


nuni akan wannan Littafin cewa bazai taɓa yi wuwa a


17


ce mutum ne ya ƙirkire shi ba, kai shi magana ce ta


Ubangijin mutum - tsarki ya tabbatar maSa Ya


ɗaukaka -.


MENENE MUUSULINCI?


Musulunci shi ne miƙa wuya ga Allah - Maɗaukakin


sarki - da Tauhidi, da jawuwa gareShi da biyayya, da


riƙo da shari’arSa da yarda da kuma karɓa, da kuma


kafircewa dukkanin abinda ake bautawa ba Allah ba.


Haƙiƙa Allah Ya aiko da Manzanni da saƙo ɗaya


shine: Kira zuwa ga bautar Allah Shi kaɗai ba Shi da


abokin tarayya, da kuma kafircewa dukkanin abinda


ake bautawa ba Allah ba.


Musulunci shi ne Addinin dukkanin Annabawa,


kuma da’awarsu ɗaya ce, shari’o’insu sun sha banban,


musulmai a yau su ne masu kaɗaita Allah su kaɗai,


masu riƙo da ingantaccen Addini wanda dukkanin


Annabawa suka zo da shi. Kuma saƙon Musulunci a


wannan zamanin shine gaskiya, kuma shi ne saƙo na


ƙarshe daga Mahaliccin mutum.


Ubangiji wanda Ya aiko (Annabi) Ibrahim da Musa


da Isah - amincin Allah ya tabbata a gare su - Shine Ya


aiko cikamakin Manzanni (Annabi) Muhammad - tsira


da amincin Allah su tabbata a gare shi -, haƙiƙa shari'ar


Musulunci tazo tana mai shafe dukkanin shari’un da


suka gabaceta.


Dukkanin addinai waɗanda mutane suke bauta da


su a yau - in banda Musulunci- addinai ne da mutane


18


suka ƙirƙira, ko kuma addinai ne waɗanda daga Allah


suke sai mutane sukayi wasa da su, sai suka wayi gari


a cakuɗe da ɗebe-ɗebe da tatsuniya da shaci faɗi


waɗan aka gada, kuma sauran tunanin mutum.


Amma Addinin Musulmai to Addini ne guda ɗaya


kuma a bayyane yake baya canzawa, kamar yadda


bautarsu wacce suke bautawa Allah da ita ɗaya ce,


dukkanin su suna salloli biyar, suna zakkar


dukiyoyinsu, suna azumin wata Ramadan, kuma kayi


la’akari da Littafin su shi ne Alƙur’ani mai girma shi


littafi ne guda ɗaya adukkanin ƙasashe. Allah -


Maɗaukakin sarki - Ya ce:





 {A yau Na cika maku Addininku, kuma Na cika


muku ni’imta a gareku, Na kuma yardar muku


Musulunci shi ne Addini, to duk wanda ya shiga


matsananciyar buƙata a yunwa ba tare da karkata ga


lefi ba, to lalle Allah Mai gafara ne Mai jinƙai}


[Suratul Ma’idah: 3].


Allah - Maɗaukakin sarki - a ckin Alƙur'ani mai


girma Ya ce:





 {Ka ce: "Mun yi ĩmãni da Allah kuma da abin da aka


saukar mana da abin da aka saukar wa Ibrãhĩma da


Isma'ĩla da Is'hãƙa da Yãƙũba da jĩkõki, da abin da aka


bai wa Mũsã da ĩsã da annabãwa daga Ubangijinsu, bã


mu bambantãwa a tsakãnin kõwa daga gare su. Kuma


mũ, zuwa gare Shi mãsu sallamãwa ne}(84)


{Kuma wanda ya nẽmi wanin Musulunci ya zama


addini, to, bã zã a karɓa daga gare shi ba. Kuma shi a


Lãhira yana daga cikin mãsu hasãra}


[Aal Imran: 84-85].


Addinin Musulunci tsari ne da ya game dukkanin


rayuwa, yayi daidai da ɗabi’a na halitta da hankali,


kuma madaidaitun rayuka suna karɓarsa, Mahalicci


Mai girma ne Ya shar’anta shi ga halittarSa, kuma


shine Addinin alheri da rabauta ga mutane baki ɗaya


a duniya da lahira, ba ya banbance ƙabila da ƙabila, ko


nuna wariyar launin fata, mutane a cikinsa daidai


suke, wani mutum a Musulunci baya fin wani sai da


gwargwadon aikinsa na gari.


Allah - Madaukakin sarki - Ya ce:





 {Wanda ya aikata aiki na ƙwarai daga namiji kõ


kuwa mace, alhãli yanã mũmini, to, haƙĩƙa Munã rãyar


da shi, rãyuwa mai dãɗi. Kuma haƙĩƙa Munã sãkã


20


musu lãdarsu da mafi kyãwun abin da suka kasance


sunã aikatãwa}


[Suratun Nahl: 97].


MUSULUNCI HANYA CE TA TSIRA


Musulunci Addini ne na dukkanin Annabawa, kuma


shi ne Addinin mutane baki ɗaya, ba wai addini ne na


Labawa kaɗai ba.


Musulunci shi ne hanyar samun farin ciki na haƙiƙa


a duniya, kuma ni'ima madawwamiyya a lahira.


Musulunci shi ne Addini ɗaya da yake amsa


buƙatun rai da jiki, da warware dukkanin matsalolin


mutane, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce:





 {Ya ce: "Ku sauka kũ biyu daga gare ta gabã ɗaya,


sãshenku yanã maƙiyi ga sãshe. To, imma dai wata


shitiya ta jẽ muku daga gare Ni, to, wanda ya bi


shiryarwãta, to, bã ya ɓacẽwa, kuma bã ya wahala}


Kuma wanda ya bijire daga ambatõNa (Alƙur'ãni)


to, lalle ne rãyuwa mai ƙunci ta tabbata a gare shi,


kuma Munã tãyar da shi a Rãnar ¡iyãma yanã makãho}


[Ɗaha: 123-124].


21


Me Musulmi yake fa’idantuwa da shi a


duniya da lahira?


Musulinci yana da fa’idoji masu girma, daga cikinsu


akwai: - Rabauta da ɗaukaka a duniya wato mutum ya


kasance bawa ga Allah. in ba haka bafa zai zama


bawan son zuciya da shaiɗan da sha'awe-sha'awe. - Rabauta a lahira shine Allah Ya gafarta masa,


kuma Ya saukar maSa da yardarSa, kuma Ya shigar da


shi


aljanna, ya rabauta da yarda da ni’ima


tabbatacciya, kuma mutum ya tsira daga azabar wuta. - Mumini yana kasancewa ne a ranar Alƙiyama tare


da Annabawa da siddiƙai da shahidai da kuma salihai.


Kai Amma wannan tawaga babu abinda ya kai ta daɗi,


duk wanda bai yi imani ba to ya kasance ne tare da


Ɗagutai da ashararai da fanɗararru da maɓarnata. - Waɗanda Allah Zai shigar da su aljnna za su rayu


a cikin ni’ima ta har abada ba mutuwa ba rashin lafiya


ko ciwon jiki ko tsufa ko baƙin ciki, kuma za’a biya


musu buƙatunsu na duk abinda suke buƙatarsa.


Wadanda za su shiga wuta za su kasance a cikin azaba


ta har abada a dawwame ba ta yankewa.


Acikin Aljanna akwai abubuwan jin daɗin da idanu


bai gansu ba, kunne bai ji su ba, kuma basu ɗarsuwa a


zuciyar wani mutum ba. Daga dalilan hakan faɗinSa -


Maɗaukakin sarki -:


22





 {Wanda ya aikata aiki na ƙwarai daga namiji kõ


kuwa mace, alhãli yanã mũmini, to, haƙĩƙa Munã rãyar


da shi, rãyuwa mai dãɗi. Kuma haƙĩƙa Munã sãkã


musu lãdarsu da mafi kyãwun abin da suka kasance


sunã aikatãwa}


[al-Nahl: 97].


Maɗaukakin sarki Ya ce:





 {Kuma rai ba ta san  abinda aka ɓoye musu na farin


idanuwa ba, sakamako na abinda suka kasance suna


aikatawa}


[Suratus Sajdah, aya ta 17]


Me abinda wanda ba musulmi ba zai yi


asara?


﴿ َ


 Mutum zai yi hasarar mafi girman ilimi da sani, shi


ne sanin Allah, kuma zai yi hasarar imani da Allah,


wanda ya ke bawa mutum aminci da nutsuwa a


duniya, da ni'ima madawwamiyya a lahira.


Mutum zai yi hasarar tsinkaye a kan mafi girman


littafin da Allah Ya saukar da shi zuwa ga mutane, da


kuma imani da wannan Littafin mai girma.


Zai yi hasarar imani da Annabawa masu girma,


kamar yadda zai yi hasarar zama tare da su a aljanna


23


ranar alƙiyama, zai kasance abokin zaman shaiɗan da


masu laifuffuka da ɗagwitai (waɗanda aka bautawa) a


cikin wutar Jahannama tir da wannan gida kuma tir da


wannan maƙotaka.


Allah - Madaukakin sarki - Ya ce:





 {Kace lallai hasararru sune waɗanda suka yi


hasarar kawunann su da ahalin su ranar alƙiyama, ku


saurara, wannan ita ce hasara bayyananna (15)


Sunã da waɗansu inuwõwi na wutã daga samansu,


kuma daga ƙasansu akwai waɗansu inuwõwi. Wancan


Shĩ ne Allah ke tsõratar da bãyinSa da shi. Yã bãyĩNa!


To, ku bĩ Ni da taƙawa}


[al-Zumar: 15-16].


Wanda yake nufin tsira a lahira, to ya


wajaba a kansa ya kasance musulmi mai


biyayya ga Allah, mai kuma bin Manzon


Allah-tsira da amincin Allah su tabbata agare


shi-


Daga tabbatattun abubuwan da Annabawa da


Manzanni - amincin Allah ya tabbata a gare su - suka


haɗu a kansu cewa babu wanda zai tsira a lahira sai


24


musulmai waɗanda suka yi imani da Allah -


Maɗaukakin sarki -, ba su haɗa kowa da Shi a bauta


ba, kuma suka yi imani da dukkanin Annabawa da


Manzanni, duk masu bin Manzanni waɗanda suka yi


imani da su masu gasgata su, to za su shiga aljanna


kuma za su tsira daga wuta.


Waɗanda suka yi imani a zamanin (Annabi) Musa


suka yi imani da shi suka bi karantarwar sa to


waɗannan musulmai ne, kuma muminai ne salihai,


saidai bayan Allah Ya aiko da Annabi Isa ya wajaba ga


mai mabiya Annabi Musa su yi imani da Annabi Isa su


kuma bi shi.


Waɗanda suka yi imani da Annabi Isa to waɗannan


musulmai ne salihai, wanda kuma ya yi watsi da imani


da Annabi Isa ya ce, zan kasance akan Addinin Annabi


Musa, to wannan bai yi imani ba, domin ya yi watsi da


imani da Manzon da Allah Ya aiko shi.


Sannan bayan da Allah Ya aiko Manzon ƙarshe


(Annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su


tabbata a gare shi -, ya wajaba akan kowa suyi imani


da shi, Ubangiji Shi ne Ya aiko (Annabi) Musa da Isah


kuma Shi ne wanda Ya aiko cikamakin Manzanni


(Annabi) Muhammad, duk wanda ya kafircewa


manzancin (Annabi) Muhammad - tsira da amincin


Allah su tabbata a gare shi - ya ce zan kasance akan


bin (Annabi) Musa ko Isa to wannan ba mumini ba ne.


25


Baya wadatarwa mutum ya ce shi yana girmama


musulmai, kuma baya wadatarwa don samun tsiransa


a ranar ƙarahe saboda ya bada sadaka kuma yana


taimakawa talakawa, kai babu makawa sai ya kasance


ya yi imani da Allah da littattafanSa da ManazaninSa


da ranar ƙarshe; domin Allah Ya karɓi hakan daga gare


shi!. Babu wani zunubi mafi girma da ya kai shirka da


kafircewa Allah da ƙin yin imani da wahayin da Allah


Ya saukar da shi ko ƙin yin imani da ƙarshan


AnnabawanSa (Annabi) Muhammad - tsira da amincin


Allah su tabbata agare shi -.


Yahudu da Nasara da sauransu waɗanda suka ji


aiko (Annabi) Muhammad Manzon Allah - tsira da


amincin Allah su tabbata a gare shi -, suka ƙi yin imani


da shi suka ƙi shiga Addinin Musulunci to za su


kasance a wutar Jahannama masu dawwama a cikinta


har abada, wannan shi ne hukuncin Allah ba hukuncin


wani ba ne cikin mutane, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya


ce:





 {Lalle ne waɗanda suka kafirta daga mutanen


Littafi da mushirikai sana cikin wutar Jahannama suna


madawwama a cikinta. Waɗannan su ne mafi


ashararancin tãlikai}


[al-Bayyinah: 5].


26


Yayin da ƙarshen saƙo ya sauka daga Allah izuwa


yan Adam, ya wajaba akan kowanne ɗaya da ya ji


(bayanin) Musulunci ya kuma ji (bayanin) Annabin


ƙarshe (Annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah


su tabbata a gare shi -, ya yi imani da shi kuma ya bi


shari'arsa, ya yi masa biyayya a umarninsa da haninsa,


saboda haka wanda ya ji wannan saƙon na ƙarshe


kuma ya ƙi binsa, to Allah ba zai karɓi wani abu daga


gare shi ba, kuma zai azabtar da shi a lahira.


Daga cikin dalilan haka, faɗinSa - Maɗaukakin sarki -:





 {Kuma wanda ya nẽmi wanin Musulunci ya zama


addini, to, bã zã a karɓa daga gare shi ba. Kuma shi a


Lãhira yana daga cikin mãsu hasãra}





 [Aal- Imran: 85].


Maɗaukakin sarki Ya ce:





 {Ka ce: "Yã ku Mutãnen Littãfi! Ku tafo zuwa ga


kalma mai daidaitãwa a tsakã ninmu da ku; kada mu


bauta wa kõwa fã ce Allah. Kuma kada mu haɗa kõme


da Shi, kuma kada sãshenmu ya riƙi sãshe Ubangiji,


27


baicin Allah." To, idan sun jũya bã ya sai ku ce: "ku yi


shaida cẽwa, lalle ne mu masu sallamã wa ne}


[Aal- Imran: 64].


Meye ya lazimci Musulmi?


Yana wajaba akan musulmi, yin imani da waɗannan


rukunan guda shida:


Yin Imani da Allah - Maɗaukakin sarki - kuma cewa


Shi ne Mahalicci Mai azurtawa Mai juya lamura


Mamallaki, babu wani abu da ya yi kama da Shi, ba Shi


da mata ba Shi da ɗa, kuma Shi kaɗai ne wanda Ya


cancanci a bauta maSa, kuma ba’a bauta wani tare da


Shi, kuma Ya ƙudirce cewa bautawa dukkanin wanda


ake bautawa koma bayanSa to bautarsa ɓatacciya ce.


Yin imani da mala'iku, cewa su bayin Allah ne -


Maɗaukakin sarki -, Ya halicce su daga haske, kuma Ya


sanya cewa daga cikin ayyukansu su suna sauko da


wahayi ga AnnabawanSa.


Yin imani da dukkanin littattafan da Allah Ya saukar


da su ga AnnabawanSa (kamar Attaura da Injila - kafin


a jirkita su -) kuma ƙarshen littattafan shi ne Alƙur'ani


mai girma.


Yin imani da dukkanin Manzanni, kamar (Annabi)


Nuhu da (Annabi) Ibrahim da (Annabi) Musa da


(Annabi) Isa, da na ƙarshensu shine (Annabi)


Muhamad, kuma dukkaninsu daga 'yan Adam suke,


(Allah) Ya ƙarfafe su da wahayi kuma Ya basu ayoyi da


mu'ujizojin da suke nuni akan gaskiyarsu.


28


Imani da ranar ƙarshe, yayin da Allah zai tashi na


farko da na ƙarshe, Allah kuma zaiyi hukunci tsakanin


halittarSa, Ya shigar da muminai aljanna, kafirai kuma


Ya shigar da su wuta.


Imani da kaddara cewa, Allah ya san komai, abinda


ya kasance ya wuce da kuma abinda zai kasance nan


gaba, kuma hakika  Allah ya rubuta haka, kuma ya so


shi ya halicci komai.


Kuma ka bautawa Allah da abinda Ya shar’anta na


sallah da zakkah da azumi da kuma hajji idan ka sami


ikon tafiya gareshi. Sannan ya wajaba akan shi ya koyi  


Addininsa wanda zai zama tushen rabautarsa a duniya


da kuma tsiransa a lahira.


***


 29


 


30


Teburin bayani


 


WA YA HALICCI HALITTU? WA YA HALICCE NI ? KUMA SABODA


ME ? ............................................................................................. 2


Ubangiji Mahalicci Mai girma. ..................................................... 4


Wannan Ubangijin Mahalicci Mai azirtawa, Shi ne Allah - tsarki


da ɗaukaka sun tabbatar masa -. ................................................ 5


SIFFOFIN UBANGIJI MAHALICCI. .................................................. 6


Ubangiji abin bauta wanda ya siffantu da siffofin cika ................ 7


To saboda me wannan Mahalicci Mai girma Ya haliccemu? Kuma


me Yake so daga garemu? ......................................................... 10


ME YASA MANZANNI SUKE DA YAWA ? .................................... 14


Mutum ba zai kasance mumini ba har sai ya yi imani da dukkanin


manzanni. .................................................................................. 15


MENENE ALƘUR'ANI MAI GIRMA? ............................................ 17


MENENE MUUSULINCI? ............................................................ 18


MUSULUNCI HANYA CE TA TSIRA .............................................. 21


Me Musulmi yake fa’idantuwa da shi a duniya da lahira? ........ 22


Me abinda wanda ba musulmi ba zai yi asara? ......................... 23


Wanda yake nufin tsira a lahira, to ya wajaba a kansa ya kasance


musulmi mai biyayya ga Allah, mai kuma bin Manzon Allah-tsira


da amincin Allah su tabbata agare shi- ...................................... 24


Meye ya lazimci Musulmi? ........................................................ 28





 



Posts na kwanan nan

WA YA HALICCI HALITTU ...

WA YA HALICCI HALITTU? WA YA HALICCE NI ? KUMA SABODA ME ?

Na sami Musulunci a m ...

Na sami Musulunci a matsayin addini ba tare da rasa imani da Yesu Almasihu (aminci ya tabbata a gare shi) ko wani daga cikin annabawan Allah Maɗaukaki ba

FALALAR GOMAN FARKO N ...

FALALAR GOMAN FARKO NA ZUL-HIJJA

SIFFAR SALLAR ANNABI ...

SIFFAR SALLAR ANNABI – TSIRA DA AMINCIJ ALLAH